Global Community For Human Rights Network

Global Community For Human Rights Network we're all Equal Before the Law. The law is the same for everyone, it must treat us all fairly

SAKUN TAYA MURNA AUREAn daura auren matashin ɗan jarida daga Radio Dala FMƘungiyar Global Community for Human Rights Net...
20/04/2026

SAKUN TAYA MURNA AURE

An daura auren matashin ɗan jarida daga Radio Dala FM

Ƙungiyar Global Community for Human Rights Network Nigeria

na taya ɗaya daga cikin fitattun ‘yan jarida a fannin labarai na gidan Radio Dala FM dake jihar Kano State, Hassan Mamuda Ya’u, murnar angwancewarsa da aka gudanar cikin farin ciki da walwala.

Ƙungiyar ta bayyana farin cikinta bisa wannan muhimmin mataki da ya ɗauka a rayuwarsa, tare da fatan Allah Ya sanya alkhairi da albarka a cikin wannan aure.

Haka kuma, ana addu’ar Allah Ya ba su zaman lafiya, soyayya mai ɗorewa, fahimtar juna, da zuri’a nagari shi da amaryarsa.
Allah Ya sanya alkhairi, Ameen.

16/04/2026

Tuna baya 2026

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA TA YABAWA KOTUN SHARI’AR MUSULUNCI TA KADUNA KAN HUKUNCI MAI ADALCIƘun...
15/04/2026

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA

TA YABAWA KOTUN SHARI’AR MUSULUNCI TA KADUNA KAN

HUKUNCI MAI ADALCI

Ƙungiyar Global Community for Human Rights Network Nigeria

tana miƙa cikakkiyar yabo da jin daɗinta ga Kotun Shari’ar Musulunci ta Jihar Kaduna

bisa hukuncin da ta yanke na rusa wata takardar aure da aka tabbatar da cewa ta bogi ce kuma mara inganci.

Wannan hukunci ya nuna ƙwazon kotun wajen tabbatar da gaskiya da adalci ba tare da tsoro ko son zuciya ba.

Hakan ya ƙara tabbatar da cewa har yanzu akwai alkalai masu tsayawa tsayin daka wajen kare mutuncin shari’a da kuma martabar al’umma.

Rahotanni sun bayyana cewa kotun ta yi hukunci a kan batun da ya shafi:

Dr. Ahmad Abubakar Gumi

Mal. Abdullahi Abubakar Goron Namaye

Mal. Umar Sambo (Shahada)

inda aka zarge su da hannu wajen ƙirƙirar takardar aure ta bogi tare da amfani da ita domin tsoma baki a cikin auren Nasir Musa Idris (Albani Agege) da matarsa ƴar Morocco, duk da cewa ba su da wata alaƙa da auren.
A hukuncinta, kotun ta tabbatar da cewa:

Takardar auren ta bogi ce kuma ba sahihiya ba
An ƙirƙire ta ne ba bisa ƙa’ida ba
An haramta amfani da ita gaba ɗaya
An umarci duk mai riƙe da ita da ya miƙa ta nan take

Bugu da ƙari, kotun ta dakatar da duk wata mu’amala da matar da ta shafi wannan rikici, tare da gargadin cewa duk wanda ya saɓa zai fuskanci hukunci mai tsauri.

Tunda fari kungiyar mu tana bin shari'ar tun daga tushe har zuwa yanzu

Ƙungiyarmu tana ganin wannan hukunci a matsayin babbar nasara ga adalci da kuma darasi ga duk wanda ke ƙoƙarin karkatar da gaskiya ko amfani da hanyoyin da ba su dace ba wajen cimma wata manufa.

Haka kuma, muna ƙarfafa wa hukumomin shari’a gwiwa da su ci gaba da bin diddigin gaskiya da tabbatar da cewa an hukunta duk wanda aka samu da laifi ba tare da nuna bambanci ba.

A ƙarshe, muna kira ga al’umma da su mutunta tsarin shari’a tare da guje wa duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya da mutuncin aure.

27/03/2026

ABUN KUNYA NE, ABUN BAN HAUSHI! GA JARIMI ALI NUHU

Abin takaici ne ganin wasu mutane har yanzu ba su fahimci illar kashe ɗan ta’adda ba—ba wai don tausayi ba, sai don hikima da tsaro na ƙasa.

Ina magana ne kai tsaye ga Ali Nuhu da duk wanda yake da irin wannan ra’ayi.

Eh, gaskiya ne—Human Rights ba ta goyon bayan kashe ɗan ta’adda ba.

