07/02/2026
Daga shafin Anas Naziru 👇👇
Hakika mai girma SD mutumin kirki ne, mai zuciya ɗaya, mai kawaici da tausayi, wanda yake ɗaukar muradin matasa da al’umma gaba ɗaya a matsayin nauyi na kansa. Jajircewarsa, gaskiyarsa da tsayuwarsa a kan gaskiya sun sanya ya zama ginshiƙi mai ƙarfi a tafiyar siyasar Maigirma Gwamna Malam Dikko Umar Raddah PhD da cigaban jihar nan.
A matsayina matashin garin malamai jibia ina Amfani da Kafafen Sadarwar Zamani (Social Media) na Kananan Hukumomin Jihar Katsina baki ɗaya, irin gudummuwar da yake ba mu wajen tafiyar da ayyukanmu, haɗa mu da hukumomin gwamnati, tare da ba mu dama mu taka rawar gani a harkokin mulki, kaɗai ya isa mu yaba masa.
Mai girma SD malamai jibia, ginshiƙi ne na matasa, jagora ne mai hangen nesa, Muna alfahari da irin namijin ƙoƙarin da yake yi wajen yada manufofin gwamnatin Mai Girma Gwamna Malam Dikko Umar Raddah PhD domin tabbatar da cigaba mai ɗorewa a Jihar Katsina.
Mai girma SD malamai. Komai lokaci ne, ka ci gaba da haƙuri da juriya, domin nasara tana nan tafe da yardar Allah.
Da wannan nake maka Barka da Juma’ah, ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi maka. jagoranci,
Ya ƙara maka
haƙuri,
juriya,
basira
da hikima.
wajen gudanar da ayyukanka. Allah Ya saka maka da alheri, Ya kare ka daga dukkan sharri, Ya kuma ɗaukaka ka a idon jama’ah.
Barka da jumaa mubarakk.
Mai girma SD garin malamai jibia.
♧♧♧Daga dan malamai jibia.♧♧♧