Almutasaddiqun Charity Foundation

Almutasaddiqun Charity Foundation Don samar da makaranta WAQAFI ta marayu, karatun boko da na Islamiyya da koyon sana'o'i

06/06/2026

*KARATUNMU NA EXTRA LESSON*
*Ranar Asabar– 20th Z.Hajj, 1447 | 6th June, 2026*

Wannan karatu na musamman an shirya shi ne *kyauta FISABILILLAH* tare da ɗaukar nauyi daga:

*ALMUTASADDIQUN CHARITY FOUNDATION*

Ana gabatar da karatun ne a *ranakun Asabar da Lahadi* *Da kuma lokacin hutu* don tallafa wa dalibai da ilimi mai amfani.

*ALLAH ya saka da alheri* ga dukkan waɗanda ke bada gudummawa don cigaban wannan cibiya mai albarka.

06/06/2026

*KARATUNMU NA HADDAR AL-QUR'ANI*
*Ranar Juma'a–19th Z.Hajj,1447, / 6th June, 2026.*
*Wanda ALMUTASADDIQUN CHARITY FOUNDATION s**a ɗauki nauyinsa.*

Wannan karatu ana shirya shi ne domin *marayu da marasa ƙarfi* *kyauta fisabilillah*, domin basu damar haddar Al-Qur’ani cikin tsabta da kulawa.

Ana gudanar da karatun ne a *ranakun Alhamis da Juma'a* a cibiyarmu.

*Allah ya saka da alheri* ga dukkan masu bayar da gudummawa da goyon baya ga wannan aiki na alheri a *ALMUTASADDIQUN CHARITY FOUNDATION*.

30/05/2026
28/05/2026

*BARKA DA SALLAH*
*Daga Daliban* *ALMUTASADDIQUN CHARITY* *FOUNDATION*
*تفبل الله منا ومنكم*

26/05/2026

*KUNDIN RANAR ARFA*

*KA SAN KUWA MATSAYIN YAU A WAJEN MASOYA?*

1. Yau ranar "Arafa", a yau masoyi babu Shi ba waige, takensa "La'ilaha illal Lahu Wahdahu la sharika Lahu, Lahul mulku wa Lahul hamdu wa huwa ala kulli shai'in kadir". Allah kadai yake duba.

2. A yau Allah zai kusanto zuwa saman duniya, Yana tambayar mala'iku: Me wadannan suke bukata, ga shi sun zo gashi a birkice, sun yi budu-budu haka? Sai su ce: Gafararka. Sai Ya ce: Na yi musu. (Muslim).

3. Masoya saboda murna a "Arafa" har kuka suke. Na gida kuwa saboda bege da soyayya wuni suke ba su sa komai a bakinsu ba, amma bakin ya kasa daina ambaton abin kauna.

4. Yayin da wani shaukinsa "fid dunya" ne masoyi kuwa dunya Wal akhira ne, ya sami dunya don ya isa lahira cikin aminci, don ya san a can ake angwanci, a can ake "budar Kai" a can ake "sayen Baki" a can za a yi masa "zaman ajo" a can Shugaba zai yi masa jagora ya ce: A bude kofa, don ya Kai mazaunin gaskiya a gaban sarki Mai iko.

5. Yi kukan shauki zuwa ga masoyi, yi sassarfan aikin alheri don nishadi ga abin kauna, yi rige-rige Kada ayarin masoya su barka a Kurar-baya.

6. Masoyinka Yana sauraron sakonka na salati don yau Juma'a, ga kuma Hailala da Kabbara da Hamdala zuwa ga abin da Ka fi so.

7. Mu yi addu'a Allah Ya Kai mu matakin Masoya Arifai, don sai da tsaninsa ake tattakawa a Kai gaci.

✒️ Dr. Abdulkadir Isma'il

25/05/2026

*KUNDIN ARFA*

*Daga Sheikh Dr. Abdulkadir Ismail*

_GOBE TAKE FA..._

1. Gobe Rana za ta hudo a *mafificin yini da Allah Yake so* .

2.Idan za Ka iya, Ka labe a wani masallacin da ba ruwanka da kowa sai nema a wajen Allah, to Ka yi, haka Sahabbai Abdullahi dan Abbas da Amru da Hurayyis ( RA) da Ada'u dan Rabah suke kwadaitar da mutane

3. Allah Ya sa Ka tashi da azumi, ba ka saurari maganar wadanda ba sa so su yi ba, bisa dogaro da Hijja Mai rauni

4. Yau ne Allah Yake alfahari da bayinSa a Arafa, idan ba ka can yi iron aikinsu, don rahamar Allah haka take kewaye masu manufa iri daya, kamar yanda Manzon Allah SAW Yana Tabuka, Amma ya ce wasu suna Madina Amma suna kwasar lada irin na su

5. Addu'a da zikiri ya fi komai a wannan yini. Yawaita addu'a domin Allah na daukowa a wannan yinin, sannan kuma ranar ce ta mafifiyar addu'a, Ka yi Kabbara a yi maka albishir da Aljanna, Ka Tasbihi a yi maka albishir da Aljanna.

6. Ka sani babu wata Rana da ake yanta bayi kamar wannan yinin na Arafa, Ka dage Ka zamo daya daga cikinsu.

7. Kada Ka manta, akwai idan akwai wani da Ka cuta, to ba mamaki ya Tanadi wannan yini don ya yi maka addu'ar Allah Ya bi masa hakkinsa, saboda haka Ka Kula da hakkin wasu Ka mayar Ka nemi yafiya.