Amma tambaya ita ce: shin kun fahimci DALILI?

Kashe ɗan ta’adda k**ar kashe maciji ne ba tare da sare kansa ba. Ka kashe guda ɗaya, amma tushen matsalar yana nan daram!
Tambaya ga masu hankali:

Shin waɗannan ‘yan ta’adda suna aiki ne su kaɗai?

Ko akwai MANYAN MUTANE a bayan su‘yan siyasa, masu kuɗi, masu iko—waɗanda ke cin gajiyar wannan ta’addanci?
Idan aka kashe ɗan ta’adda, wa zai tona asirin waɗanda ke ɗaukar nauyinsa?
Ku tuna tarihi: lokacin da aka k**a shugaban Boko Haram, ya fara tona wasu asirai masu girma… amma me ya faru? An kashe shi kafin ya gama magana.

Shin wannan ya kawo ƙarshen Boko Haram ne? Amsar ita ce A’A!
Saboda matsalar ba a sama take ba—a ƙasa take, a ofisoshi take, a hannun masu iko take!
A Nigeria akwai nau’ikan ‘yan ta’adda guda biyu:

Na daji – masu bindiga, masu garkuwa da mutane, masu kashe rayuka.

Na ofis – masu kujeru, masu bada umarni,

masu cin ribar jini da hawaye.

Wadannan na ofis su ne tushen matsala!

Shi ya sa idan aka k**a ɗan ta’adda, sai ka ga an sake shi.

Me yasa?
Saboda ubannin gidansa suna zaune a ofis suna bada umarni!
Amma ina matsalar take?

Mu ne matsalar! Ni da kai!

Ba ma bin diddigi, ba ma tambaya, ba ma neman gaskiya.

Sai mu yi shiru, mu zama bayi cikin ƙasarmu.

Saboda haka: Ina kira ga Ali Nuhu da ya sake duba wannan magana nasa, ya janye ta, domin irin wannan bayani na iya rikitar da jama’a da raunana fahimtar yaki da ta’addanci.

Yaki da ta’addanci ba kashe mutum kawai bane—yaki ne da tsari, da masu daukar nauyi, da masu cin moriya!

🌙✨ SAKON TAYA MURNAR SALLAH ✨GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK (GCHN)Na taya daukacin al’ummar Musulmi murnar Ba...
20/03/2026

🌙✨ SAKON TAYA MURNAR SALLAH ✨

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK (GCHN)

Na taya daukacin al’ummar Musulmi murnar Babbar Sallah.
Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana zunubanmu,
Ya maida mana ita cikin ƙoshin lafiya, zaman lafiya da wadata.

Muna kira ga al’umma da su kasance masu haƙuri, tausayi, da haɗin kai,

tare da mutunta haƙƙin ɗan Adam a kowane lokaci.

🤲 Allah Ya kawo mana ƙarshen matsalolin tsaro,

Ya ba mu zaman lafiya mai ɗorewa a Najeriya da duniya baki ɗaya.

🌍 Global Community for Human Rights Network (GCHN)

“Muryar Kare Haƙƙin Dan Adam”

SANARWAR MAI MAHIMMANCI KUTU TABADA DAMA GA ƳAN NIGERIA DASU YI BIDIYO LOKACIN DA JAMI AN TSARO SUKE KAN AIKIGlobal Comm...
18/03/2026

SANARWAR MAI MAHIMMANCI

KUTU TABADA DAMA GA ƳAN NIGERIA DASU YI BIDIYO LOKACIN DA JAMI AN TSARO SUKE KAN AIKI

Global Community for Human Rights Network Nigeria
Domin wayar da kan al’umma da kuma rage cin zarafi da jami’an tsaro ke yi wa jama’a, muna sanar da ku wani muhimmin hukunci da Babbar Kotun Tarayya da ke Warri, Jihar Delta ta yanke:

⚖️ MUHIMMIN HUKUNCI:

Mai shari’a H. A.

Nganjiwa ya tabbatar da cewa:

🔹 Duk ɗan Najeriya yana da cikakken haƙƙin ɗaukar hoto ko bidiyon jami’an ‘yan sanda yayin da suke bakin aiki a bainar jama’a.

