Akafsan Channel

Akafsan Channel AKAFSAN - Promoting Peace, Unity and Academic Excellence✊✊✊ AKAFSAN - Promoting Peace, Unity and Academic Execellence...

AKAFSAN is an organization of intellectuals whose activities, engagements and responsibilities are mainly dedicated toward Promotion of Peace, Unity and Academic Excellence. As such, members of the association are required to be the good ambassadors, and do the needful actions for realization of the AKAFSAN vision.

Muna Addu'a da nagiya ga Allah, tareda neman taimakonSa SWT. Ubangiji yasa ace gamma da akayi. Allah ya kawo mana ƙarshe...
25/04/2026

Muna Addu'a da nagiya ga Allah, tareda neman taimakonSa SWT. Ubangiji yasa ace gamma da akayi. Allah ya kawo mana ƙarshen wannan al'amari, Allah yasa lokaci ne da Sheikh Abduljabbar zai samu adalci da nasara a wannan case nasa albarkar Annabi Alaihis-Salam.

CIKAKKEN RAHOTON SHARI’A | Zaman Kotun Ɗaukaka Ƙara kan Shari’ar Sheikh AbduljabbarRANA: 23 Afrilu, 2026WURI: Kotun Ɗauk...
23/04/2026

CIKAKKEN RAHOTON SHARI’A | Zaman Kotun Ɗaukaka Ƙara kan Shari’ar Sheikh Abduljabbar

RANA: 23 Afrilu, 2026
WURI: Kotun Ɗaukaka Ƙara (Court of Appeal), Kano

TAƘAITACCEN BAYANI (Executive Summary)

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta gudanar da zama domin sauraron ƙorafin da Sheikh Abduljabbar Sheikh Nasiru Kabara ya shigar. Bayan nazari kan ƙa’idojin shari’a da tsarin doka, kotu ta mayar da hankali kan ingancin ɗaukaka ƙarar da kuma bin matakan doka kafin sauraron muhimman hujjoji. A ƙarshe, kotu ta sallami ƙarar tare da bada umarnin a mayar da shari’ar zuwa kotun ƙasa domin ci gaba da sauraron shari’ar bisa doka da oda.

CIKAKKEN RAHOTO NA ZAMAN KOTU

1. Bayyanar ɓangarori a gaban kotu:
Kotun ta fara da tambayar mai ɗaukaka ƙara ko yana da lauya. Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara (Appellant) ya bayyana cewa yana kare kansa ba tare da wakilcin lauya ba.
A ɓangaren gwamnati kuwa, Barrister Bashir ya bayyana kansa a matsayin lauya mai kare martanin Gwamnatin Jihar Kano (Respondent), tare da gabatar da abokin aikinsa.

2. Matsayin kotu da huruminta:
Mai shari’a (Presiding Justice) ya jaddada cewa wannan babbar kotu ce mai hurumin sauraron ɗaukaka ƙara daga kotunan ƙasa, kuma aikin kotun shi ne duba hukuncin da aka yanke a ƙananan kotuna bisa tsarin doka.

3. Batun gabatar da ƙara da takardu (Record of Appeal):
Kotun ta tunatar da mai ɗaukaka ƙara cewa duk wani ƙorafi dole ne ya kasance cikin tsarin da doka ta tanada, wato ta hanyar takardun ɗaukaka ƙara (Record of Appeal).
Kotu ta bayyana cewa:

a) Takardun ƙara su ne tushen shari’a a wannan mataki.
b) Ba a sauraron bayanai kai tsaye, sai an bi tsarin da doka ta tanada.

4. Ka’idojin doka kan gabatar da ƙara:
Kotun ta yi nuni da tanadin doka (Order 19 na dokokin kotun ɗaukaka ƙara), wanda ya baiwa mai ƙara ko lauyansa damar shigar da bayanai cikin ƙayyadadden lokaci, sannan a ba shi gajeren lokaci (ƙasa da mintuna 15) domin gabatar da muhimman hujjoji.

5. Shiri na mai ɗaukaka ƙara:
Mai ɗaukaka ƙara ya tabbatar da cewa yana shirye ya gabatar da kansa ba tare da lauya ba.

6. S**an farko (Preliminary Objection):
Lauyan gwamnati ya bayyana cewa sun riga sun shigar da s**a (objection) kan ingancin ɗaukaka ƙarar, suna jayayya cewa ƙarar ba ta cika sharuddan doka ba.
Kotun ta tambayi mai ɗaukaka ƙara ko an ba shi takardar wannan s**a, inda ya amsa cewa an kai masa amma bai karɓa ba saboda wanda ya kawo takardar lauya ne ba jami’in kotu ba.

