Tijjaniyya grassroots mobilization and Empowerment initiative zamfara state

  • Home
  • Nigeria
  • Gusau
  • Tijjaniyya grassroots mobilization and Empowerment initiative zamfara state

Tijjaniyya grassroots mobilization and Empowerment initiative zamfara state 105

Fassarar Diwanin Maulanmu sheikh Ibrahim Nyass R T A Ina Yan uwa masoya manzon Allah masoya Maulanmu sheikh Ibrahim Nyas...
16/03/2024

Fassarar Diwanin Maulanmu sheikh Ibrahim Nyass R T A

Ina Yan uwa masoya manzon Allah masoya Maulanmu sheikh Ibrahim Nyass masoya Maulana Sheikh Abdullahi Abubakar Yabo muna farin cikin Sanar daku cewa mun Dora muku fassarar Diwanin Maulanmu sheikh Ibrahim Nyass Wanda Maulanmu sheikh Abdullahi yabo yake Gabatarwa a YouTube channel namu Mai suna Aisha A. Yabo TV karkashin jagorancin yayarmu Aisha Abdullahi Yabo

Muna Rokon Allah Allah ya karawa shehi Lafiya, Allah yabamu Albarkar su Alfarmar sayyidina Rasulullah S A W

✍️
Abdullahi Adam
Jama'a

Ranar ta zagayo ta Kuma ta zagayo Ranar Khatmar Diwani 2024Amadadin shugaba Sheikh Abdullahi yabo Tare da sauran dukkan ...
15/12/2023

Ranar ta zagayo ta Kuma ta zagayo Ranar Khatmar Diwani 2024

Amadadin shugaba Sheikh Abdullahi yabo Tare da sauran dukkan mukarrabansa da Kuma kungiyar Iksiru sa'adati suna farin cikin sanar da ya uwa masoya cewa Ranar Ta zagayo, Ranar da ake Khatmar Diwani Tare da Kaddamar da khidima ga Iyalan shehunnanmu Dake Zawiyyar Sheikh balarabe Zawiyya Gusau.

A ranar ne fuskoki mabanbanta suke Haduwa da s**a jima Basu Haduba bayan kammala a karatu Zawiyyar Sheikh balarabe taron zai Gudana ne a karkashin jagorancin shugaba Sheikh Abdullahi yabo Wanda za'ayi kamar Haka::

Rana:: 05/01/2024
Lokaci:: 8:30pm
Wuri::: a Harabar Gidan maulana sheikh Abdullahi yabo (Daiba)

✍️
Abdullahi Adam
Jama'a

Shawara zuwa ga mahukunta akan sha'anin wa'azi a wannan Kasar tamu ta Nigeria 🇳🇬1. Kafa majalisar Fatawa ta kasa wacce t...
13/12/2023

Shawara zuwa ga mahukunta akan sha'anin wa'azi a wannan Kasar tamu ta Nigeria 🇳🇬

1. Kafa majalisar Fatawa ta kasa wacce take ita kadai ce keda Hakkin warware wata mas'ala da ta taso ta Addinin musulunci a Nigeria, wacce za'ayi ta a matakin kasa da Kuma jaha da Kuma karamar hukuma, dole ne a Sanya malamai Dattijai daga kowanne Bangare Tijjaniyya/Kadiriyya/Izala/Shi'a.

2. Wannan majalisar dole ne Tafitar da tsarin tantance kowanne Limami kafin a bashi damar yin huduba ta Juma'a Tare da Bashi Tsari a hukumance yanda Zaiyi hudubar a kowanne sati, sannan Dole ne a tantance Dukkan Littafan da ake tafsir dasu a hukumance a wannan Kasar tare da malaman dake karantar da Tafsir.

3. Dole ne ayi Gyaran yanda ake tarukan Addinin musulunci a Nigeria wato Taron Maulud da wa'azi da waliyayye da Kuma muzahara a wannan Kasar domin a tsaftace kowanne irin taro tsafta irin na shari'ar musulunci, tare da Tilasta tsaftace Halshen duk Mai magana a wajan Taron.

4. Hukunta duk Wanda kalamansa s**a tayar da Hargitsi a tsakanin musulmi yazama Tilas a wannan Kasar, tare da Haramta karantar da duk wani Littafin da zai kawo rabuwar Kai tare da raba kan musulmi, sannan A kirkiri hukumar da zata kula da masu karantarwa Online tare da Hukunta duk Wanda baije yayi Register ba Koh ya karya dokar Hukumar.