🔹 Wannan haƙƙi yana ƙarƙashin ‘yancin faɗin albarkacin baki da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada.
🚫 ABUBUWAN DA S**A HARAMTA:

Kotun ta bayyana cewa:

❌ Haramun ne jami’in ɗan sanda ya tsoratar da wanda ke ɗaukar bidiyo

❌ Haramun ne k**a mutum saboda ɗaukar bidiyo

❌ Haramun ne ƙwace waya ko lalata kayan mutum

📌 UMARNI GA JAMI’AN TSARO:

✔️ Su riƙa sanya cikakken kayan aiki na hukuma

✔️ Su bayyana sunayensu da lambobin aikinsu a fili yayin aiki
💰 DIYAR DA KOTU TA UMARTA:

➡️ An bai wa Maxwell Uwaifo naira miliyan 5 a matsayin diyya

➡️ Ƙarin naira miliyan 2 kuɗin shari’a

📝 DALILIN SHARI’AR:
Shari’ar ta samo asali ne daga korafe-korafen cin zarafi, tsayar da mutane ba bisa ƙa’ida ba, da kuma zargin karɓar kuɗin dole daga wasu jami’an ‘yan sanda.

📢 SAKO DAGA ƘUNGIYAR MU:

A matsayinta na ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam, Global Community for Human Rights Network Nigeria na kira ga:

✔️ Jama’a su san haƙƙoƙinsu kuma su tsaya kai da fata

✔️ Jami’an tsaro su bi doka da mutunta haƙƙin jama’a

✔️ A daina duk wani nau’in cin zarafi ko zalunci

Wannan hukunci wata babbar nasara ce ga:

✔️ Gaskiya da adalci

✔️ Kare haƙƙin ɗan Adam

✔️ Rage cin zarafi a cikin al’umma

📌 MUHIMMI:

A riƙa amfani da wannan haƙƙi cikin natsuwa da mutunci, ba tare da hana jami’an tsaro gudanar da aikinsu ba.

Global community for human rights network Ungogo branch,Hujjojin Doka Kan Kare Haƙƙin Wanda Aka K**a a Najeriya.1. Hana ...
14/03/2026

Global community for human rights network Ungogo branch,

Hujjojin Doka Kan Kare Haƙƙin Wanda Aka K**a a Najeriya.

1. Hana Azabtarwa ko Dukar Mutum (Prohibition of Torture)
A karkashin Section 34(1)(a) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria, an tabbatar da cewa kowane mutum yana da haƙƙin mutunci da daraja, kuma:
“No person shall be subjected to torture or to inhuman or degrading treatment.”
Haka kuma Section 2 da Section 8 na Anti-Torture Act sun haramta duk wani nau’i na:
azabtarwa
duka
wulakanci
ko tilasta mutum ya amsa laifi.
Duk jami’in tsaro da ya aikata haka yana iya fuskantar hukunci a kotu.

2. Hana Cin Zarafi ko Wulakanta Mutum
A karkashin Section 34(1) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria, doka ta tabbatar da Right to Dignity of Human Person.
Wannan yana nufin:
ba a yarda jami’in tsaro ya zagi mutum ba
ko ya wulakanta shi yayin bincike ko tsarewa.

3. Haramcin Tilasta Mutum Ya Amsa Laifi
Section 35(2) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria ya ba wanda ake zargi damar:
yin shiru
neman lauya kafin bada bayani.
Wannan yana nufin ba a yarda jami’an tsaro su:
tilasta mutum ya amsa laifi
ko su tilasta masa bada shaida a kansa.

4. Haramcin Tilasta Sa Hannu a Bayani
A karkashin Section 29(2) na Evidence Act:
Duk wani confessional statement da aka samu ta hanyar tsoro, barazana, ko azabtarwa ba zai karɓu a kotu ba.
Saboda haka:
idan an tilasta mutum ya sa hannu
ko aka azabtar da shi kafin ya bada bayani
to wannan bayanin ba zai zama hujja a kotu ba.

5. Haramcin Tsare Mutum Ba Tare da Kai Shi Kotu ba
Section 35(4) da 35(5) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria sun bayyana cewa:
Mutumin da aka k**a dole ne a kai shi gaban kotu cikin:
awa 24 idan kotu tana kusa
ko awa 48 idan kotu tana nesa.
Idan ba a yi haka ba, tsarewar tana zama illegal detention.

6. Haramcin K**a Mutum Saboda Laifin Wani
Section 36(5) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria ya kafa ka’idar:
“Every person who is charged with a criminal offence shall be presumed to be innocent until he is proved guilty.”
Saboda haka:
ba a k**a mutum saboda laifin ɗan uwansa ko abokinsa ba
sai idan akwai hujjar cewa shi ma yana da hannu a laifin.