7. Tabbatar da bayar da takarda (Service of Process):
Registrar na kotu ya tabbatar da wanda ya kai takardar, kuma kotu ta gamsu cewa an isar da takardar yadda ya kamata bisa doka.
Daga bisani, mai ɗaukaka ƙara ya amince cewa ya karɓi takardar a gaban kotu, wanda aka rubuta a cikin kundin kotu (record).

8. Muhimmancin fara duba s**a (Objection):
Kotun ta bayyana cewa a tsarin shari’a, idan akwai s**a kan ingancin ƙara, dole ne a fara tantance wannan kafin shiga cikin muhimman batutuwan shari’a.

9. Lokacin mayar da martani:
Kotun ta bayyanawa mai ɗaukaka ƙara cewa a tsarin doka yana da kwanaki uku ne domin mayar da martani kan s**ar da aka yi masa. Sai dai ya bayyana cewa bai da wata amsa (sai abinda kotu ta yi).

10. Bayanin haƙƙin lauya
Kotun ta jaddada cewa:

- Doka ta baiwa mai ƙara damar zaɓar lauya.

- Idan bai da lauya, gwamnati na da ikon samar masa da lauya domin tabbatar da adalci.

11. Tsarin doka da shari’ar Musulunci:
Kotun ta bayyana cewa wannan shari’a na da nasaba da shari’ar Musulunci, kuma dole ne a bi doka da tsarin shari’a wajen gabatar da dukkan takardu da hujjoji.

12. Matsalar ingancin ɗaukaka ƙara -
Kotun ta lura da cewa:

a) Har yanzu shari’ar tana gaban kotun ƙasa (High Court).

b) Ba a kammala matakan da s**a dace ba kafin ɗaukaka ƙara.

c) Takardun da aka shigar ba su bi ka’idojin doka ba.

HUKUNCIN KOTU (FINAL DETERMINATION):

Bisa la’akari da hujjoji da tsarin doka:

i) Kotun ta sallami ɗaukaka ƙarar saboda rashin cika sharuddan doka.

ii) Ta bayar da umarnin sakamako (consequential order) cewa:

a) A mayar da shari’ar zuwa ofishin Alƙalin Alƙalai na Jihar Kano.

b) A ci gaba da sauraron shari’ar a kotun ƙasa (High Court) ba tare da jinkiri ba.

Daga ƙarshe, kotun ta jaddada cewa wannan mataki yana da nufin tabbatar da adalci ga dukkan ɓangarori cikin gaggawa tareda bin doka da oda.

~ DAN JARIDA DAGA KOTU (Akafsan Channel)

AN DAWO DA SHEIKH ABDULJABBAR KANO BISA UMARNIN KOTU - Laraba, 22 ga Afrilu, 2026.A ƙoƙarin ci gaba da sauraron shari’ar...
22/04/2026

AN DAWO DA SHEIKH ABDULJABBAR KANO BISA UMARNIN KOTU - Laraba, 22 ga Afrilu, 2026.

A ƙoƙarin ci gaba da sauraron shari’ar babban Malamin Addinin Musuluncin nan (Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara), yau Laraba 22/04/2026 an dawo da shehin Malamin Jihar Kano, bayan umarnin Kotun Ɗaukaka Ƙara (Court of Appeal) mai zamanta a Sakatariyar Audu Bako, a Kano ta bayar.

Matakin ya biyo bayan tsarin shari’a da ke gudana tsakanin malamin addinin da Gwamnatin Jihar Kano, inda kotun ta amince da ci gaba da shari’ar bayan wani lokaci na duba ƙorafe-ƙorafe da aka gabatar a gabanta.

Masu lura da al’amura sun bayyana cewa dawowar shari’ar na nuna wani muhimmin mataki a cikin wannan lamari, wanda ya jawo hankalin jama’a a jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.

Ana sa ran zaman kotu na gaba zai ƙara fayyace muhimman batutuwan shari’a tare da tsara matakan da za a bi a gaba.

A dakace mu zuwa gobe, muna tafe da rahoton zaman shari'ar Inshaa Allahu ta'ala.

21/04/2026

SHAWARA:
Masu neman ayi adalci a Shari’ar Malam Abduljabbar, a maida hankali wurin yin addu'o'i da neman taimakon Allah.

20/04/2026

Saƙon Murya - Rahoton Zaman Kotu (Shari’ar Sheikh Abduljabbar) na ranar Litinin 20/04/2026.

