30/05/2026
Wasu mutane s**a ce ma Sayyidina Umar ya kamata 'danka Abdullahi ya gaji mulkin ka idan ka rasu, sai yace "ban yarda ba, idan mulkin da nayi alkhairi ne toh ya wadaci iyalai na daga yanzu har tashin Qiyama, idan kuma sharri ne toh ya tsaya daga kai na, kada a fadada wannan sharrin, ban yarda wani cikin family na ya samu ko karamin mukami (councilor) a gwamnatin nan ba".
Ya fadi haka ne a lokacin da aka yi masa mummunar rauni a Masallaci da Sallar Asubah, Hanjin cikin sa sun zuba 'kasa, hanta da Kodar sa an huda su, yana numfashi da kyar daf zai rasu.
Wani mutum mai suna Abu Lu'ulu'u Al'majusiy ne ya soka masa Mashi, amma Sahabbai basu barshi ya fita daga Masallacin a raye ba, sai da s**a kashe shi. Sai dai ya kashe wasu mutane da s**a yi yunkurin hana shi fita daga Masallacin.
A lokacin sai Umar yace ina Abdullahi yake? wato ina 'dansa? sai Abdullahi ya matso kusa yace "gani nan Ya Baba".
Yace kaje gidan Manzon Allah (S.A.W) ka sanar da Nana Aisha abinda ya faru dani a Masallaci yanzu, Abu Lu'ulu'u Al'majusiy ya soke ni da Mashi, kuma kace da ita ina rokon alfarma anjima kadan zan cika, idan na cika ta taimake ni da filin dake cikin dakin ta a binne ni a gefe da Manzon Allah (S.A.W) gefe da Abubakar Siddeeq.
Da aka je aka fada mata sai tace "Ayya, wallahi na tanadi sauran wannan filin ne domin idan na rasu a binne ni kusa da mijina da Babana, amma wallahi zan fifita Umar akan kaina, duk ranar dana rasu a binne ni a makabartar Baqee'a, kaje kace masa na amince".
Abdullahi Bin Umar ya koma Masallaci, sai Umar ya hango shi, yace ku tambayi Abdullahi menene Aisha tace?
Sai aka ce ta fadi abinda kake so, yace Alhamdulillah.
A lokacin Sayyidina Umar yana tallafe a jikin kafadar wani talaka daga cikin talakawan sa, sai ya cika.
Lessons:
1. Ashe Sahabbai basa son shugabanci, sai dai in ya zama musu dole, basa kaunar 'ya'yan su akai, saboda suna kallon ukubar da masu mulki zasu shiga ranar Qiyama.
2. Musulunci bai koyar da zalunci ko nuna fin karfi ba, filin da za'a