7. Haramcin Kwace Dukiyar Mutum Ba Tare da Doka ba
Section 44(1) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria ya tabbatar da Right to Property.
Wannan yana nufin:
ba a kwace waya, kudi, ko wata dukiya ba
sai da izinin doka ko kotu.

8. Haramcin Karɓar Rashawa (Bribery)
A karkashin Section 98 na Criminal Code Act:
duk wani jami’in gwamnati da ya karɓi:
kudi
kyauta
ko wata fa’ida
domin yin wani aiki ba bisa doka ba, yana aikata laifin rashawa (bribery).

9. Barazana da Makami Domin Tilasta Bayani
Section 2 na Anti-Torture Act ya bayyana cewa:
barazana, tsoratarwa, ko amfani da makami domin tilasta mutum ya bada bayani ana ɗaukarsa torture.

10. Haƙƙin Ganin Lauya da Sadarwa da Iyali
A karkashin:
Section 35(2) na Constitution of the Federal Republic of Nigeria
Section 6(2) na Administration of Criminal Justice Act
mutumin da aka k**a yana da haƙƙin:
ganin lauya
sadarwa da iyalansa ko abokansa.

C,O Ungogo Branch Sabi'u Auwal gama.

URGENT ANNOUNCEMENT(PRESS RELEASE)GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORKStrongly condemns, in the harshest terms, the...
02/03/2026

URGENT

ANNOUNCEMENT
(PRESS RELEASE)

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK

Strongly condemns, in the harshest terms, the brutal assassination of the Religious Leader of the Islamic Republic of Iran, Ayatollah Ali Khamenei.

This horrific incident is a great tragedy for humanity and a threat to global peace and security. The killing of leaders through violence will not bring solutions;

it will only fuel conflict, bloodshed, and instability around the world.

Our organization calls on all countries involved in the conflict to cease violence and embrace dialogue, reconciliation, and peaceful means in order to protect civilian lives and human dignity.

We also call on the United Nations and international organizations

to urgently take appropriate measures to prevent the escalation of the conflict and ensure justice.

The right to life and human dignity must remain the foundation of every political and security policy.

May God bring lasting peace to the world.

Amb karibu yahaya lawan kabara cheaf executive office and national director general

✍️ Global Community for Human Rights Network

SANARWA TA GAGAWA (PRESS RELEASE) GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORKTana Allah wadai da kakkausar murya kan kisan...
02/03/2026

SANARWA TA GAGAWA

(PRESS RELEASE)

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK

Tana Allah wadai da kakkausar murya kan kisan gillar da aka yi wa Jagoran Addinin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Ayatollah Ali Khamenei.

Wannan mummunan lamari babban abin takaici ne ga bil’adama, kuma barazana ce ga zaman lafiya da tsaron duniya baki ɗaya. Kashe shugabanni ta hanyar tashin hankali ba zai haifar da mafita ba, sai dai ƙara rura wutar rikici, jini da rashin zaman lafiya a duniya.

Kungiyarmu na kira ga dukkan ƙasashen da suke cikin rikici da su dakatar da tashin hankali, su rungumi tattaunawa, sulhu da hanyoyin zaman lafiya domin kare rayukan fararen hula da martabar ɗan Adam.

Muna kuma kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ƙungiyoyin duniya da su gaggauta ɗaukar matakan da s**a dace domin hana faɗaɗa rikici da tabbatar da adalci.

Hakkin rayuwa da mutuncin ɗan Adam dole ne su kasance ginshiƙin duk wata manufa ta siyasa ko tsaro.

Allah Ya kawo zaman lafiya mai ɗorewa a duniya.

✍️ Global Community for Human Rights Network

SANARWAR MANEMA LABARAI GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA Muna yin Allah wadai da kakkausar murya kan ci...
24/02/2026

SANARWAR MANEMA LABARAI

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA

Muna yin Allah wadai da kakkausar murya kan cin zarafin da aka yi wa ɗan jarida Abdulbaki Ali Ahmed Sharifai da ake zargin wani jami’in gwamnatin Jihar Kano, Auwal Sani Rogo (SSR), ya aikata a yayin wani taro na gasar kamun kifi ta Argungu.

Wannan abu ba wai cin mutuncin mutum ɗaya ba ne kawai — hari ne kai tsaye ga ’yancin aikin jarida, ’yancin faɗin albarkacin baki, da dimokuraɗiyya baki ɗaya.

