Taskar Alheri Media

Taskar Alheri Media Taskar Alkhairi Shafi ne da ke kawo muku sahihan labarai, sharhi da nazari kan harkokin siyasar Najeriya cikin harshen Hausa. Ku biyo mu
(1)

Muna tare da ku daga Abuja har zuwa Sakkwato.

YANZU YANZU: An Rantsar da Murtala Sule Garo a Matsayin Mataimakin Gwamnan Jahar Kano An rantsar da Murtala Sule Garo ne...
05/05/2026

YANZU YANZU: An Rantsar da Murtala Sule Garo a Matsayin Mataimakin Gwamnan Jahar Kano

An rantsar da Murtala Sule Garo ne yayin wani ƙwarya-ƙwaryan biki a gidan gwamnatin jihar a ranar Talata 05/05/26, inda sabon mataimakin gwamnan ya ce zai yi aiki tuƙuru don ciyar da gwamnatin Abba Kabir Yusuf gaba dama Jahar Baki Daya.

Naɗin Garo na zuwa ne bayan murabus ɗin da Comrade Aminu Abdussalam ya yi a watan Maris.

Gwamnan Jihar kano abba kabir yusuf zai Rantsar da mataimakinsa Wato Murtala sule Garo a gobe talata 04/05/26Hakan na da...
04/05/2026

Gwamnan Jihar kano abba kabir yusuf zai Rantsar da mataimakinsa Wato Murtala sule Garo a gobe talata 04/05/26

Hakan na dauke ne cikin wata Sanarwa da mai bawa gwamnan shawara kan harkokin yada labarai, Ibrahim Adam, ya fada

Sanarwar ta ce za'a gudanar da bikin rantsuwar ne da karfe 11 na safe a zauren Coronation Hall da ke gidan gwamnatin Kano.

Kwankwaso da Peter obi sun koma jam’iyyar NDCManya Mayan Yan adawa, Rabiu Kwankwaso da Peter Obi, sun karɓi katin jam'iy...
03/05/2026

Kwankwaso da Peter obi sun koma jam’iyyar NDC

Manya Mayan Yan adawa, Rabiu Kwankwaso da Peter Obi, sun karɓi katin jam'iyyar ne bayan ficewa daga jam'iyar ADC saboda rikice-rikicen shugabanci da s**a ce sun dabaibaye ta.

Dukkansu sun karɓi katin NDC ne a hedikwatar jam'iyyar tare da jagoranta Hon. Seriake Dickson.

Peter Obi ya tabbatar da ficewar sa daga jam’iyyar ADC Hakan na zuwa ne Cikin wata sanarwa da ya fitar, Mista Obi ya ce ...
03/05/2026

Peter Obi ya tabbatar da ficewar sa daga jam’iyyar ADC

Hakan na zuwa ne Cikin wata sanarwa da ya fitar, Mista Obi ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon rigingimun cikin gida da s**a dabaibaye jam'iyyar ADC.

Ku biyo mu Ƙarin bayani na nan tafe

“Muna cigaba da zurfafa tuntuba ciki harda jagororin jam’iyyun NDC,PRP da wasun su don samun zabi mafi dacewa da zai kar...
03/05/2026

“Muna cigaba da zurfafa tuntuba ciki harda jagororin jam’iyyun NDC,PRP da wasun su don samun zabi mafi dacewa da zai kare muradunmu na dimokradiyya”

Cewar Jagoran Darikar Kwankwasiyya

Sanata Kwankwaso, wanda jigo ne a jam'iyyar ADC, ya bayyana hakan ne bayan raɗe-raɗin da ake yi game da makomarsa a siyasa, duba da irin ƙalubalen da jam'iyyar ke fuskanta.

Ya kuma jaddada cewa har yanzu bai yanke shawara game da makomarsa da na abokan hulɗar siyasarsa ba, sai dai ya ce nan ba da jimawa ba, za su sanar da matsayarsu.

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce har yanzu bai yanke hukunci na karshe kan makomarsa ta siyasa ko ...
02/05/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce har yanzu bai yanke hukunci na karshe kan makomarsa ta siyasa ko ta magoya bayansa ba, duk da rade-radin da ake yi kan yiwuwar sauya sheka daga jam’iyyar ADC.