Muna Rokon Allah yakara hada kan dukkan Musulmi yakarya kafirci da kafirai Alfarmar sayyidina Rasulullah S A W
✍️
Abdullahi Adam
Jama'a

*Sanin Hakkin Dake kan khaleefan Tijjaniyya shi ya kamata mufara sani kafin mufara kofafi (3)!!!*Koh Ina mafita ?1.Ajiye...
12/12/2023

*Sanin Hakkin Dake kan khaleefan Tijjaniyya shi ya kamata mufara sani kafin mufara kofafi (3)!!!*

Koh Ina mafita ?

1.Ajiye Banbancin Halara: dole ne dukkan Tijjanawa su karbi dukkan Cigaba, a hannun kowaye yazo, ko da kuwa ba shehin ku Daya ba, Kuma Koda Mahaifinsa muridi ne a Zawiyyar ku, Lura da Girman abun da yazo dashi yafi a kalli Girmansa.

2. Dole ne kowacce a Zawiyya tasan adadin malamanta da Kuma Muridanta, sannan dole ne tasan duka adadin Rassu da take dasu a fadin Duniya tare da daliban Dake karatu a cikinsu Hakan zai taimaka Mana wajan Gane yawanmu tare da samun sauki wajan Tallafawa marasa Karfi dake cikin kowacce Zawiyya, dole ne Sai ansan da mutum sannan za'asan Yana cikin Bukata Koh baida ita.

3. Dole ne a fitar da kungiyar Dalibai Yan Tijjaniyya a Nigeria Mai magana Daya wacce zata kasance karkashin kulawar majalisar shura, hakan zai kawar da cin zarafin dakewa Dalibai a manyan Makarantun Nigeria, Kuma hakan zai sa asamu Tsari Mai kyau wajan Rabawa Tijjanawa tallafin karatu na kasashen waje, hakan Kuma zai iya sawa a duk shekara a bawa wannan kungiya Gurbin tura wasu Dalibai a makarantun Nigeria.

4. Dole ne a kafa kungiyar Lauyoyi, jami'an Tsaro, Likitoci, malaman manyan Makarantu, Yan jarida dukkansu mabiya Darikar Tijjaniyya, domin kuwa wannan zaisa idan angina Asibiti mallakin Tijjaniyya kamar yanda muke fata, to sune zasuyi Aiki a ciki, idan aka Gina jami'a Koh Gidan Jarida s**a Yan Tijjaniyya ne zasuyi Aiki, Lauyoyi kuwa kowa yasan amfanin su ga irin cin Kashin Dakewa Yan Tijjanawa a Nigeria.

Wadannan sune kadan daga cikin shawarwarin da Nike bawa Yan uwana Tijjanawa muyi, matukar mukayi wannan Tsari ba'a taimakemu ba, Sai mu fito muyi korafi domin kuwa anyi Tsari Kuma ammallaki dukkan takardun da ya kamata Amma khaleefa Yaki taimakawa!!!

Allah yasa mudace, Allah yabamu ikon Halacci ka rabamu da Butulci

✍️
Abdullahi Adam
Jama'a

*Sanin Hakkin Dake kan khaleefan Tijjaniyya shi ya kamata mufara sani kafin mufara kofafi(2)!!!*Koh me yakawo Tsaiko kan...
11/12/2023

*Sanin Hakkin Dake kan khaleefan Tijjaniyya shi ya kamata mufara sani kafin mufara kofafi(2)!!!*

Koh me yakawo Tsaiko kan Haka?

A farkon Nada khaleefa Muhammad sunusi na biyu Ya kafa majalisar shura ta malamai daga kowanne bangare a cikin Nigeria, inda ka dauko wasu daga cikin khaleefofi da shehunnai Dake Zawiyyoyi Tare da umartarsu da kafa irin wannan majalisar a kowacce jaha, domin samun kyakyawan Tsari a Zawiyyoyin da muke dasu A Nigeria.

Wannan committee na Shura shine keda al-Hakin tattara bayanai tare da dukkan Taimakon da kowacce Zawiyya take dashi tare da bin dukkan hanyoyin da za'abi domin magance kowacce irin matsala a Zawiyya Koh a Tijjaniyya Baki Daya, khaleefa yayi wannan Tsari ne domin kau saukin Jin korafe-korafen zawuyoyi, Tare da Nunawa khaleefofi da shehunnai ta yanda zasu iya magance matsalolin su da kansu.

