18/09/2023
JAHILCIN DA ZAKZAKIY YAKE YADAWA:
1. Jahilci da hayaniyar da Malam Zakzakiy yake yadawa a Duniya a gaban magoya bayansa da sunan bayar da darasi abin takaici ne matuka.
2. Dazun nan ne na yi karo da wani video na shi Zakzakiy yana bayar da darasi a gaban magoya bayansa inda ya soki lafazin “A’ameen” ya ce wai asalinsa maguzanci ne na kafuran Masar! Kuma duk wanda ya furta lafazin bayan karatun Fatiha toh sallarsa ta baci! Ya kuma ce: hatta a littattafan Sunnah ma babu inda aka ce Annabi ne ya ce a rika cewa: “A’ameen” a karshen Fatiha! Haka dai Zakzakiy ya fada babu kunya babu tsoron Allah; duk kuwa da cewa littattafan Sunnah sun ce Annabi ya fadi hakan. Haka nan ruwayah ta inganta a littattafan Shi’ah cewa ana iya fadar hakan!!
3. Na farko dai hadithai da yawan gaske ne cikin littattafan Ahlus Sunnah s**a inganta daga Annabi mai tsira da aminci wadanda a cikinsu Shi Annabi yake umurtan Musulmi da su ce: “A’ameen” bayan fatiha, ga ma daya daga cikinsu a masayin misali: Muslim ya ruwaito hadithi na 404, da Abu Dawud na 972, da Nasa’iy na 655, da Ibnu Khuzaimah na 1,584, da Daramiy na 1,351 daga Sahabi Abu Musal Ash-ary ya ce: خطبنا رسول الله صلى الله عليه وسلم فبين لنا سنتنا وعلمنا صلاتنا فقال: اذا صليتم فاقيموا صفوفكم ثم ليومكم احدكم فاذا كبر فكبروا واذا قال غير المغضوب عليهم ولا الضالين فقولوا ءامين)).
4. Na biyu: ba dukkan Shi’ah Ithna Ishriyyah ba ne s**a hana yin “A’ameen” bayan kare karatun Fatiha a cikin salla, a’a, akwai wadanda suke yin “A’ameen” bayan Fatiha saboda ingantacciyar ruwayah daga littattafan hadithi na Shi’ah, ga ma ruwayar: Tuusiy ya ruwaito cikin Tahzeebul Ahkam 2: 75/277, ya kuma ruwaito cikin Alis Tibsar 1: 318/1,187, haka nan Muhammadul A’amily ya ruwaito cikin Wsaa’ilush Shi’ah 6/68, dukkansu biyun sun ruwaito kamar haka: ((عن جميل قال: سألت أبا عبد الله عليه السلام عن قول الناس في الصلاة جماعة حين يقرأ فاتحة الكتاب: ءامين. فقال: ما أحسنها! واخفض الصوت بها)).
Babban malamin Shi’ah Abul Qasim Al-Qummiy ya ce cikin littafinsa: Ganaa’imul Ayyam 2/507: ((ونقل عن ابن الجنيد الجواز عقيب الحمد وغيرها، وقواه بعض المتوخرين لصحيحة جميل، قال: سالت ابا عبد الله عن قول الناس جماعة حين يقرا فاتحة الكتاب " ءامين قال ما احسنها واخفض الصوت)).
Haka nan babban malamin Shi’ah Al-Muhaqqiqul Bahraaniy ya ce a cikin littafinsa Al-Hadaa’iqun Naadhirah 8/196 kamar haka: ((ونقل عن ابن الجنيد انه يجوز التأمين عقيب الحمد وغيرها)).
5. Allah muke rokon Ya tsare mu daga sharrin jahilci. Ameen.
Daga Dr Ibrahim jalo jalingo