09/07/2026
SHAHADA BA ƘARSHEN RAYUWA BA CE, FARKON DAUKAKA CE
Tunawa da Shahid Sayyid Ali Khamenei (QS)
Saƙo daga Kasshafatul Imamil Mahdi (Atfs) na Najeriya
﴿إِنَّا لِلّٰهِ وَإِنَّا إِلَيْهِ رَاجِعُونَ﴾
ِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيمِ
*وَلَا تَحْسَبَنَّ الَّذِينَ قُتِلُوا فِي سَبِيلِ اللَّهِ أَمْوَاتًا ۚ بَلْ أَحْيَاءٌ عِندَ رَبِّهِمْ يُرْزَقُونَ*
“Kada ka yi zaton waɗanda aka kashe a hanya ta Allah sun mutu. A’a, rayayyu ne a wurin Ubangijinsu, ana ba su arziki."
(Ali 'Imran - Aya ta 169)
Wannan aya ta sauka ne bayan yakin Uhud. Allah yana mana albishir cewa shahidai ba su mutu ba. Suna da rai a wurin Allah, cikin jin daɗi da arziki na Aljanna. Ba su jin zafi na mutuwa, kuma suna farin ciki da abin da Allah ya ba su.
Wannan yana ba mu bege da ƙarfi cewa sadaukarwa a hanyar Allah ba ta ɓata ba.
Kuma Ya ce:
إِنَّ اللَّهَ اشْتَرَىٰ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ أَنْفُسَهُمْ وَأَمْوَالَهُمْ بِأَنَّ لَهُمُ الْجَنَّةَ
Ma’ana “Lallai Allah Ya sayi rayukan muminai da dukiyoyinsu da Aljanna a madadinsu.”
(Suratut Tawbah: 111)
Waɗannan ayoyi ba wai suna ba da labari ba ne kadai; alkawarin Allah (T) ne ga waɗanda s**a ba addini rayuwarsu, s**a fifita gaskiya a kan jin daɗin duniya, s**a ɗauki wahala domin kare abin da s**a yi imani da shi.
A cikin tarihin al’ummomi wadanda s**a wuce dama Wanda suke a yanzu, akwai mutane da ba za'a auna su da shekarun su ko mulkin da s**a yi ba, sai dai da irin tasirin da s**a bari a zukatan mutane. Daga cikin irin waɗannan akwai Shahid Sayyid Ali Khamenei (QS).
Wanda ya kasance tun yana matashi ya ɗauki tafarkin ilimi, da’awa da gwagwarmaya. Ya sha ɗaurin kurkuku, ya fuskanci azabtarwa da tsangwama saboda matsayinsa, bai sayar da imaninsa ba, bai yi shiru saboda tsoro ba, bai sauya manufarsa saboda wahala ba. Ya zaɓi hanya mai ƙaya domin neman yardar Allah.
A shekarar 1981, wani mummunan hari ya jikkata hannunsa sosai. Wannan rauni ya kasance tare da shi har tsawon rayuwarsa. Amma bai taɓa zama uzuri na janyewa daga hidimar addini da al’umma ba. Ya ci gaba da jagoranci, koyarwa, da kira zuwa ga abin da ya yi imani da shi.
Kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya ce:
قَالَ رَسُولُ اللَّهِ ﷺ.
*"أَفْضَلُ الْجِهَادِ كَلِمَةُ عَدْلٍ عِنْدَ سُلْطَانٍ جَائِرٍ"*
“Mafificin jihadi shi ne faɗin gaskiya a gaban shugaba azzalumi.”
Sannan kuma Imam Ali (AS) ya ce: “Ku kasance masu taimakon zalumci ta hanyar yaƙarsa, kuma masu taimakon wanda aka zalunta ta hanyar kare shi.”—(Nahjul Balagha)
Rayuwar manyan mutane tana koyar da cewa gaskiya tana da farashi. Wanda ya zaɓi tafarkin Allah dole ne ya shirya fuskantar gwaji.
Kamar yadda Allah (T) yake cewa a cikin littafin sa Mai tsarki.
*Suratul Ankabut - Aya ta 2*
*أَحَسِبَ النَّاسُ أَنْ يُتْرَكُوا أَنْ يَقُولُوا آمَنَّا وَهُمْ لَا يُفْتَنُونَ*
*"Shin mutane sun yi zaton za a bar su kawai su ce: 'Mun yi imani' kuma ba za a jarrabesu ba?"*
Shugabanci na gaskiya ba wai sarauta ba ce. Amana ce, Nauyi ne. Sadaukarwa ce. Jagora na gaskiya shi ne wanda yake gaba idan jarabawa ta zo, ba wanda yake ɓoye idan haɗari ya bayyana ba, Tarihi yana tuna waɗanda s**a sadaukar da rayuwarsu saboda manufa. Ba don sun nemi ɗaukaka ba, sai don sun nemi yardar Allah.
Kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya ce: “Mafi soyuwa ga Allah daga cikin mutane shi ne wanda ya fi amfanar mutane.”—(Al-Mu’jam al-Awsat na Tabarani)
Kasshafatul Imamil Mahdi (Atfs) na Najeriya, muna kallon irin wannan rayuwa a matsayin makaranta ga matasa. Makarantar haƙuri, juriya, sadaukarwa da tsayawa kan gaskiya ko da kuwa duniya baki ɗaya ta juya maka baya. Ko da mutuwa ta zo. To Mutuwa ba ta kashe manufa. Jini ba ya kashe gaskiya. Shahada ba ƙarshen tafiya ba ce; tana zama fitila ga waɗanda s**a rage.
Muna miƙa ta’aziyyarmu ga mai wannan zamanin Sahibul Asr Al-Mahdi (AJTF), Jagoran gwagwarmayar Musulumci Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) iyalai, masoya, da duk masu jin wannan babban rashi. Muna roƙon Allah Ya karɓi shahadarsa, Ya gafarta masa, Ya ɗaukaka matsayinsa tare da annabawa, siddiqai, shahidai da salihai.
Allah Ya ba mu ikon koyo daga rayuwar mutanen kirki, Ya sa mu kasance masu kare gaskiya, masu hidimar addini da al’umma, ba tare da tsoro ko son zuciya ba. za mu tuna da shi saboda ya ba shekarunsa ma’ana, Ba za mu tuna da shi saboda ya riƙe matsayi ba, za mu tuna da shi saboda ya ɗauki nauyin da matsayi sa ya zo da shi. Ba za mu tuna da shi saboda ya yi suna a duniya ba, za mu tuna da shi saboda ya yi rayuwar da ta zama darasi ga masu zuwa a bayansa.
Saqo;
Daga Kasshafatul Imamil Mahdi (Atfs) na Nigeria, karkashin Jagorancin Sayyid Ibraheem El-Zakzaky (H)