Kasar DUTSE gadawur

Kasar DUTSE gadawur Wannan shafin an kirkireshine domin isar da sakonni da kulla zumunci tsakanin Al’ummun Duniya.

Cikin kwanciyan Hankali da Kaunan Al’umma kayi Mulkinka, ALLAH Sabunta Maka Rahma Lamidon Gabas Na Yamma da Borno.
08/02/2026

Cikin kwanciyan Hankali da Kaunan Al’umma kayi Mulkinka, ALLAH Sabunta Maka Rahma Lamidon Gabas Na Yamma da Borno.

31/01/2026
31/01/2026

Marigayi Sarkin Dutse Nuhu Yau 31 January ya cika Shekara uku da Rasuwa, Allah Sabunta Maka Rahma Sarkin Zumunci, YAnda Karaya Gidajen Al’umma Allah ya Raya Naka yakuma Kyautata Makwancinka.

21/01/2026
21/01/2026

DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE

A yau Laraba MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. (Dr.) MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI, CFR ya karɓi baƙuncin;

1. Sabon Kwamishin ‘Yan Sandan Jihar Jigawa CP. Dahiru Muhammed da Jama’arsa, da

2. Kwamandan Rundunar Hisbah na Jihar Jigawa Dr. Muhammad Fa’iz Bashir da Jama’arsa,

3. ⁠Ɗaliban Sashen Ilimi da suke koyan Tarihi wato (History) dake Jami’ar Ado Bayero dake Kano bisa jagorancin Shugaban Sashen Dr. Halliru Surajo.

Dalilin wannan Ziyara tasu kuwa shi ne domin gabatar da kawunansu ga Uban Ƙasa kana da neman tabarraki da Addu’ah ta fatan alheri bisa wannan jogoranci nasu.

Mai Martaba Sarki ya fara da yi musu maraba sannan ya musu godiya bisa wannan ziyara da s**a kawo wannan Fada mai tarin Albarka. Ya ƙara da godewa Mai Girma Gwamna bisa kafa wannan runduna ta Hisbah domin ƙara tsaftace Jihar mu mai tarin albarka, wadda muke da kyakkyawan zato za kuyi aiki bisa amana da gaskiya.

Hakazalika, Mai Martaba ya ja hankalinsu sosai duba da irin ƙalubalen dake gabansu dangane da aikin Allah da s**a ƙudiri niyyar yi, ya ce kada ku yarda ayi amfani daku domin zaluntar al’umma.

A ƙarshe Mai Martaba Sarki ya musu fatan alheri da sanya musu albarka a wannan gagarumin ayyuka nasu a faɗin Jihar Jigawa.

Sun sami tarba daga wajen ‘yan Majalissar sa daga cikinsu akwai Mai Girma Galadima, Waziri, Madaki, Sarkin Bai, Marafa, Sarkin Fada, Jakadan Sulhu, Magatakarda, Barwa da sauransu.

Allah ya taumaki Sarki, Allah ya ja Zamanin Sarki, Allah ya Jiƙan Baba Sarki ya ƙarawa Mai Babban Ɗaki Lafiya.

📸/✍️:
Copied from: Nasir Ibrahim, sNITP
Wazirin Tafarkin Dutse
Fadar Mai Martaba Sarki
Laraba, 21st January, 2025.

21/01/2026

DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE

A yau Laraba MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. (Dr.) MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI, CFR ya karɓi baƙuncin;

1. Sabon Kwamishin ‘Yan Sandan Jihar Jigawa CP. Dahiru Muhammed da Jama’arsa, da

2. Kwamandan Rundunar Hisbah na Jihar Jigawa Dr. Muhammad Fa’iz Bashir da Jama’arsa,

3. ⁠Ɗaliban Sashen Ilimi da suke koyan Tarihi wato (History) dake Jami’ar Ado Bayero dake Kano bisa jagorancin Shugaban Sashen Dr. Halliru Surajo.

Dalilin wannan Ziyara tasu kuwa shi ne domin gabatar da kawunansu ga Uban Ƙasa kana da neman tabarraki da Addu’ah ta fatan alheri bisa wannan jogoranci nasu.

Mai Martaba Sarki ya fara da yi musu maraba sannan ya musu godiya bisa wannan ziyara da s**a kawo wannan Fada mai tarin Albarka. Ya ƙara da godewa Mai Girma Gwamna bisa kafa wannan runduna ta Hisbah domin ƙara tsaftace Jihar mu mai tarin albarka, wadda muke da kyakkyawan zato za kuyi aiki bisa amana da gaskiya.

Hakazalika, Mai Martaba ya ja hankalinsu sosai duba da irin ƙalubalen dake gabansu dangane da aikin Allah da s**a ƙudiri niyyar yi, ya ce kada ku yarda ayi amfani daku domin zaluntar al’umma.

A ƙarshe Mai Martaba Sarki ya musu fatan alheri da sanya musu albarka a wannan gagarumin ayyuka nasu a faɗin Jihar Jigawa.

Sun sami tarba daga wajen ‘yan Majalissar sa daga cikinsu akwai Mai Girma Galadima, Waziri, Madaki, Sarkin Bai, Marafa, Sarkin Fada, Jakadan Sulhu, Magatakarda, Barwa da sauransu.

Allah ya taumaki Sarki, Allah ya ja Zamanin Sarki, Allah ya Jiƙan Baba Sarki ya ƙarawa Mai Babban Ɗaki Lafiya.

📸/✍️:
Copied from: Nasir Ibrahim, sNITP
Wazirin Tafarkin Dutse
Fadar Mai Martaba Sarki
Laraba, 21st January, 2025.

