Youth Movement For Justice and Community Development

Youth Movement For Justice and Community Development Lets the youth join the onrush...

To achieve and build a batter tomorrow and developed our state in particular and Nigeria in general.

12/08/2024

Assalamu alaikum!

Barkan mu da wannan lokaci.

Hakika ƴan'uwa Matasa yanayi ya sauya, Rayuwa tayi daban, muna cikin ƙalubale, gami da ƙara tunkarar wasu ƙalubalen da yawa nan gaba idan har ba muyi abinda ya dace ba.

Menene abinda ya dace?

Babban dalilin da ya haddasa mana tarin matsaloli a Najeriya musamman ma kuma yankin mu na Arewa shine rashin ingantaccen Shugabanci, shuwagabannin mu tun daga mataki na ƙasa har zuwa sama sun rasa tsantsar kishin al'umma, da tausayin al'ummomin da suke Jagoranta, gami da karin wasu dalilan da s**a haɗa da rashin ayyukan yi a tsakanin Matasan mu.

A ta ɗayan ɓangaren kuma, muma da namu matsalar, domin idan gaskiya tazo kamata yayi a faɗe ta, mun rasa karshashi, da ƙwarin guiwa yin haɗaka wajen fuskantar matsalolin da ke addabar mu, wasun mu nada ra'ayin cewa ba zamu iya ba, don haka kar ma mu soma. Wasu matasan kuwa da s**a samu damar shiga cikin gwamnati, to suna makancewa ne wajen kare ɗan abinda suke samu ba tare da yin la'akari da cewa dubban al'umma suna cikin mawuyacin hali ba.

Adalci daya ne, kuma duk wanda yayi shi ko aka yi shi a gaban shi ya sani, don haka mu Matasa mu sani babu abinda yafi ƙarfin mu, mu haɗa kai mu zage damtse cikin zumma da kishi, da yardar Allah za mu cimma duk wata buƙata da muka sanya a gaba.

Ina ta faɗin haka ne a sabili da kowa yasan halin da ƙasar nan take ciki, kuma yanzu zamani ne na wayewa, wanda a halin yanzu kowa ya ɗan fahimci musabbabin fuskantar waɗannan matsaloli. Masu iya magana su kace gano Matsala, kaso hamsin ne na maganinta.

Me ya rage mana? Mu yi tunani duk wata hanya da muke ganin mafita ce ga al'ummar mu dai-dai da yadda za mu iya bada gudummawa, to mu yi hakan. Tabbas za mu iya, haɗin kai kawai shine makamin.

Wannan shine abinda ya dace, kuma ya kamata mu yi.

Muna rokon Allah ya datar da mu.

✍️Lukman Aliyu Iyatawa

12/08/2024

Wato fa 'Yan Majalisun Tarayya da Sanatocin-mu idan ba zaku tsaya mana akan Zaluncin da ake mana a Gwamnatance ba, to Insha Allahu zamu ci gaba da yunkurin dawo da ku gidajen ku. Kuma da yardar Allah zamuyi Nasara.

Ace Gwamnati zata Gina Gidaje Dubu 6 daga cikin kudin tallafin Man Fetur da ta cire a Nigeria, Amma Lagos Kadai nada 2500 sai Kano 500 kawai, Sauran jihohi wasu bama zasu Samu ko 1 ba, wai a kowane Zone state 2 za'a ginawa 250. Kuma wai a haka Ministan Gidajen Nan ma Dan Katsina ne.

Wane irin rashin Adalci ne Nan, Kuma sai kuyi shiru.

✍️Naziru Abdullahi Batsari

Assalamu alaikum ƴan'uwa Matasa masu albarka, abin alfaharin kowace al'umma, tsanin nasara da garkuwa ga kowace al'umma....
11/08/2024

Assalamu alaikum ƴan'uwa Matasa masu albarka, abin alfaharin kowace al'umma, tsanin nasara da garkuwa ga kowace al'umma.

Kamar yadda muka sani cewa Matasa sune kashin bayan kowace al'umma, don haka yana da muhimmanci Matashi ya san wannan tasirin nashi a cikin al'umma.

Ƴan'uwa da yawa sun tsinci kan su a wannan gida na dandazon Jajirtaccin Matasa wadanda aka zaƙulo su ta la'akari da cancantarsu ta fuskar, ilimi, zamantake, wayewa, sanin Yakamata da sauransu.

Don haka muke sanar da ku cewa wannan gida yana a karkashin wata ƙungiya mai suna YOUTH MOVEMENT FOR JUSTICE AND COMMUNITY DEVELOPMENT (YMJCD) kamar yadda kuka gani a rubuce.

Wannan ƙungiya Matasa ne s**a kafata, tare da bin duk wani tsari da kundin tsarin Mulkin Najeriya ya gindaya, da nufin gudanar da ayyuka da s**a shafi cigaban Matashi da kuma al'ummar da yake rayuwa a cikin su.

Ya zuwa yanzu, wannan ƙungiya tayi ayyuka da dama, tare da ƙulla abota da manyan kungiyoyi a matakin ƙasa baki daya domin samun karfin gudanar da ayyukan ta yadda ya kamata.

Da haka nake kira tare neman hadin kai da goyon baya ga kowace mamba da ya tsinci kan shi a nan, tare da Kasancewa Matashi abin alfahari, gami da yin duk mai yiwuwa wajen ganin ya bada gudummawar sa domin cigaban al'umma dai-dai gwargwadon zummar sa.

Sa'annan kuma ina kira a gare mu da muji tsoron Allah, mu zamo Jakadun al'umma na ƙwarai, duk wani abu da kasan cewa tsani ne na nasara gare ka da Matashi ɗan'uwan ka da kuma al'umma, to ka tashi tsaye domin ganin ka tabbatar da shi.

Da fatan Allah madaukakin sarki yayi riƙo da hannayen mu, yayi mana Jagoranci, ya koma yi mana maganin matsalolin da s**a dabaibaye ƴan Najeriya baki ɗaya.

✍️ Lukman Aliyu Iyatawa
11th August, 2024.

Address

Kofar Kaura Katsina
Katsina

Telephone

+2348036675113

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Youth Movement For Justice and Community Development posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Youth Movement For Justice and Community Development:

Share