K-Mashi Voice

K-Mashi Voice Address: Wulshiri Sports Arena, Down Garage. 0816 597 9397

•An online community news outlet that keeps you updated about the happenings around K-Mashi Community.
•A medium for advocacy on community development and promotion of peaceful coexistence.

ABU-FAAIZ LEARNING ACADEMY – NA NEMAN  MALAMAI DA DALIBAI!ABU-FAAIZ LEARNING ACADEMY, da ke No. 4 Captain Road, Kurmin M...
19/08/2026

ABU-FAAIZ LEARNING ACADEMY – NA NEMAN MALAMAI DA DALIBAI!

ABU-FAAIZ LEARNING ACADEMY, da ke No. 4 Captain Road, Kurmin Mashi, Kaduna, na sanar da buɗe karɓar sabbin ɗalibai domin zangon karatu na 2026/2027 a matakan Day Care, Nursery, Primary da Secondary, tare da ɓangaren Islamiyya da Tahfiz.

Haka kuma, makarantar na neman ƙwararrun malamai a ɓangaren Boko da Islamiyya, waɗanda ke da ƙwarewa (experience) na aƙalla shekaru 2.

Ku garzaya ku yi rijistar yaranku yanzu domin ingantaccen ilimi mai haɗa ilimin Boko da na Addinin Musulunci.

📞 +234 803 699 0375
📧 [email protected]
📍 No. 4 Captain Road, Kurmin Mashi, Kaduna

ABU-FAAIZ LEARNING ACADEMY – Ilimi mai inganci, tarbiyya mai kyau!

18/08/2026

K-Mashi Voice ta kai ziyara Government College Kurmin Mashi, Kaduna domin ganin yadda rabon takin Zamani ke cigaba da gudana wanda gwamnan jihar Kaduna ya ware domin ba wa manoma.

Kabiru Salisu ya bar Ranchers Bees, ya koma Saudi ArabiaDan wasan ƙwallon ƙafa Kabiru Salisu ya bar ƙungiyar Ranchers Be...
18/08/2026

Kabiru Salisu ya bar Ranchers Bees, ya koma Saudi Arabia

Dan wasan ƙwallon ƙafa Kabiru Salisu ya bar ƙungiyar Ranchers Bees, bayan da ya kulla yarjejeniya da ƙungiyar Al-Jabalain FC ta ƙasar Saudi Arabia. 🇸🇦⚽

Ranchers Bees ta tabbatar da tafiyar dan wasan, inda ta bayyana godiyarta ga Kabiru Salisu bisa gudummawar da ya bayar a lokacin da yake wakiltar ƙungiyar.

Ƙungiyar ta kuma yi masa fatan samun nasara da ci gaba a sabon babin rayuwarsa ta ƙwallon ƙafa a Saudi Arabia.

Wannan mataki na zuwa ne a matsayin sabon ƙalubale ga Kabiru Salisu, yayin da zai fara fafatawa a gasar ƙwallon ƙafa ta Saudi Arabia tare da Al-Jabalain FC.

K-Mashi Voice na taya Kabiru Salisu murnar wannan sabon mataki, tare da yi masa fatan samun nasara a sabon kulob ɗinsa. 🤝⚽🇸🇦

MUHADARAR DALIBAI: KUNGIYAR HADIN KAN MAKARANTUN ISLAMIYYUN AHLUS-SUNNAH TA KURMIN MASHI TA SHIRYA TARO NA ILIMANTARWAKu...
17/08/2026

MUHADARAR DALIBAI: KUNGIYAR HADIN KAN MAKARANTUN ISLAMIYYUN AHLUS-SUNNAH TA KURMIN MASHI TA SHIRYA TARO NA ILIMANTARWA

Kungiyar Hadin Kan Makarantun Islamiyyun Ahlus-Sunnah ta Kurmin Mashi, Kaduna, ta shirya wata muhimmiyar muhadara ga dalibai, domin wayar da kansu kan muhimmancin neman ilimi da kuma yadda za su yi amfani da ilimin da suke samu wajen inganta rayuwarsu da al’umma.

