07/08/2026
Da alama Gwamnatin Jihar Kebbi ta yi wa mutanen Wasagu alkawuran ƙarya!
By Kebbi Update
Sama da wata biyu kenan da Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi ya yi wa al'ummar Wasagu alƙawura a Fadar Mai Martaba Sarkin Wasagu cewa gwamnati za ta ƙara yawan jami'an tsaro, za ta wadata su da ingantattun kayan aiki, za ta samar da motocin sulke na 'Kurkunu' (APC), sannan kuma za ta tabbatar an fara gina Sansanin Sojojin Najeriya na Forward Operating Base (FOB) a Wasagu ba tare da ɓata lokaci ba.
Amma har zuwa wannan lokaci, shiru ka ke ji kamar an shuka dusa. Babu wani gagarumin mataki da aka aiwatar, babu wani bayani da zai kwantar wa jama'a hankali.
Abin takaici kuwa shi ne, kusan kowace rana sai an samu rahoton kashe mutane ko kuma yin garkuwa da su, musamman manoma da ke neman halalinsu a gonaki. Hakan ya sa al'ummar Wasagu da ƙauyukan da ke kewaye da ita ci gaba da rayuwa cikin tsoro, fargaba da rashin tabbas.
Tambayar da mutanen Wasagu da dama ke yi a yau ita ce: Shin wannan shiru da Gwamnatin Jihar Kebbi ke yi a kan irin azabtar wa da barayin daji ke yi wa mutanen Wasagu da ƙauyukan da ke kewaye da ita na nufin cewa gwamnatin ta sadaukar da al'ummar Wasagu ga barayin daji?
Al'ummar Wasagu na jiran a cika alkawuran da aka yi musu, domin tsaro ba alfarma ba ne, haƙƙi ne na kowane ɗan ƙasa.