Abin takaici, lamarin ya faru a gaban manyan jami’an gwamnati,

amma har yanzu babu wata hukunci ko neman afuwa daga wanda ake zargi ko gwamnatin Jihar Kano.

Wannan shiru yana nuna rashin mutunta dokoki da kuma ƙoƙarin danne ’yan jarida.

Muna ba gwamnatin Jihar Kano wa’adin

sa’o’i 24 kacal ta:

Daukar matakin ladabtarwa kan wanda ake zargi

Bayar da hakuri a hukumance ga ɗan jaridar

Tabbatar da kariya ga ’yan jarida a jihar
Idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba,

za mu garzaya kotu domin neman cikakken hakkinsa tare da ɗaukar dukkan matakan doka da s**a dace.

Muna kira ga

kwamashina Yansanda jahar Kano da Yak**a ya gudanarda bincike sannan a gabatar da shi a gaban kutu
munada majiya mai ƙarfi kan an shigar da kurafi gaban kwamashina Yansanda jahar Kano amma yaki zuwa gaiyata da aka yi masa saboda karan tsaye akan doka

Wannan ba shi ne karo na farko ba.

Kwanan nan ma an samu cin zarafin ɗan jarida Aminu Halilu Tudunwada. Wannan yana nuna cewa cin zarafin ’yan jarida a Jihar Kano yana ƙara k**ari, abin da ba za mu lamunta ba.

Muna kira ga:

Kungiyoyin kare hakkin dan Adam

Kungiyoyin ’yan jarida

Lauyoyi da masu rajin dimokuraɗiyya

Al’umma baki ɗaya

da su tashi tsaye domin kare martabar aikin jarida kafin a mayar da shi abin tsoro.

’Yancin Jarida ba laifi ba ne — ginshiƙi ne na adalci da gaskiya.

✍️ Duk wanda ya ci zarafin ɗan jarida, ya ci zarafin al’umma ne baki ɗaya.

🚨 READ, SHARE, AND DEMAND JUSTICE!GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIAstrongly condemns the refusal to comp...
23/02/2026

🚨 READ, SHARE, AND DEMAND JUSTICE!

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA

strongly condemns the refusal to comply with a court order by the Department of State Services (DSS),

which has failed to return Walida to her parents

following allegations that a DSS officer abducted her.

❗ This incident is not just a violation of one person’s rights,

it is a threat to the freedom of every citizen.

⚖️ If court orders are not respected, what law will protect the common people?

If a child is separated from her parents, who will accept such injustice?

Silence is not the solution — justice must prevail!

We urgently call on all relevant stakeholders to:

Immediately comply with the court order
Return Walida to her parents without delay
Punish anyone found involved in this matter
Justice delayed is justice denied!

Please share this message so the world will know.

We also commend the prominent journalist,

Abubakar Haruna Galadanci,

for his tireless efforts in seeking justice over the abuse committed against Walida and her parents. This is true journalism in action.



GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA

🚨 KU KARANTA KU YADA KU NEMI ADALCI! GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA tana Allah wadai da kakkausar mur...
23/02/2026

🚨 KU KARANTA KU YADA KU NEMI ADALCI!

GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA

tana Allah wadai da kakkausar murya kan kin bin umarnin kotu da Hukumar Department of State Services (DSS)

tayi na kin maida Walida ga iyayenta

tun bayan zargin yin garkuwa da ita da wani jami’in DSS yayi.

❗ Wannan lamari ba wai take hakkin mutum daya bane kawai

barazana ce ga ‘yancin kowane dan kasa.

⚖️ Idan ba a mutunta kotu ba, wace doka za ta kare talaka?

Idan aka raba ‘ya da iyayenta, wa zai ji dadin wannan zalunci?

Shiru ba mafita bane adalci dole ne!

Muna kira cikin gaggawa ga duk masu ruwa da tsaki:

A gaggauta bin umarnin kotu

A mayar da Walida ga iyayenta ba tare da bata lokaci ba.

A hukunta duk wanda aka samu da hannu a wannan lamari

jinkiri, adalci hanawa ne!

Ka/ki yada wannan sako domin duniya ta sani

Muna yabawa fitaccan dan jarida
Abubakar haruna galadanci

bisa aiki tukuru dan neman anyi adalci a wanna cinzarafin da akayiwa Walida da iyayanta wanna shine aiki jarida



GLOBAL COMMUNITY FOR HUMAN RIGHTS NETWORK NIGERIA

Address

Kano
700001

Telephone

+2348138296105

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Global Community For Human Rights Network posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share