18/01/2026
Ziyarar mai martaba sarkin Dutse Alh Dr Hamim Nuhu Sanisi. cfr domin duba aiki  gidan Mal Sanusi Bello Basiru  Assistant...
18/01/2026

Ziyarar mai martaba sarkin Dutse Alh Dr Hamim Nuhu Sanisi. cfr domin duba aiki gidan Mal Sanusi Bello Basiru Assistant secretary special duties Na Mai Martaba Sarkin Dutse.

DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE JUMA’AH 🕋 🕌, 04th OCTOBER, 2024_ 02nd RAB.II., 1446-AH.Assalamun Alaikum……His Royal ...
04/10/2024

DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE
JUMA’AH 🕋 🕌, 04th OCTOBER, 2024_ 02nd RAB.II., 1446-AH.
Assalamun Alaikum……

His Royal Highness EMIR OF DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI CFR, has Commissioned the New Juma’at Mosque 🕋 🕌 at JAHUN, Jigawa State which and it was built by ALH. HAMISU RILWAN JAHUN under the Alham Educational Foundation Mosque, with the present of the Jigawa State Governor Mal. Umar Namadi FCA, Katsina State Governor Mal. Umar Dikko Radda, and Jigawa State Speaker Rt. Hon. Haruna Aliyu Ɗangyatun, which the prayer leads by the Islamic Scholar Sheikh Bin Usman.

***********************************************************

MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI CFR, yayin da ya halarci buɗe Masallacin Juma’ah a garin Jahun, dake Gundumar Jahun, Jihar Jigawa wadda Babban Malamin Addini ya Jagoranta Sheikh Bin Usman, wadda wani bawan Allah mai suna ALH. HAMISU RILWAN JAHUN ya gina a ƙarƙashin Gidauniyarsa mai suna (Alham Educational Foundation).

Cikim wanda s**a halarta akwai Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa Mal. Umar Namadi FCA, Gwamnan Jihar Katsina Mal. Umar Dikko Radda, da Kakakin Majalissar Jihar Jigawa Rt. Hon. Haruna Aliyu Ɗangyatun.

Bayan Kammala Sallah Juma’ah Shugaban Kwamatin Gudanarwa ba Masallacin Prof. Bala ya gabatar da jawabin Godiya a madadin Jama’ar gari da sauran al’umma baki ɗaya.

Cikin Jawabin Mai Martaba Sarki, ya fara da yabawa wanda s**a bayar da gudunmawar Gina wannan Masallaci k**a tun daga shawarwari har aka zo ga kammala ginin. Ya ƙara da janyo hankalin jama’ar wannan gari ta yadda zasu raya wannan katafaren Masallaci k**a daga kan karatuttuka na mata dana maza ta yadda za’a samu ilimi ga al’umma a wannan Makaranta ta cikin Masallacin.

A ƙarshe Mai Martaba Sarki ya bawa Gwamna da Jama’ar wannan gari tabbacin kawo Limamin da zai jagoranci wannan Masallacin bisa chanchanta k**ar yadda ake yi idan an samu sabon Masallaci ta hanyar yi masa Jarrabawa.

Mai Martaba Sarki ya samu rakiyar Masu Girma hakimansa daga cikinsu akwai Mai Girma Galadiman Dutse Alh. Basiru Muhammad Sanusi Babban Ɗan Majalissar Sarki, Ɗan Malam ɗin Dutse Alh. Aminu Ɗanmalam Hakimin Aujara, da kuma Sarkin Fadar Dutse Alh. Wada Alhaji Shugaban Ma'aikatan Fadar Mai Martaba Sarki, Magajin Rafin Dutse Alh. Balarabe Ahmed Hakimin Jahun, Kogunan Dutse Alh. Garba Muhammed Hakimin Miga, da dai sauransu.

Allah yaja zamanin Sarki, Allah ya ƙarawa sarki Lafiya, Allah ya sada mu da albarkacin Juma'ah, Amin 🤲🤲🤲.

📸/✍️:
WAZIRIN TAFARKIN DUTSE
Fadar Mai Martaba Sarki

DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALHAMIS, 19th SEPTEMBER, 2024 - 16th RAB.I., 1446-AH.Assalamun Alaikum……Ƙungiyar WOF...
19/09/2024

DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE
ALHAMIS, 19th SEPTEMBER, 2024 - 16th RAB.I., 1446-AH.
Assalamun Alaikum……

Ƙungiyar WOFAN bisa Jagorancin Hajiya Salamatu Garba da sauran jama’arsu s**a kawowa MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI CFR ziyarar a Fadarsa dake soron Gida.

Dalilin wannan ziyara tasu shi ne domin neman Tabarraki kana da sanya musu albarka a waje Mai Martaba Sarki. Sun kuma gabatarwa da Mai Martaba Sarki irin ayyukan alherin da s**a kawo a wannan Masarauta tamu mai albarka.

A ƙarshe, Shugabar tafiyar tasu ta roƙi Mai Martaba Sarki kan ya amince da ƙudirinsu wadda suke neman amincewarsa a matsayim GRANDPATRON na wanna ƙungiya tasu a Jihar Jigawa baki ɗaya.

Sun samu tarba a wajen ‘yan Majalissar Sarki daga cikin su akwai Mai Girma Galadiman Dutse, Sa’in Dutse, Ɗan Malam, Ɗan Masani, Barnawa, Jakadan Sulhu, da kuma Sarkin Fadar Dutse.

Allah yaja zamanin Sarki, Allah ya ƙarawa Sarki Lafiya da Nisan Kwana. Allah ya jiƙan Sarki.

📸/✍️:
WAZIRIN TAFARKIN DUTSE
CEO Waziri Studio
Fadar Mai Martaba Sarki

Address

Dutse

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kasar DUTSE gadawur posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Kasar DUTSE gadawur:

Share