Labaran Najeriya

Labaran Najeriya Samar da ingantattun labaran Najeriya da dumi-duminsu.

Da alama Gwamnatin Jihar Kebbi ta yi wa mutanen Wasagu alkawuran ƙarya!By Kebbi Update Sama da wata biyu kenan da Mataim...
07/08/2026

Da alama Gwamnatin Jihar Kebbi ta yi wa mutanen Wasagu alkawuran ƙarya!

By Kebbi Update

Sama da wata biyu kenan da Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi ya yi wa al'ummar Wasagu alƙawura a Fadar Mai Martaba Sarkin Wasagu cewa gwamnati za ta ƙara yawan jami'an tsaro, za ta wadata su da ingantattun kayan aiki, za ta samar da motocin sulke na 'Kurkunu' (APC), sannan kuma za ta tabbatar an fara gina Sansanin Sojojin Najeriya na Forward Operating Base (FOB) a Wasagu ba tare da ɓata lokaci ba.

Amma har zuwa wannan lokaci, shiru ka ke ji kamar an shuka dusa. Babu wani gagarumin mataki da aka aiwatar, babu wani bayani da zai kwantar wa jama'a hankali.

Abin takaici kuwa shi ne, kusan kowace rana sai an samu rahoton kashe mutane ko kuma yin garkuwa da su, musamman manoma da ke neman halalinsu a gonaki. Hakan ya sa al'ummar Wasagu da ƙauyukan da ke kewaye da ita ci gaba da rayuwa cikin tsoro, fargaba da rashin tabbas.

Tambayar da mutanen Wasagu da dama ke yi a yau ita ce: Shin wannan shiru da Gwamnatin Jihar Kebbi ke yi a kan irin azabtar wa da barayin daji ke yi wa mutanen Wasagu da ƙauyukan da ke kewaye da ita na nufin cewa gwamnatin ta sadaukar da al'ummar Wasagu ga barayin daji?

Al'ummar Wasagu na jiran a cika alkawuran da aka yi musu, domin tsaro ba alfarma ba ne, haƙƙi ne na kowane ɗan ƙasa.

KEBBI STATE GOVERNMENT AND OUR ELECTED REPRESENTATIVES, HOW LONG WILL WASAGU BE LEFT TO BLEED?By Muhammad MusaExecutive ...
06/08/2026

KEBBI STATE GOVERNMENT AND OUR ELECTED REPRESENTATIVES, HOW LONG WILL WASAGU BE LEFT TO BLEED?

By Muhammad Musa

Executive Governor of Kebbi State, Commissioner for Internal Security, Our elected representatives at national and state houses of assembly, and Chairman Danko-Wasagu Local Government! This is a direct question, and the people of Wasagu deserve a direct answer: how long will you allow our people to be killed, kidnapped, and terrorised?

Hajara Ibrahim Dan'azumi Ta Lashe Gasar Haddar Al-Qur'ani Ta Duniya a JordanDaga Muhammad Musa Ɗaliba Hajara Ibrahim Dan...
03/08/2026

Hajara Ibrahim Dan'azumi Ta Lashe Gasar Haddar Al-Qur'ani Ta Duniya a Jordan

Daga Muhammad Musa

Ɗaliba Hajara Ibrahim Dan'azumi, mai shekara 19 daga Jihar Gombe, ta kafa tarihi bayan ta lashe matsayi na farko a Gasar Hashemite ta Mata ta Duniya karo na 18 ta Haddar Al-Qur'ani Mai Tsarki, wadda aka gudanar a ƙasar Jordan.

Hajara ta yi fice ne a rukunin haddar Al-Qur'ani gaba ɗaya (Hizbi 60) tare da Tajwidi, inda ta samu maki 99.5 cikin 100, lamarin da ya ba ta damar doke mahalarta gasar kusan 40 da s**a wakilci ƙasashe daban-daban na duniya.

A halin yanzu, Hajara ɗaliba ce mai karantar Botany (Mataki na Biyu – 200 Level) a Jami'ar Jihar Gombe (Gombe State University).

Nasarar da ta samu ta sake nuna irin ƙwarewa, jajircewa da himmar matasan Najeriya wajen neman ilimin Al-Qur'ani Mai Tsarki, tare da ɗaga martabar ƙasar a idon duniya.

