03/07/2025
(FALALAR AZUMIN TASU'A DA ASHURA)
Manzon Allah ﷺ Yace : Idan Allah Ya Rayani Zuwa Shekara Mai Zuwa Zan Azumci Ranar Tara Ga Wata (Tasu'a).
Sahih Muslim (1162)
Manzon Allah ﷺ Yace : Yin Azumin Ranar (Ashura), Ina Fata A Wajen Allah Zai Kankare Zunubin Shekarar Da Ta Gabace Shi.
Sahih Muslim (1134)
Kuma A Wani Hadisin Manzon Allah ﷺ
Yace: "Allah (Ta'ala) Ya Faɗa A Cikin Hadisi Qudusiy : "Dukkan Ayukkan Ɗan Adam Nasa Ne, Face Azumi, Wannan Nawa Ne, Ni Nake Sakayya Da Shi"
Sahih Al-bukhari (1904)
Sahih Muslim (1151)
Wanda Babu shakka Azumin Ranakkun Tasu'a da Ashura suna ciki.
Hakama!
Manzon Allah ﷺ Yace: Duk Wanda Ya Yi Azumi A Wata Rana Saboda Allah,
Toh, Allah (Ta'ala) Zai Nisanta Fuskar Sa Daga Wuta Tsawon Shekara 70.
Sahih Al-bukhari (2840)
Sahih Muslim (1153)
Wanda Shima Babu Shakka Azumin Ranakkun Tasu'a da Ashura suna ciki.
TASU'A ranar 9 ga Watan MUHARRAM 1447, zai yi daidai da Ranar JUMU'A 4 ga Watan July 2025.
ASHURA ranar 10 ga Watan MUHARRAM 1447, zai yi daidai da Ranar ASSABAR 5 ga Watan July 2025.
Ƴan'uwa musulmi ina mai tunatar da mu, da mu dauki ranakun Tasu'a da Ashura da matuqar Muhimmancin.
Mu yi kokari wajen yin ibadah a wadannan ranaku masu darajja ta hanyar yin azumi da Addu'o'i da bayar da sadaka da sauran ayyukan Alkhairi.
Sa'annan Ina Kara kira ga ƴan uwa musulmi, da mu ci gaba da hada kawunanmu, kuma mu hada karfi da karfe wajen kiyaye addininmu.
Mu taru a matsayin ƴan uwa, domin kare Martaba Da kuma koyarwar addininmu.
Allah Ubangiji Ya bamu ikon Azumtar kwanakin nan na TASU'A da ASHURA Masu Albarka (Ameen).