Daya daga cikin malaman shura sheikh Ahmad Attijani sani Auwal ya kirkiri kungiyar da zata sauwakewa shura wannan Aiki domin Tattance dukkan muridan Nigeria tare da makarantunsu da Kuma baya Nan su a Website na Tijjaniyya domin baza'a taba samun cigaba ba Sai da kyakyawan Tsari, Ina Daya daga cikin wadanda s**a halarci Taron karawa juna sani da akayi a Kano na wannan website tare da kaddamar dashi domin Fara Aiki.

Me zawuyoyi s**a jefemu dashi?

A Lokacin wasu sun fahimci kudurinmu, wasu kuwa cewa sukeyi Mu Yan damfara ne, zamuyi Amfani dasu domin karbar kudi a hannun Yan siyasa kamar yanda Izala takeyi, domin tsarin duka Daya ne, muna so mu siyasan tar da Tijjaniyya, mun sauka daga karantarwar shehu ibrahim Nyass, da yawa wasu Zawiyiyoyi Basu bamu bayanan muridanta, daga cikin manyan khaleefofi suna Ganin za'a kwace musu karfin iko akan muridansu, akwai matsaloli da dama.

Al-ummar da Bata San adadin yawan makaratunta,da mabiyanta, da malamanta, da shirya yanda zata taimaki marasa karfi, itace take Tunanin za'a samo Mata tallafi?

Kafin kuga Lafin kowa kuga Laifin kanku!!!

Koh Ina mafita? Mu Hadu a Rubutu Na Na gaba
✍️
Abdullahi Adam

07/12/2023

TIJJANIYYA GRASSROOTS

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un A jiya lahadi 3/12/2023 jirgin sama ya jefowa 'yan uwa BOM a filin mauludi da yake g...
04/12/2023

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un

A jiya lahadi 3/12/2023 jirgin sama ya jefowa 'yan uwa BOM a filin mauludi da yake gudana a garin TUDUN/BIRI dake yankin airport Kaduna a cikin dare wanda hakan yayi sanadiyyar rasa rayuka sama da mutum 50 muna rokon Allah ya gafarta masu ya hadasu da wanda su ka taru domin sa Sallallahu Ta'ala AlaiHi Wa Sallam ya kuma karbi shahadarsu.

إنا لله وإنا إليه راجعون 😭😭😭 انتقل اليوم 06/11/2023م أحد شيوخنا الكرام، الشيخ الدكتور يوسف علي الكنوي، أمير علماء غيا، خ...
06/11/2023

إنا لله وإنا إليه راجعون 😭😭😭
انتقل اليوم 06/11/2023م أحد شيوخنا الكرام، الشيخ الدكتور يوسف علي الكنوي، أمير علماء غيا، خطر ببالي مرثية في حقه فقلتها كالآتي:

رحمان يا حنان يا متعالي
فارحم أبي أستاذ يوسف عالي

إني جبلت بحبه وحديثه
منذ الصبا تفسيره في بالي

إذ أستفيد بعلمه، أسلوبه
راق يبث بحكمة ولآالي

بلطافة وفصاحة وتعمق
متأنيا لا لا تراه عجالي

متفننا بين العلوم قديمها
وحديثها بكليهما متجال

هو في الولاية نال كرسيا له
في عالمي جن وإنس عال

قد عاش في طبيب ومات بطيبه
فإلى جوار رسولنا المتعالي

إني أعز كل فرد مسلم
في عالم الإسلام والإفضال

وكذا التجانيين او في الفيضة
وتعم تعزيتي جميع عيال

وأخص بنت الشيخ وارثة له
في. قوله في عمله والحال

بلقيس يوسف عال بنت بارة
فالتحسبي لله نعم الوالي

يا رب ألحق شيخنا يوسف بهم
الأوليا عند الرسول الغالي

وتصل ربي ثم سلم دائما
نحو النبي وصحبه والآل

حق قدره ومقداره العظيم

نسأل الله أن يتغمده بواسع رحمته وعفوه، ويغفر له ويلحقه بالنبيين والصديقين والشهداء والصالحين وحسن أولئك رفيقا بجاه النبي صلى الله عليه وسلم
محمد الحافظ لول الزرمي

Address

Zawiyya Gusau
Gusau

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tijjaniyya grassroots mobilization and Empowerment initiative zamfara state posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Tijjaniyya grassroots mobilization and Empowerment initiative zamfara state:

Share