Al'umma da dama sun taya Hajara murnar wannan babban abin alfahari, tare da yi mata addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara mata ilimi mai amfani, Ya tabbatar da ita a kan tafarkin Al-Qur'ani, Ya kuma sanya wannan nasara ta zama abin ƙarfafawa ga sauran matasa.

Allah Ya azurta 'ya'yanmu da baiwar haddar Al-Qur'ani Mai Tsarki, Ya sanya su cikin masu aiki da koyarwarsa, saboda darajar Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (SAW). Amin. 🤲

03/08/2026

Ko Yanzu alama ya nuna cewa Professor Isa Ali Pantami ne zai lashe zaben jihar Gombe.
Credit: Abdul Journalist 1

03/08/2026

"A Journey of 30 Minutes Now Takes Over One Hour" —Danko Youths Cry Out Over Decade-Long Neglect of Zuru–Danko–Gadar Zaima Road

By Muhammad Musa

The Danko Youth Progressive Association (DYPA) has appealed to the Kebbi State Government to urgently intervene in the reconstruction of the Zuru–Danko–Gadar Zaima Road, describing its deplorable condition as a major obstacle to transportation, farming and economic activities in the area.

The Association said the road, which serves as the only major federal highway linking Danko town with neighbouring communities and other parts of the state, has remained in a state of disrepair for more than a decade, causing untold hardship to motorists, traders and farmers.

Speaking on behalf of the Association, its President, Musa Maidamma, called on the Executive Governor of Kebbi State, Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), to come to the rescue of the people by facilitating the reconstruction of the road.

According to him, the poor condition of the highway has significantly increased travel time, explaining that a journey between Zuru and Gadar Zaima, which should ordinarily take less than 30 minutes, now takes more than one hour because of the numerous potholes and damaged sections of the road.

The Association noted that the situation has continued to affect the movement of agricultural produce, increase transportation costs and expose commuters to avoidable risks.

The youths urged both the Kebbi State and Federal Governments to treat the reconstruction of the road as a matter of urgent public importance, stressing that rehabilitating the highway would boost economic activities, ease transportation and improve the living conditions of thousands of residents who depend on it daily.

They expressed hope that the government would respond positively to their appeal and bring lasting relief to the people of Danko and surrounding communities.

"Mtswww!Ni kam na ɗauka wasu manyan gidaje ne na alfarma a birnin Abuja Malam ya mallaka, har kuke ta yi masa yaɗa batut...
03/08/2026

"Mtswww!

Ni kam na ɗauka wasu manyan gidaje ne na alfarma a birnin Abuja Malam ya mallaka, har kuke ta yi masa yaɗa batutuwan cin mutunci.

Ashe wai wannan duplex mai ɗakuna biyar (5-bedroom) ne kawai?

Wannan ai ba wani abin mamaki ba ne. Ko ɗansa, Abdulrahman, ma zai iya mallakar irin wannan gida.

Gaskiya, kun raina hankalin jama'a a banza."

Credit: Mailafia

29/07/2026

I got over 3,500 reactions on one of my posts last week! Thanks everyone for your support! 🎉

''Yan Bindiga Sun Kashe Yasir Wasagu Bayan Shafe Mako Uku a Hannunsu.Daga Muhammad Musa Rahotanni daga garin Wasagu da k...
29/07/2026

''Yan Bindiga Sun Kashe Yasir Wasagu Bayan Shafe Mako Uku a Hannunsu.

Daga Muhammad Musa

Rahotanni daga garin Wasagu da ke Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi sun tabbatar da mutuwar Yasir, wanda wasu 'yan bindiga s**a yi garkuwa da shi kimanin makonni uku da s**a gabata yayin da yake aiki a gonarsa da ke kusa da garin.

Majiyoyi sun ce Yasir ya shafe kusan makonni uku a hannun masu garkuwa da mutanen, inda iyalansa s**a ci gaba da rayuwa cikin fargaba da addu'ar ganin ya dawo gida lafiya. Sai dai cikin baƙin ciki, rahotanni sun nuna cewa maharan sun kashe shi.

