28/02/2026
Isra’ila da Amurka sun kai hari ga Jamhuriyar Musulunci, suna nufin zuciyar gwamnatin ƙasar…
Isra’ila tare da haɗin gwiwar Amurka ta kai hare-hare a Iran a ranar Asabar din nan, inda aka kai farmaki wurare da dama yayin da aka ruwaito fashe-fashe a Tehran da wasu birane.
Daya daga cikin muhimman wuraren da aka kai hari shi ne ofishin jagoran addini na Iran, Ali Khomeini, da ke tsakiyar Tehran. Kamfanin dillancin labarai na Reuters, ya ce Khamenei bai kasance a wurin ba yayin harin, duk da cewa ba a tabbatar da hakan kai tsaye ba.
Bidiyoyin da ke yawo a yanar gizo sun nuna hayaki mai duhu yana tashi daga yankin da ake dangantawa da hedkwatar jagoran addinin wurin da ake ɗauka a matsayin cibiyar ikon gudanarwa na gwamnatin Iran.
Bayan hare-haren, rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewa an harba makamai daga Iran zuwa yankin Isra’ila, lamarin da ya sa aka kunna kararrawar gargadi a arewacin Isra’ila yayin da ake kallon harin a matsayin alamar farko ta martanin Tehran.
Wani jami’in Iran ya shaida cewa martanin ƙasar zai kasance “mai ƙarfi,” abin da ya tayar da fargabar cewa rikicin na iya fadada zuwa yaƙin yankin gaba ɗaya.
Hukumomi a Iran sun fara takaita sadarwa yayin da hare-haren ke gudana.
Kungiyar lura da yanar gizo ta NetBlocks ta ruwaito cewa karfin intanet ya ragu zuwa kusan kaso 54 cikin ɗari na yadda aka saba, yayin da kafafen yada labarai na Iran s**a ce an samu katsewar hanyoyin sadarwar waya da manhajojin aika saƙo. Haka kuma, wasu shafukan labarai na Iran an ruwaito cewa an yi musu kutse a yayin ayyukan yaƙin yanar gizo.
Wannan tashin hankali ya zo ne makonni kaɗan bayan jami’an tsaro sun gudanar da mummunan kame-kame a fadin ƙasar inda aka kashe dubban Iraniyawa, abin da aka bayyana a matsayin ɗaya daga cikin mafi muni a tarihin kasar.
Hare-haren yanzu suna gudana a cikin yanayin fushi na cikin gida da matsin lamba mai tsanani kan gwamnatin da ke mulki.
Yarima Reza Pahlavi ya kira Iraniyawa da su shirya komawa kan tituna, yana bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta kusa rushewa, tare da roƙon jama’a da su kwantar da hankalinsu su jira ƙarin umarni.