RAHOTON ZAMAN KOTU - SHARI’AR SHEIKH ABDULJABBARRANA: 20 ga Afrilu, 2026WURI: Court of Appeal, Kano Division, Audu Bako ...
20/04/2026

RAHOTON ZAMAN KOTU - SHARI’AR SHEIKH ABDULJABBAR

RANA: 20 ga Afrilu, 2026
WURI: Court of Appeal, Kano Division, Audu Bako Secretariat

TAƘAITACCEN BAYANI:

A ranar Litinin, 20 ga Afrilu, 2026, kotu ta ci gaba da sauraron shari’ar Sheikh Abduljabbar Kabara kamar yadda aka tsara. Zaman ya ƙunshi muhimman matakai na shari’a, umarni daga kotu, da kuma bayyana damuwar kotu kan yadda ɓangaren Gwamnatin Jihar Kano (ofishin Kwamishinan Shari’ah) suke jan ƙafa wajen tafiyar da wannan shari’a.

MUHIMMAN ABUBUWAN DA S**A FARU:

1. Fara Zaman Kotu da Gabatar da Takarda
Da aka kira shari’ar: Usman Malam Hussaini ya miƙe a madadin kwamitin Shari’ar Sheikh Abduljabbar, wanda ya ƙunshi mutane 14, inda ya gabatar da wata takarda wacce Sheikh Abduljabbar Kabara ne ya rubuta domin a miƙa wa kotu.

Mai Jagorantar Shari’a (Presiding Justice) ya tambayi halin da mai appeal (Appellant) yake ciki da kuma inda yake. Hussaini ya bayyana masa cewa yana tsare a Gidan Gyaran Hali na Kuje kuma yana cikin ƙoshin lafiya.

2. Karɓar Takardar da Kotu Ta Yi:
Kotu ta amince da karɓar takardar domin nazari, tana mai nuna cewa saƙon na da muhimmanci ga shari’ar.

3. Kiran Shugaban Sashen Shari’a (HOD Litigation):
Ɗaya daga cikin alkalai (Presiding Justice) ya bayar da umarnin a kira Ibrahim, shugaban sashen shari’a (HOD Litigation) .

Bayan zuwansa, ya tabbatar wa kotu cewa an karɓi takardar Malam Abduljabbar kuma an yi mata rajista (filing). Sai dai ya kuma tabbatar da cewa ba a kawo wanda ake ƙara kotu ba.

4. Umarnin Kotu ga Ma’aikatar Shari’a:
Bisa wannan yanayi, kotu ta bayar da umarni a kira Darakta daga Ofishin Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano domin ba da bayani.

5. Bayanin Abin da Takardar Ta Ƙunsa:
Kotu ta nemi a yi taƙaitaccen bayani kan abin da takardar ta ƙunsa. Hussaini ya miƙa wannan aikin ga Jilani Makwarari, wanda ya yi bayani a takaice cikin harshen Hausa.

6. Nazarin Takardar da Alƙalai S**a Yi:
Alƙalai sun ɗauki kusan mintuna biyar suna nazarin kwafin takardar da ke hannunsu. Bayan haka, sun umarci Hussaini da ya koma ya zauna, suna mai nuna cewa sun wadatu da kwafin da suke da shi.

7. Ɗan Dakatar da Shari’ar (Case Down):
Mai Jagorantar Shari’a ya bayyana cewa an “sauke” shari’ar na ɗan lokaci (the case is down), wato za a dakatar da ita na ɗan lokaci kafin a sake kiranta.

8. Sake Kiran Shari’ar:
Bayan kimanin awa biyu, kotu ta sake kiran shari’ar a matsayin ta takwas cikin jerin shari’o’in ranar.

Zahraddeen Kofar Mata daga Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano ya miƙe, inda ya nemi afuwar kotu bisa jinkirin zuwansu. Ya kuma sanar da kotu cewa an miƙa shari’ar ga wani lauya mai zaman kansa (Private Lawyer).

9. Gargadin Kotu:
Mai Jagorantar Shari’a ya nuna rashin jin daɗi matuƙa kan yadda ake tafiyar da shari’ar, yana mai jaddada cewa wannan ba shari’a ce ta yau da kullum ba, don haka bai kamata a yi sakaci da ita ba.

10. Ƙin Amincewa da Buƙatar Ɗagawa:
Lokacin da aka tambaye shi abin da zai ce, wakilin Ma’aikatar Shari’a ya nemi a ɗaga shari’ar na tsawon mako guda. Nan take kotu ta ƙi wannan buƙata, tana mai nuna cewa an riga an samu jinkiri mai yawa.

HUKUNCI DA UMARNIN KOTU:

Bayan cikakken nazari, Mai Jagorantar Shari’a ya yanke hukunci kamar haka:

a) An ɗage shari’ar zuwa ranar Alhamis, 23 ga Afrilu, 2026.

b) Kotu ta umarci Lauyan Gwamnati ya halarci zama na gaba ba tare da ƙin halarta ba.

c) Kotu ta bayar da umarni ga Hukumar Gidan Ajiya da Gyaran Hali (Correctional Center) da su tabbatar an kawo Appellant, wato Sheikh Abduljabbar Kabara gaban wannan kotu a zama na gaba.

d) Kotu ta bayyana cewa Appellant shi ne zai gabatar Shari’arsa da kansa, kasancewar ba shi da lauya.