Allah Kai ne Mai datarwa, Ka datar da mu, Ka karba mana, Ka yafe mana

25/05/2026

*TSOHUWAR AJIYA*

*Yau Take Arafah*
✍️Prof Mansur Sokoto, mni
Daga rubutun
Alhamis 8 Dhul Hajj 1442H (07/07/2021)

1. Yau talata 9 ga Dhul Hajji ita ce ranar Arafa.
2. Ita ce rana ta 9 daga cikin kwanukan shekara mafi daraja da falala a wurin Allah.
3. A ranar Arafat ne Allah ya kammala saukar da Alkur’ani ga Manzonsa a wurin Hajjin bankwana.
4. A wannan ranar Allah yana gafarta zunubai, ya yafe kurakurai, ya karba addu'oin bayinsa.
5. Allah ya rantse da wannan rana a inda ya ce:
(واليوم الموعود * وشاهد ومشهود)
Al-Yaumul Mau'úd shi ne yinin alkiyama, Sháhid shi ne ranar Arafa, Mashhúd shi ne ranar Jum'ah.
6. Kuma Allah ya rantse da ranar Arafa inda yake cewa: *"والشفع والوتر"* Shafa'i shi ne ranar layya, witiri shi ne ranar Arafa.
7. Hadisi ya inganta daga Manzon Allah (S) cewa, "babu wani yini wanda yake mafifici a wurin Allah fiye da yinin Arafa. Allah yana saukowa zuwa saman duniya sai ya yi kuri da mutanen kasa, ga mutanen sama". Sahihu Ibn Hibban 3583. Akwai hadisai da dama ingantattu a kan wannan. Duba Sahihu Muslim 1348 da Musnad Ahmad 8033.
8. A ranar Arafa ana son yawaita zikiri da addu'a. Kuma mafificiyar addu'a a ranar ita ce: *"LA ILAHA ILLALLAHU WAHDAHU LA SHARIKA LAHU, LAHUL MULKU WALHUL HAMD, WAHUWA ALA KULLI SHAI'IN QADEER"*.
Ana kuma son a yawaita fadin: *"SUBHANALLAH, WALHAMDU LILLAH, WA LA ILAHA ILLALLAH, WALLAHU AKBAR"*.
9. Magabata sun kasance a ranar Arafa suna aikata ayyuka iri daban daban na neman lada don samun gafarar Allah mahalicci.
10. An sunnanta yin azumi ga wanda ba ya aikin Hajji a wannan rana. Kuma ana fatar Allah zai yafe ma wanda ya yi shi zunubin bara da na bana.
11. Ana son mutum ya umurci iyalansa da yayansa - har kanana - su yi azumin ranar saboda gamewar falala da gafara.
12. Mutum yana iya yin azumin Arafa ko da ana bin sa bashin azumi. Idan kuma ya yi ramko a ranar babu laifi; ana sa ran zai samu karin falala saboda darajar wannan rana.
13. Babu laifi matafiyi ya yi azumin wannan rana idan ba zai sha wahala a kai ba.
14. Daga sallar asuba ta ranar Arafa ana so yin kabbarori bayan sallah *"ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLALLAHU, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMD"* daga nan har zuwa sallar la'asar a rana ta uku bayan sallah.
15. Daga cikin abubuwan da Annabi (S) ya roka a wannan rana akwai: gafara da jinkai da afuwa, da shiriya da tsarkin zuciya da sutura da wadatar arziki da lafiya da kamun kai da kariya da nasara da aminci da mafi girma kuma uwa uba; samun aljanna firdausi. Don haka ana son mutum ya dukufa da tsarkin zuciya da magiya ga ubangiji musamman a yammacin wannan rana domin neman bukatunsa na duniya da lahira da neman gafara ga kansa da iyayensa da iyalansa da kasarsa da al'ummar musulmi.
16. Akwai matukar hatsari ga yin sabon Allah a ranar Arafa saboda girmanta da darajarta a wurin Allah.
17. Alhazai a wannan rana suna cikin gafarar Allah, kuma Allah yana shaida ma Mala'iku haka.
18. Wanda bai samu tsayin Arafa ba, ya tsaya a kan iyakokin Allah. Wanda ba zai samu yanka dabba a gobe ba, ya yanka son zuciyarsa.
19. Rana ta 10 ita ce ranar Idi babba, kuma ranar layya. Ta fi duk sauran ranaku muhimmanci kuma babu abinda Allah ke so a ranar kamar kwararar da jinin dabbobi ana kiran sunansa.
20. Ranaku 3 bayan Sallah su ne Ayyamut Tashriq. Ana son musulmi ya darajta su, ya ci abinci, ya ziyarci yan uwa, ya caba ado, ya yi sadaka da sashen naman da ya yanka.

*_Allah ya yi mana muwafaqa da samun gafara, ya saukar mana da aminci da zaman lafiya da yalwantar arziki a kasarmu, ya daukaka addinin Musulunci da Musulmi._*

24/05/2026

*KARATUNMU NA EXTRA LESSON*
*Ranar Lahadi– 7th Z.Hajj, 1447 | 24th May, 2026*

Wannan karatu na musamman an shirya shi ne *kyauta FISABILILLAH* tare da ɗaukar nauyi daga:

*ALMUTASADDIQUN CHARITY FOUNDATION*

Ana gabatar da karatun ne a *ranakun Asabar da Lahadi* *Da kuma lokacin hutu* don tallafa wa dalibai da ilimi mai amfani.

*ALLAH ya saka da alheri* ga dukkan waɗanda ke bada gudummawa don cigaban wannan cibiya mai albarka.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Almutasaddiqun Charity Foundation posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share