25/08/2026
*RANAR HAUSA TA DUNIYA 2026*
Ina taya daukacin al’ummar Hausawa a Najeriya, Afirka da duniya murnar Ranar Hausa ta Duniya, wadda za a gudanar a ranar 26 ga Agusta 2026 a fadar Mai Martaba Sarkin Hausawan Najeriya, Amb. Alh. Sani Adamu Geza Garkuwan Hausawan Duniya, a Kano.
Wannan rana tana da matukar muhimmanci, domin ba biki kawai ake yi ba; rana ce ta nuna muhimmancin harshen Hausa, tarihinsa, al’adunsa da kuma irin gudunmawar da Hausawa suke bayarwa wajen ci gaban Najeriya da Afirka.
Ina kira ga daukacin Hausawa, shugabannin al’umma, sarakuna, malamai, matasa da mata da su dauki wannan rana da muhimmanci, su halarci taron, domin kasancewa tare a irin wannan gagarumin taro na kara dankon zumunci da hadin kanmu.
Ina kuma kira ga kafafen yada labarai da su ci gaba da tallata muhimmancin harshen Hausa da al’adunmu, domin abin da ba mu kare ba, tarihi zai iya karbe shi.
A matsayina na Shugaban Majalisar Masarauta ta AREWARMU DUNIYARMU African Chiefdom and Council, ina goyon bayan duk wani shiri da zai hada kan Hausawa, ya kare al’adunmu, ya inganta harshen Hausa, tare da samar da kyakkyawar makoma ga matasanmu.
Ina taya Mai Martaba Sarkin Hausawan Najeriya murna da godiya bisa wannan babban shiri. Allah Ya sanya taron ya zama sanadin hadin kai, zaman lafiya da ci gaban Hausawa a Najeriya da duniya baki daya.
*Amb. Alh. Ibrahim Haruna*
Shugaban Majalisar Masarauta
AREWARMU DUNIYARMU African Chiefdom and Council