A wata sanarwa da ya fitar, Kwankwaso ya ce akwai bayanai masu rudani da ke yawo a kafafen yada labarai dangane da matsayinsa a siyasa, musamman bayan matsalolin da ke addabar ADC.

Ya bayyana cewa hukuncin kotun koli da ya tabbatar da halascin kwamitin gudanarwa na kasa karkashin jagorancin David Mark ya kuma mayar da shari’ar zuwa babbar kotu, lamarin da ya sanya jam’iyyar cikin wani yanayi mai sarkakiya.

Kwankwaso ya kara da cewa wata babbar kotun tarayya ta kuma soke halascin babban taron jam’iyyar na baya-bayan nan, yayin da babban lauyan gwamnatin tarayya ya nemi wata kotu ta soke rajistar ADC.

Tsohon ministan tsaron ya ce sun fice daga jam’iyyar NNPP ne saboda matsalolin shari’a da ya ce wasu na waje s**a haddasa, yana mai cewa yanzu ADC ma tana fuskantar irin wannan matsala.

Saboda haka, ya ce shi da sauran masu ruwa da tsaki sun fara tuntubar wasu jam’iyyu da shugabanninsu ciki har da NDC da PRP domin duba mafi alherin mataki na kare muradunsu na siyasa da dimokuradiyya.

Kan batun takarar shugaban kasa kuwa, Kwankwaso ya ce bai bayyana aniyar tsayawa takara ba, kuma bai goyi bayan kowane dan takara ba. Ya tuna cewa a zaben fidda gwani na APC a 2014 ya zo na biyu bayan Muhammadu Buhari, sannan a 2019 ya nemi tikitin PDP kafin daga bisani ya mara wa Atiku Abubakar baya bayan ya lashe zaben fidda gwani.

Kwankwaso ya ce a kullum yana fifita hadin kan jam’iyya da muradun kasa sama da bukatun kansa.

Ya kuma bayyana cewa rashin halartarsa a tarukan masu ruwa da tsaki na ADC guda biyu da aka yi kwanan nan ya faru ne saboda wasu uzurori na kashin kai, kuma ya sanar da shugabannin jam’iyyar tun da wuri.

A karshe, ya ce duk wani hukunci da zai dauka game da alkiblarsa ta siyasa za a sanar da shi ne ta hanyoyin hukuma a lokacin da ya dace.

YANZU-YANZU: Peter Obi zai fice daga jam’iyyar ADC.Wasu majiyoyi na cikin sirri sun ce “an riga an yanke shawara” bayan ...
02/05/2026

YANZU-YANZU: Peter Obi zai fice daga jam’iyyar ADC.

Wasu majiyoyi na cikin sirri sun ce “an riga an yanke shawara” bayan hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke kan rigingimun shugabancin jam’iyyar ta ADC.

Rabiu Musa Kwankwaso “ya amince gaba ɗaya” kuma “yana tafiya daidai da wannan shawara,” inda ɓangarorin biyu s**a amince cewa “tsayawa a ADC a ƙarƙashin waɗannan yanayi haɗari ne da ba mu son shiga.”

Majiyoyin da ke cikin tattaunawar sun bayyana halin da ake ciki a fili cewa “kunshin magudi ne kawai,” s**a ƙara da cewa “shirinsu mai sauƙi ne, a kawo kowa a ciki, sannan a fitar da su ta hanyar fasaha.”

Wani babban jami’in cikin sirri ya faɗa : “Da zarar wannan ya kai Kotun Tarayya, to an gama. Ba wanda zai iya ceton ku.”

A kan rikicin cikin gida, majiyoyin sun ce matsayin Atiku Abubakar ya “rufe ƙofa kwata-kwata,” suna nanata cewa “ƙin da ya yi na sauka ya ƙara taurare komai, babu hanyar ci gaba a wannan hali.”

Janyewa ya riga ya fara. Obi da Kwankwaso “sun ja baya da gangan,” yayin da “tattaunawar neman wani sabon dandamali ba bincike ba ne kuma, sun kai mataki na gaba.”