Lamarin ya sake ƙara jefa al'ummar Wasagu cikin jimami da fargaba, yayin da hare-haren 'yan bindiga, kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ci gaba da addabar yankin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa matsalar tsaro ta ci gaba da ta'azzara duk da cewa gwamnatin jihar Kebbi ta yi masu alkawuran ƙara tura jami'an tsaro da samar da kayan yaƙi, ciki har da motocin sulke da sauran kayan aiki domin taimaka wa jami'an tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al'umma, amma har yanzu babu wani abun kirki da aka aiwatar.

Sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Jihar Kebbi da su ɗauki matakan gaggawa domin dakile hare-haren 'yan bindiga, tare da tabbatar da cewa al'ummomin Wasagu da ƙauyukan da ke kewaye da ita sun samu kariya.

Mazauna yankin sun ce rayuwar manoma na ci gaba da kasancewa cikin haɗari, lamarin da ke hana mutane zuwa gonakinsu tare da ƙara jefa al'umma cikin tsoro da rashin tabbas.

Allah Ya jiƙan Yasir da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya ba iyalansa da al'ummar Wasagu haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

RAHOTO: 'YAN NAJERIYA MILIYAN 16 NA IYA FUSKANTAR MATSANANCIYAR YUNWA NAN DA SHEKARAR 2027Daga Muhammad Musa Wani sabon ...
29/07/2026

RAHOTO: 'YAN NAJERIYA MILIYAN 16 NA IYA FUSKANTAR MATSANANCIYAR YUNWA NAN DA SHEKARAR 2027

Daga Muhammad Musa

Wani sabon rahoto ya bayyana cewa ana sa ran akalla 'yan Najeriya miliyan 16 za su fuskanci matsananciyar yunwa nan da watan Janairun shekarar 2027, idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba.

Rahoton ya danganta yiwuwar ƙara ta'azzarar matsalar da ci gaba da tabarbarewar tsaro, hauhawar farashin kayayyaki, sauyin yanayi, da kuma matsalolin tattalin arzikin da ke addabar ƙasar.

A cewar rahoton, miliyoyin mutane na iya shiga cikin matsanancin ƙarancin abinci, musamman a jihohin da hare-haren 'yan ta'adda, rikice-rikicen al'umma da ambaliyar ruwa s**a fi shafa.

Masana sun yi gargaɗin cewa matsalar na buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, ƙungiyoyin agaji da sauran abokan hulɗa domin ƙarfafa samar da abinci, inganta tsaro da kuma tallafa wa al'ummomin da ke cikin mawuyacin hali.

Sun kuma buƙaci gwamnatin tarayya da ta ƙara zuba jari a fannin noma, inganta hanyoyin samar da abinci, da kuma ɗaukar matakan rage illolin sauyin yanayi domin dakile ƙarin ta'azzarar matsalar yunwa a Najeriya.

Governor Nasir Idris Convenes High-Level Security Meeting to Strengthen Peace in KebbiBy Muhammad Musa Kebbi State Gover...
29/07/2026

Governor Nasir Idris Convenes High-Level Security Meeting to Strengthen Peace in Kebbi

By Muhammad Musa

Kebbi State Governor, Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), has convened a high-level security meeting with heads of security agencies and other critical stakeholders as part of efforts to reinforce peace and enhance the protection of lives and property across the state.

The strategic meeting, held at the Government House in Birnin Kebbi, brought together senior representatives of the Nigerian Armed Forces, the Nigeria Police Force, the Department of State Services (DSS), the Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), the National Drug Law Enforcement Agency (NDLEA), vigilante groups, officials of the Ministry of Internal Security, chairmen of the 21 local government areas, and members of the State Executive Council.

The meeting focused on strengthening collaboration among security agencies, improving intelligence sharing, and developing coordinated strategies to tackle emerging security threats across all parts of Kebbi State.

Governor Idris reaffirmed his administration's commitment to ensuring the safety of residents, stressing that maintaining peace and security remains a top priority of his government.

The meeting also provided an opportunity for security stakeholders to assess the current security situation, review ongoing operations, identify emerging challenges, and adopt measures aimed at sustaining peace, stability, and public safety throughout the state.

The gathering forms part of the governor's regular security engagements designed to enhance cooperation among security agencies and ensure a swift response to security challenges in Kebbi State.

Address

Birnin-Kebbi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labaran Najeriya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share