Shugaban kungiyar, Dr. Muhammad Salis Abdulhamid, wanda aka fi sani da Ustaz Nahda, kuma limamin Masallacin Aliyu bn Usman da ke NDA Road, ne ke jagorantar kungiyar tare da hadin gwiwar sauran malamai.

Kungiyar ta shafe kimanin shekaru takwas tana gudanar da ayyukan ilimantarwa da bunkasa ilimin addini a unguwar Kurmin Mashi, Kaduna.

A yayin muhadarar, babban malamin addini, Malam Aminu Ibrahim Sautus-Sunnah, ya gabatar da karatun ranar Lahadi da safiya, inda ya yi bayani kan muhimmancin neman ilimi, fahimtarsa da kuma wajabcin aiki da abin da mutum ya koya.

Taron ya samu halartar malamai da dama, shugabannin makarantun Islamiyya, da iyaye, musamman iyaye mata daga sassa daban-daban na Kurmin Mashi. Haka kuma, Sarkin Sabon Layi, Malam Abdullahi Rabo, ya kasance cikin manyan bakin da s**a halarci taron.

An gudanar da muhadarar ne a Masallacin Yar Makwallan, Sabon Layi, Kaduna, inda mahalarta s**a samu damar sauraron darussa da nasihohi masu muhimmanci.

Masu shirya taron sun bayyana fatan cewa mahalarta za su amfana da darussan da aka gabatar, tare da daukar nauyin amfani da ilimin wajen kyautata rayuwarsu da al’umma.

Daga Abu Hisham, K-Mashi Voice.

Korafe-korafe Kan Rabon Takin Zamani a Government College Kurmin-MashiRahotanni daga Government College Kurmin-Mashi sun...
17/08/2026

Korafe-korafe Kan Rabon Takin Zamani a Government College Kurmin-Mashi

Rahotanni daga Government College Kurmin-Mashi sun bayyana yadda wasu daga cikin al’ummar da s**a je wurin rabon takin zamani s**a fuskanci wahalhalu, inda wasu s**a shafe lokaci suna jiran samun takin, amma daga bisani s**a koma gidajensu babu komai.

Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun koka da yadda ake gudanar da rabon, suna bayyana cewa tsarin bai kasance a fili kuma cikin saukin kai ba. Mafi muni, wasu daga cikin masu neman takin sun zargi cewa ana karbar wasu kudade daga hannun jama’a da sunan kudin tsaro (security) kafin a ba su damar samun takin.

Sai dai abin da ya kara janyo damuwa shi ne, wasu daga cikin wadanda aka ce sun biya wadannan kudade sun bayyana cewa duk da biyan kudin, ba su samu takin ba.

Wannan yanayi ya haifar da tambayoyi masu muhimmanci kan yadda ake gudanar da rabon takin, musamman game da gaskiya, adalci da kuma yadda ake sarrafa duk wani kudi da ake karba daga hannun al’umma.

Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa, musamman wadanda ke da alhakin kula da rabon takin, da su gaggauta binciken wadannan korafe-korafe domin tabbatar da cewa tallafin noma ya isa ga wadanda aka tanadar wa, ba tare da wariya, cin zarafi ko wani nau’in almundahana ba.

Idan har ana karbar kudin tsaro, ya kamata a bayyana dalilin karbar kudin, adadin da ake karba da kuma inda kudin ke tafiya. Haka kuma, ya kamata a tabbatar da cewa babu wani manomi da zai rasa hakkinsa saboda rashin biyan wani kudi da ba a sanar da shi tun farko ba.

Al’umma na da hakkin sanin yadda ake gudanar da irin wannan rabon, yayin da hukumomi ke da alhakin tabbatar da gaskiya da adalci domin kauce wa duk wani abu da zai iya lalata amincewar jama’a.

16/08/2026

Cigiya! Cigiya!! Cigiya!!!

