04/10/2024
DAGA FADAR MAI MARTABA SARKIN DUTSE
JUMA’AH 🕋 🕌, 04th OCTOBER, 2024_ 02nd RAB.II., 1446-AH.
Assalamun Alaikum……
His Royal Highness EMIR OF DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI CFR, has Commissioned the New Juma’at Mosque 🕋 🕌 at JAHUN, Jigawa State which and it was built by ALH. HAMISU RILWAN JAHUN under the Alham Educational Foundation Mosque, with the present of the Jigawa State Governor Mal. Umar Namadi FCA, Katsina State Governor Mal. Umar Dikko Radda, and Jigawa State Speaker Rt. Hon. Haruna Aliyu Ɗangyatun, which the prayer leads by the Islamic Scholar Sheikh Bin Usman.
***********************************************************
MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI CFR, yayin da ya halarci buɗe Masallacin Juma’ah a garin Jahun, dake Gundumar Jahun, Jihar Jigawa wadda Babban Malamin Addini ya Jagoranta Sheikh Bin Usman, wadda wani bawan Allah mai suna ALH. HAMISU RILWAN JAHUN ya gina a ƙarƙashin Gidauniyarsa mai suna (Alham Educational Foundation).
Cikim wanda s**a halarta akwai Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa Mal. Umar Namadi FCA, Gwamnan Jihar Katsina Mal. Umar Dikko Radda, da Kakakin Majalissar Jihar Jigawa Rt. Hon. Haruna Aliyu Ɗangyatun.
Bayan Kammala Sallah Juma’ah Shugaban Kwamatin Gudanarwa ba Masallacin Prof. Bala ya gabatar da jawabin Godiya a madadin Jama’ar gari da sauran al’umma baki ɗaya.
Cikin Jawabin Mai Martaba Sarki, ya fara da yabawa wanda s**a bayar da gudunmawar Gina wannan Masallaci k**a tun daga shawarwari har aka zo ga kammala ginin. Ya ƙara da janyo hankalin jama’ar wannan gari ta yadda zasu raya wannan katafaren Masallaci k**a daga kan karatuttuka na mata dana maza ta yadda za’a samu ilimi ga al’umma a wannan Makaranta ta cikin Masallacin.
A ƙarshe Mai Martaba Sarki ya bawa Gwamna da Jama’ar wannan gari tabbacin kawo Limamin da zai jagoranci wannan Masallacin bisa chanchanta k**ar yadda ake yi idan an samu sabon Masallaci ta hanyar yi masa Jarrabawa.
Mai Martaba Sarki ya samu rakiyar Masu Girma hakimansa daga cikinsu akwai Mai Girma Galadiman Dutse Alh. Basiru Muhammad Sanusi Babban Ɗan Majalissar Sarki, Ɗan Malam ɗin Dutse Alh. Aminu Ɗanmalam Hakimin Aujara, da kuma Sarkin Fadar Dutse Alh. Wada Alhaji Shugaban Ma'aikatan Fadar Mai Martaba Sarki, Magajin Rafin Dutse Alh. Balarabe Ahmed Hakimin Jahun, Kogunan Dutse Alh. Garba Muhammed Hakimin Miga, da dai sauransu.
Allah yaja zamanin Sarki, Allah ya ƙarawa sarki Lafiya, Allah ya sada mu da albarkacin Juma'ah, Amin 🤲🤲🤲.
📸/✍️:
WAZIRIN TAFARKIN DUTSE
Fadar Mai Martaba Sarki