16/04/2026
Ana zarginta da badakalar kuɗi na dala miliyan $1.3 da kuma naira miliyan N746.6: Kotu ta bayar da umarnin k**a Sadiya Umar Farouq da sakataren ma’aikata
Alkalin babbar kotun babban birnin tarayya (FCT) da ke Abuja, Justice Jude Onwuegbuzie, a ranar Alhamis 16 ga Afrilu, 2026, ya bayar da umarnin k**a tsohuwar ministar harkokin jin ƙai da kula da bala’o’i, Sadiya Umar Farouq, da kuma Babban Sakataren ma’aikatar, Bashir Nura Alkali.
An tsara a gurfanar da su a gaban kotu a ranar, amma ba su halarta ba. Mutum na uku kawai, Sani Nafiu Mohammed, shi ne ya bayyana a kotu.
Hukumar Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) ce ke tuhumar su da laifuka guda 21, ciki har da cin amanar dukiya, amfani da mukami ba daidai ba, bada kwangila ta hanyar zamba, da karkatar da kuɗaɗen gwamnati da s**a kai kusan dala $1,300,000 da kuma naira N746,574,303.
A cikin tuhuma ta farko, an ce lokacin da Sadiya ke minista, tare da Bashir a matsayin sakatare, sun karɓi amana ta kuɗin dala miliyan $1.3 amma s**a karkatar da su don amfanin kansu. Kuɗin na daga cikin waɗanda kamfanin Visual ICT Limited ya k**ata ya mayar wa ma’aikatar, bayan an biya fiye da kima a wani shirin gwamnati.
Lauyan masu ƙara, Rotimi Jacobs, ya bayyana wa kotu cewa an shigar da ƙarar tun Disamba 2025, amma ba a samu damar kawo waɗanda ake tuhuma ba. Ya kuma ce Sadiya ta je Saudiyya domin duba lafiyarta tun 2024, amma har yanzu ba ta dawo da fasfonta ba, kuma ba a samu rahoton lafiyarta ba.
Lauyan Sadiya, Abdul Ibrahim, ya ce rashin zuwanta saboda rashin lafiya ne, amma kotu ta ƙi amincewa da takardun da ya gabatar.
EFCC ta roƙi kotu ta bayar da umarnin k**a Sadiya da Bashir saboda sun gaza halartar kotu duk da an ba su beli. A ƙarshe, alkalin kotu ya amince da hakan, ya bayar da umarnin k**a su, sannan ya ɗage shari’ar zuwa ranar 18 ga Mayu, 2026 domin ci gaba da gurfanar da su da fara shari’a.