Allah ya bayyana iyalanta.

Domin karin bayani, za ku iya tuntubar wannan lambar waya?

Lajnatu Ansarillah Kurmin Mashi Ta Rabawa Al’umma Kyautuka Domin Murnar Shigowar Mauludi -Rabi’ul AwwalWakilin mu Basiru...
14/08/2026

Lajnatu Ansarillah Kurmin Mashi Ta Rabawa Al’umma Kyautuka Domin Murnar Shigowar Mauludi -Rabi’ul Awwal

Wakilin mu
Basiru Idris

Kungiyar Lajnatu Kurmin Mashi ta gudanar da wani shiri na musamman a yau 14/8/2026 domin murnar shigowar 1 ga watan Rabi’ul Awwal, inda ta raba kyautuka tare da biyan kuɗin sufuri ga wasu matafiya.

Shirin na daga cikin ayyukan alheri da kungiyar ke gudanarwa domin faranta ran al’umma da tunawa da shigowar watan Mauludi.

Kungiyar ta bayyana fatanta na ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da hidima ga al’umma.

Allah Ya saka musu da alheri, Ya sa albarka a wannan wata mai albarka. 🤲🏽

11/08/2026

Ana cigiyar iyalan wannan matar da aka gani a Dahiru Road, Kurmin-Mashi, Kaduna.

Domin karin bayani, ku tuntube wannan lambar waya: 07033195744
Mai Unguwa Dahiru Road

10/08/2026

Dan takarar kujerar Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya a Jam'iyyar PRP, Hon. Munir Sulaiman Babangida (Babs), ya kai ziyara unguwar Kurmin-Mashi a yau Lahadi, inda ya gana da kungiyoyi masu zaman kansu tare da wasu daga cikin shugabannin al’umma.

SHUGABAN AJAK FURNITURE YA BA SULEIMAN EVERGREEN SCHOOL TALLAFIN NAIRA MILIYAN 1Daga Aminu Abubakar Yahuza Shugaban kamf...
09/08/2026

SHUGABAN AJAK FURNITURE YA BA SULEIMAN EVERGREEN SCHOOL TALLAFIN NAIRA MILIYAN 1

Daga Aminu Abubakar Yahuza

Shugaban kamfanin AJAK Furniture & Interior Company da ke Kurmin-Mashi, Kaduna, ya bayar da tallafin naira miliyan 1 ga makarantar Suleiman Evergreen School, a wani bangare na kokarin tallafawa ci gaban ilimi da inganta gine-ginen makarantar.

An bayyana wannan tallafi ne a yayin bikin Speech and Prize-Giving Day na makarantar, wanda aka gudanar a harabar makarantar da ke Commander Close, Kurmin-Mashi, Kaduna.

Taron ya samu halartar manyan baki da s**a hada da sarakunan gargajiya, shugabannin unguwanni, ‘yan siyasa, shugabannin al’umma, iyayen dalibai da sauran jama’ar gari.

Mai bayar da tallafin, wanda tsohon dalibi ne a makarantar kuma shugaban dalibai na farko, ya bayyana cewa wannan gudunmawa na daga cikin kokarinsa na mayar da alheri ga makarantar da ta ba shi ilimi.

Rahotanni sun nuna cewa makarantar na neman kimanin naira miliyan 120 domin kammala wasu muhimman ayyukan gine-gine da za su kara inganta harkokin koyarwa da ilmantarwa. Haka kuma, sauran tsoffin daliban da s**a halarci taron sun bayar da nasu gudummawar domin tallafawa wannan buri.

An kammala taron cikin nasara, inda aka raba kyaututtuka ga dalibai da s**a yi fice a karatu tare da karrama wasu mutane da s**a bayar da gagarumar gudummawa wajen ci gaban makarantar.

Address

Kurmin Mashi Kaduna
Kurmin Mashi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when K-Mashi Voice posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to K-Mashi Voice:

Shortcuts

Share