13/08/2026
2027: Gwamnan Oyo kuma dantakarar Shugaban kasa a jam’iyyar APM Seyi Makinde ya ayyana tsohon shugaban hukumar DSS Lawal Daura a matsayin wanda zai masa takarar mataimaki a jam’iyyar APM.
Makinde ya bayyana hakan a wurin babban taron jam’iyyar APM da aka gudanar a jihar Bauchi.
Daura zai maye gurbin Ibrahim Adamu Bala, wanda a baya aka sanar da shi a matsayin abokin takarar Makinde, amma rahotanni s**a ce an sanya shine matsayin wucin-gadi.