20/01/2023
Assalamu alaikum warahamatullahi wabarakatuhu
Yakai dan uwar rabin jiki karka manta da fadar manzo (S.A.W) dukkan ku masu kiwo ne.
Sannan za'a tambaye ku game da kiwon da'aka baku,to kasani haka zumunci Idan baka sada shiba za kayi bayanin ka a gaban Allah.
Kar jaga Allah ya baka mulki,kudi,karfi,ilimi da sauran su ka raina wani don kana ganin shi kaskantacce ne, bakai kaba kanka ba, ba dubarar ka bace ba, domin Allah zai iya kwacewa cikin dakika daya kamar ba'ayi kaba, kuma ma inka wulakanta ma daga karshe su kare koka mutu kabar su domin gidan ka daka gina wanda babu mai kamar shi a families inku, ko garin ku ko kasarku za'a fitar da kai kamar yanda ake fitar da kayan daki Idan An canza sabbi.
Idan ka mutu baza ayima Kara ba akaika a motar da kafi so akan kowa ba,a makara za'a sakaka kamar yanda akasa ka wanda kake gani kaskantacce, kuma a farin yadi za'a sakaka kamar yanda akasa kowa,kuma makabarta ba ta mai kudi ba ta talakka.
Don haka ina nasihantar mu damu gyara tun kafin mutuwa ta riske mu, mu gyara zumunci domin yanzu da uba ya mutu gida ya mutu,da uwa ta mutu daki ya mutu,da aboki ya mutu aboki ya manta da iyalan abokin sa,da dan'uwa ya mutu dangi ba ruwan su da iyalan sa, da amini ya mutu amini zai fara cin ganima da dukiyar marayu,
Sannan ma abin haushi ba taimakon yan'uwa sai shar'holiya,kaine kanshi kisi wurin fati amma baka iya daukar nauyin mararsa lafiya a dangin ka, Zaka iya kashe ko nawane a hidimar ka ta duniya amma Naira dubu goma ta gagara wajen gyara lafirar ka.
Don haka mu tanaji mi zamu fada ma Allah a kan yace muyi zumunci munki.
Bissalam ga wanda na bata ma rai Allah yaba shi hakuri.
Signed
Ismail Abdullahi Balarabe
Director General
Katsina youth development and enlightenment forumΒ©