“Kotun Ƙoli ba ta warware kome ba,” in ji wata majiya. “Ta ƙara munana al’amarin, kuma haɗarin shari’a na can rataye.”

“Wannan ba kila-kila ba ne,” wata majiya ta ƙara da cewa. “Abin yana faruwa. Abin da ya rage kawai shi ne lokaci.”

Tsohon kwamishinan kasuwanni na Kano kuma jigo a kwankwasiyya, Alhaji Shehu Wada Sagagi ya ce shiri yayi nisa wajan shig...
02/05/2026

Tsohon kwamishinan kasuwanni na Kano kuma jigo a kwankwasiyya, Alhaji Shehu Wada Sagagi ya ce shiri yayi nisa wajan shigar jagoran kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, cikin jami’iyyar NDC, sakamakon rikicin da ya dabaibaye jami’iyyar ADC.

Sagagi ya kara da cewa, shari’un dake gaban kotuna daban daban zai taimaka wajan hana jami’iyyar ta ADC samun nasara a zaban shekarar 2027.

A gefe guda ,rahotanni sun nuna cewa Kwankwaso zai haɗu da Peter Obi a jam’iyyar NDC, inda ake sa ran su fito takara tare a zaɓen shugaban ƙasa, a ƙarƙashin tikitin haɗin gwiwa na Obi-Kwankwaso.

Gwamnan Kano abba Kabir yusuf yayi alkawarin biyan bashin duka ragowa kudin da yan fansho suke bi kafin wa’adinsa na far...
01/05/2026

Gwamnan Kano abba Kabir yusuf yayi alkawarin biyan bashin duka ragowa kudin da yan fansho suke bi kafin wa’adinsa na farko ya kare

Gwamna Abba Kabir Yusif ne ya bayyana hakan, lokacin da yake jawabi a wajen bikin ranar ma’aikata ta duniya, wanda aka gudanar a filin wasa dake kofar mata.

Gwamna Yusif ya ce gwamnatin sa ta gaji bashin kudin ‘yan fansho da yawan su ya kai naira biliyan 48 daga tsofaffin gwamnatocin da s**a gabaci ta shi, sai dai kawo yanzu ya biya kimanin naira biliyan 32, inda ya rage saura biliyan 16.

Hukumar zaɓe ta kasa INEC ta sabunta bayanan da ke shafinta na intanet inda ta sanya David Mark a matsayin shugaban jam’...
01/05/2026

Hukumar zaɓe ta kasa INEC ta sabunta bayanan da ke shafinta na intanet inda ta sanya David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa, tare da Rauf Aregbesola a matsayin sakataren jam’iyyar na ƙasa, bayan hukuncin kotun koli.

An gano wannan sauyi ne a yammacin ranar Alhamis, lamarin da ya sauya matsayar da INEC ta ɗauka a farkon watan Afrilu lokacin da ta cire shugabancin bangaren David Mark daga shafinta, tana mai danganta hakan da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara kan rikicin shugabancin ADC.

Bangaren David Mark da kuma Nafiu Bala, na ikirarin shugabancin jam’iyyar

Me zaku ce akan hakan?

Ba gaskiya ba ne labarin cewa matasa sun ƙone gidan Nafiʼu Bala a jihar Gombe.Kakakin ƴan sandan jihar ASP Buhari Abdull...
30/04/2026

Ba gaskiya ba ne labarin cewa matasa sun ƙone gidan Nafiʼu Bala a jihar Gombe.

Kakakin ƴan sandan jihar ASP Buhari Abdullahi ne ya tabbatar da hakan, Ya ce labari ne na ƙanzon kurege wasu masu son tada hankali ke yaɗawa.

Ya ƙara da cewa, unguwar da ake magana ma ba a nan Nafiʼun ya ke ba, yanki ne da iyayensa su ke, kuma babu wani abu da ya faru.

Har zuwa yanzu mazauna yankin da ake yaɗawa sun tabbatar da cewa babu gaskiya a labarin.

Kazalika an soma yaɗa hotunan ne tunda yammaci, amma kuma hotunan sun nuna lokaci ne na dare.

Address

Zoo Road, Kumbotso LGA
Kano
700101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskar Alheri Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share