16/04/2026
ZAITUNAH ORPHANS ASSOCIATION TULAI, TAKAI ZIYARAR GAISUWAN SALLAH GA MAI MARTABA HAKIMIN ƘASAR TULAI (ALH. JAFAR IDRIS) NA SHEKARAR 1447/2026.
_______________________________
Amadadin kungiyar baki daya bisa Jagorancin (Alh. Murtala Mohammad Balarabe) tare da Rakiyar Abokan gudanar da wannan kungiyar cikin tawaga s**a kai Ziyarar Gaisuwan sallar tare da taya Mai MARTABA Murnar karin girma da ci gaba da wannan Masarautar tasamu.
Bayan haka kungiyar ta gabatar da cikakken BAYANI akan irin gudunmawar da Mai MARTABA yake bawa wannan kungiyar tun zaman Farkon kafata tare da bayyana farin cikin Shuwagabannin ƙungiyar,
Sannan kungiyar ta ci gaba da bayyana irin nasarorin da aka samu tun bayan kafuwar kungiyar tare da kara Jaddada Manufofinta ga Mai MARTABA tare da neman goyon baya kan Ƙudirurin data sanya da tsare-tsaren ta anan gaba.
A Jawabin Godiya tare da nuna farin cikin sa marar misaltuwa ga jagororin wannan ƙungiya mai Albarka, bayan haka, ya kara da tabbatar mana Alkawarin cikakken Goyon bayansa a dukkan Manufar wannan kungiya, ya kara da cewa a gunsa,
Wannan Kungiyar tafi dukkanin kungiyoyi Dubu Muhimmanci a cikin AL'UMMA, Sannan ya tabbatar mana da jin dadinsa bisa BAYANIN da aka gabatar, kungiyar ta samu Mallakar Rejista da Gwamnatin tarayya.
Daga Karshe yayi Nasihu masu Muhimmanci tare da Jan hankali da NUSARWA ga wannan kungiyar sannan yayi jawabai masu tasiri da harshe irin na manya kuma yayi Alƙawarin bata cikakken goyon baya.
Allah ya karawa wannan kungiyar Albarka
Allah ya karawa Jagororin ta Albarka
kuyi Sharring Da Following Domin Tarayya Cikin Lada
Yakubu Dauda Hussaini
Sakataren Watsa labarai
Zaitunah Orphans Association Tulai
16-04-2026/1447.