KAMMALAWA:

Zaman kotu na wannan rana ya nuna tsayin daka daga bangaren kotu wajen tabbatar da bin doka da tsari, da kuma kauce wa ƙarin jinkiri. Umarnin da aka bayar sun nuna ƙudurin kotu na ganin an tafiyar da shari’ar cikin gaskiya, da kuma tabbatar da halartar mai ƙara - Sheikh Abduljabbar (Appellant) domin ci gaba da shari’ar ba tare da tsaiko ba.

Wanda Ya Rubuta Rahoton:
Ɗan Jarida na Shari’a
20 ga Afrilu, 2026

14/04/2026
SABON RAHOTO: KAN SHARI’AR SHEIKH ABDULJABBAR KABARA Sheikh Abduljabbar Ya Miƙa Sabuwar Buƙata Zuwa Kotun Daukaka Kara a...
07/04/2026

SABON RAHOTO: KAN SHARI’AR SHEIKH ABDULJABBAR KABARA

Sheikh Abduljabbar Ya Miƙa Sabuwar Buƙata Zuwa Kotun Daukaka Kara a Kano...

Fitaccen malamin addinin Musulunci a birnin Kano, Sheikh Abduljabbar Sheikh Nasir Kabara, wanda ke tsare a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja, ya sake gabatar da wata sabuwar takardar ƙorafi a gaban Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Kano.

Rahotanni sun nuna cewa malamin ya ɗauki wannan mataki ne bayan wani sako da ya bayyana cewa ya samu ta wayar tarho daga Shugaban Sashin Shari’a (H.O.D Litigation) na kotun a ranar 31 ga watan Maris, 2026, wanda ya kunshi sanarwar cewa za a aiko masa da takardar sanarwar ranar zaman kotu.

CIKAKKEN BAYANAI KAN TAKARDAR ƘORAFIN:

A cikin takardar ƙorafin mai shafuka biyar, wadda aka gabatar wa kotun a ranar Talata, 7 ga Afrilu, 2026, ta hannun wakilan kwamitin shaidunsa, malamin ya nuna damuwa kan yadda ake tafiyar da shari’arsa.

Daga cikin muhimman batutuwan da ya gabatar sun hada da:

1. Sauya Masa Wurin Tsarewa: Malamin Ya koka kan yadda aka sauya masa wurin tsarewa daga gidan gyaran hali na Kurmawa da ke Kano zuwa Kuje a Abuja tun ranar 14 ga Oktoba, 2025, ba tare da ba shi damar ɗaukar muhimman takardunsa na shari’a ba.

2. Batun Takardun Shari’a: Sheikh Abduljabbar Ya bayyana cewa tsawon watanni biyar bai samu cikakken bayani kan halin da takardunsa suke ciki ba, tare da zargin cewa ba a ba shi damar tantance su ba kafin sauya masa Matsuguni.

3. Ƴancin Kare Kai: Malamin ya jingina buƙatarsa da tanadin Sashe na 36 (6) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima), yana mai neman a ba shi damar kare kansa da kansa a gaban kotu.

MANYAN BUƘATUN DA AKA GABATAR:

A cikin korafin, Sheikh Abduljabbar Sheikh Nasir Kabara ya roƙi kotun da ta yi la’akari da waɗannan buƙatu kafin a ci gaba da sauraron karar:

1. A mayar da shi zuwa gidan gyaran hali na Kurmawa da ke Kano domin ya duba halin da takardunsa suke ciki.

2. A ba shi damar sake tsara ko mayar da duk wasu takardu idan aka samu sun bace ko an sauya su.

3. A dakata da ci gaba da shari’a har sai ya tabbatar da sahihancin takardunsa, tare da karɓar cikakkiyar sanarwar ranar zaman kotu da kuma takardar izini na halarta domin gabatar da hujjojinsa.

KAMMALAWA:

Malamin ya jaddada cewa tun bayan tsare shi da akayi a ranar 16 ga Yuli, 2021, bai aikata wani laifi ba, inda ya roƙi kotu da ta yi masa adalci wajen duba bukatunsa.

Zuwo lokacin kammala wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga kotun dangane da wannan sabon korafi.

SOURCE:
https://www.facebook.com/share/p/1CYVL5H6xQ/

02/04/2026
31/03/2026

Ɗaliban Sheikh Abduljabbar Kabara sun ziyarce shi, ya basu saƙo kamar yadda za a ji👂

Address

Gwale
Kano
700103

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Akafsan Channel posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Akafsan Channel:

Share