Sokoto Facts

Sokoto Facts The most reliable and strong Online Media in the Caliphate.
(1)

Dantakarar gwamnan Kaduna a zaben 2023 karkashin PDP Isah Ashiru Kudan ya sayi fom din takarar gwamnan Kaduna karkashin ...
11/05/2026

Dantakarar gwamnan Kaduna a zaben 2023 karkashin PDP Isah Ashiru Kudan ya sayi fom din takarar gwamnan Kaduna karkashin ADC a zaben 2027.

2026 Hajj: JIRGI NA UKKUHukumar jindadin Alhazzai ta jahar Sokoto na kiran Maniyyatan aikin Hajji daga Kananan hukumomin...
11/05/2026

2026 Hajj: JIRGI NA UKKU

Hukumar jindadin Alhazzai ta jahar Sokoto na kiran Maniyyatan aikin Hajji daga Kananan hukumomin Gada, Kebbe da Sokoto ta Arewa da su hallara a sansanin Alhazzai dake Modorawa yau Attanin 11/05/2026 da karfe 4:00 na yamma domin shirin tafiya ƙasa mai tsarki.

Danmajalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gada/Goronyo ya sake raba motoci kirar Highlander 2009 ga Hon. Abdul...
11/05/2026

Danmajalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gada/Goronyo ya sake raba motoci kirar Highlander 2009 ga Hon. Abdulwahab Yahaya Goronyo da Malam Nasiru Sagera.

2026 Hajj: JIRGI NA BIYUHukumar jindadin Alhazzai ta jahar Sokoto na kiran Maniyyatan aikin Hajji daga karamar hukumar  ...
11/05/2026

2026 Hajj: JIRGI NA BIYU

Hukumar jindadin Alhazzai ta jahar Sokoto na kiran Maniyyatan aikin Hajji daga karamar hukumar Gwadabawa da wasu daga cikin na karamar hukumar Illela da su hallara a sansanin Alhazzai dake Modorawa yau Attanin 11/05/2026 yanzu domin shirin tafiya ƙasa mai tsarki.

Jam’iyyar ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da kuma jam’iyyarsa ta APC da hannu wajen kafa sabuwar jam’iyyar NDC do...
11/05/2026

Jam’iyyar ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da kuma jam’iyyarsa ta APC da hannu wajen kafa sabuwar jam’iyyar NDC domin raunata haɗin kan ‘ƴan adawa a Najeriya.

Zargin na zuwa ne yayinda ake cigaba da tafka muhawara tsakanin jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

A cewar ADC, kafa jam’iyyar NDC wata dabara ce da aka ƙirƙira domin raba kan masu jefa ƙuri’a ga jam’iyyun hamayya, tare da rage ƙarfin manyan jam’iyyun adawa dake shirin ƙalubalantar gwamnati mai mulki.

ADC tace maimakon bunƙasa dimokaraɗiyya ta gaskiya, an kafa sabuwar jam’iyyar ne domin kawo cikas ga haɗin kai tsakanin ƴan adawa.

Sai dai jam’iyyar APC ta musanta zargin, inda tace ba ta da hannu wajen kafa jam’iyyar NDC, tare da ƙoƙarin wanke kanta daga zarge-zargen da ADC ke yi.

A yau Litinin ne wa’adin mika rajistar membobin jam’iyyu ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa wato INEC yake cika, an...
11/05/2026

A yau Litinin ne wa’adin mika rajistar membobin jam’iyyu ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa wato INEC yake cika, ana fargabar wasu masu neman takara da masu shirin canza sheƙa zuwa wasu jam’iyyu zasu rasa damar shiga zaɓen 2027 domin yau ne za’a kulle kofar shiga zaben.

Rahotanni sun nuna cewa masu neman takarar shugaban ƙasa da gwamnoni da na majalisun tarayya da jihohi na daga cikin waɗanda makomarsu ke cikin duhu sakamakon rikice-rikicen shugabanci da ke addabar wasu jam’iyyunsu.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa duk da cewa wa’adin mika rajistar ya cika a jiya Lahadi, kasancewar ranar hutu ce da ofisoshin INEC ba sa aiki, ana ganin za’a iya karɓar takardun a yau Litinin.

Sheikh Isa Ali Pantami yace ya sha bayarda gudummuwar kuɗi ga jam'iyyar APC a lokutta daban-daban, inda ya yi iƙirarin c...
10/05/2026

Sheikh Isa Ali Pantami yace ya sha bayarda gudummuwar kuɗi ga jam'iyyar APC a lokutta daban-daban, inda ya yi iƙirarin cewa ko a kwanan nan ya bada "gudummuwar naira miliyan 50" lokacin babban taron jam'iyar a Abuja

Pantami yace ya kuma bada wata "miliyan 45" a lokacin sabunta rijistar jam'iyyar ta APC.

Shehin Malamin ya ƙara da cewa, ba’a taɓa neman wata gudummuwa daga gareshi ba ya ƙiya.

2027: Masu neman takarar Gwamnan jahar Sokoto karkashin jam’iyyar ADC.1. Hon. Bashir Usman Gorau2. Malam Sa’idu Umar3. H...
10/05/2026

2027: Masu neman takarar Gwamnan jahar Sokoto karkashin jam’iyyar ADC.

1. Hon. Bashir Usman Gorau
2. Malam Sa’idu Umar
3. H.E Manir Muhammad Dan’iya
4. Sanata Ibrahim Lamido
5. Hon. Yusuf Suleiman
6. Hon. Faruku Malami Yabo
7. Hon. Abdussamad Dasuki
8. A. A Gumbi
9. Hon. Abdullahi Balarabe Salame
10. Malam Bashir Ahmad Dan Hili

Masu neman takarar Danmajalisar tarayya mai wakiltar Isah/Sabon Birni a jam’iyyar ADC.1. Hon. Abubakar Mai Kuddi2. Hon. ...
10/05/2026

Masu neman takarar Danmajalisar tarayya mai wakiltar Isah/Sabon Birni a jam’iyyar ADC.

1. Hon. Abubakar Mai Kuddi
2. Hon. Abba Shu’aibu

10/05/2026

Yadda wani matashi yayi yunkurin kifarda Kakakin majalisar wakilai Hon. Tajudeen Abbas a wurin yekuwar kaddamarda sake zabensa Danmajalisar tarayya karo na biyar a jam’iyyar APC.

Masu neman takarar Danmajalisar tarayya mai wakiltar Wurno/Rabah a jam’iyyar ADC.1. Hon. Hassan Muhammad Rabah 2. Hon. B...
10/05/2026

Masu neman takarar Danmajalisar tarayya mai wakiltar Wurno/Rabah a jam’iyyar ADC.

1. Hon. Hassan Muhammad Rabah
2. Hon. Bashir Gidado
3. Hon. Shehu Labbo Gandi
4. Hon. Aliyu Ja’afar

Address

Lodge Road
Sokoto

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sokoto Facts posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Sokoto Facts:

Share