12/08/2024
Assalamu alaikum!
Barkan mu da wannan lokaci.
Hakika ƴan'uwa Matasa yanayi ya sauya, Rayuwa tayi daban, muna cikin ƙalubale, gami da ƙara tunkarar wasu ƙalubalen da yawa nan gaba idan har ba muyi abinda ya dace ba.
Menene abinda ya dace?
Babban dalilin da ya haddasa mana tarin matsaloli a Najeriya musamman ma kuma yankin mu na Arewa shine rashin ingantaccen Shugabanci, shuwagabannin mu tun daga mataki na ƙasa har zuwa sama sun rasa tsantsar kishin al'umma, da tausayin al'ummomin da suke Jagoranta, gami da karin wasu dalilan da s**a haɗa da rashin ayyukan yi a tsakanin Matasan mu.
A ta ɗayan ɓangaren kuma, muma da namu matsalar, domin idan gaskiya tazo kamata yayi a faɗe ta, mun rasa karshashi, da ƙwarin guiwa yin haɗaka wajen fuskantar matsalolin da ke addabar mu, wasun mu nada ra'ayin cewa ba zamu iya ba, don haka kar ma mu soma. Wasu matasan kuwa da s**a samu damar shiga cikin gwamnati, to suna makancewa ne wajen kare ɗan abinda suke samu ba tare da yin la'akari da cewa dubban al'umma suna cikin mawuyacin hali ba.
Adalci daya ne, kuma duk wanda yayi shi ko aka yi shi a gaban shi ya sani, don haka mu Matasa mu sani babu abinda yafi ƙarfin mu, mu haɗa kai mu zage damtse cikin zumma da kishi, da yardar Allah za mu cimma duk wata buƙata da muka sanya a gaba.
Ina ta faɗin haka ne a sabili da kowa yasan halin da ƙasar nan take ciki, kuma yanzu zamani ne na wayewa, wanda a halin yanzu kowa ya ɗan fahimci musabbabin fuskantar waɗannan matsaloli. Masu iya magana su kace gano Matsala, kaso hamsin ne na maganinta.
Me ya rage mana? Mu yi tunani duk wata hanya da muke ganin mafita ce ga al'ummar mu dai-dai da yadda za mu iya bada gudummawa, to mu yi hakan. Tabbas za mu iya, haɗin kai kawai shine makamin.
Wannan shine abinda ya dace, kuma ya kamata mu yi.
Muna rokon Allah ya datar da mu.
✍️Lukman Aliyu Iyatawa