Sunnah zallah

Sunnah zallah الحمد للہ

31/05/2026

ILIMIN FALSAFA Sunnah zallah
Sheikh abdulrazak yahaya haifa

SOYAYYAR DA BA AURE, DA AUREN DA BABU SOYAYYA, DUKA SUNA JAWO MATSALASoyayya wata ni’ima ce da Allah Ya sanya tsakanin m...
31/05/2026

SOYAYYAR DA BA AURE, DA AUREN DA BABU SOYAYYA, DUKA SUNA JAWO MATSALA

Soyayya wata ni’ima ce da Allah Ya sanya tsakanin mutane, amma idan soyayya ta kasance ba tare da aure ba, tana iya zama sanadin fitina, ɓacin rai, da karya zuciya. Haka kuma idan an yi aure ba tare da soyayya, tausayi, da fahimtar juna ba, zaman aure zai iya cika da rashin jin daɗi da yawan saɓani.

Soyayyar da ba aure ba tana iya jawo:

1. Karya zuciya da baƙin ciki.
2. Shagala daga ibada da ayyuka masu amfani.
3. Faɗawa cikin abin da Allah Ya haramta.
4. Rashin mayar da hankali ga karatu ko sana’a.
5. Rikice-rikicen iyali da al’umma.

Auren da babu soyayya kuma yana iya jawo:

1. Rashin kwanciyar hankali a gida.
2. Yawan faɗa da saɓani.
3. Rashin kulawa da haƙƙoƙin ma’aurata.
4. Tasirin tarbiyya mara kyau ga yara.
5. Kaiwa ga rabuwa ko zaman wahala.

Saboda haka, mafita ita ce a gina aure a kan addini, kyawawan halaye, soyayya, girmamawa, da tausayi. Soyayya ta halal ita ce wadda take ƙara kusantar da mutane ga Allah, ta kuma samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Allah Madaukakin Sarki Ya ce:

“Kuma daga ayoyinsa akwai Ya halitta muku mataye daga cikinku domin ku samu natsuwa gare su, kuma Ya sanya soyayya da rahama a tsakaninku.” (Suratul Rum: 21)

Don haka, mafi kyawun soyayya ita ce wadda ta ƙare da aure, kuma mafi kyawun aure shi ne wanda aka gina a kan soyayya, rahama, da tsoron Allah.

Wasu mutane s**a ce ma Sayyidina Umar ya kamata 'danka Abdullahi ya gaji mulkin ka idan ka rasu, sai yace "ban yarda ba,...
30/05/2026

Wasu mutane s**a ce ma Sayyidina Umar ya kamata 'danka Abdullahi ya gaji mulkin ka idan ka rasu, sai yace "ban yarda ba, idan mulkin da nayi alkhairi ne toh ya wadaci iyalai na daga yanzu har tashin Qiyama, idan kuma sharri ne toh ya tsaya daga kai na, kada a fadada wannan sharrin, ban yarda wani cikin family na ya samu ko karamin mukami (councilor) a gwamnatin nan ba".

Ya fadi haka ne a lokacin da aka yi masa mummunar rauni a Masallaci da Sallar Asubah, Hanjin cikin sa sun zuba 'kasa, hanta da Kodar sa an huda su, yana numfashi da kyar daf zai rasu.

Wani mutum mai suna Abu Lu'ulu'u Al'majusiy ne ya soka masa Mashi, amma Sahabbai basu barshi ya fita daga Masallacin a raye ba, sai da s**a kashe shi. Sai dai ya kashe wasu mutane da s**a yi yunkurin hana shi fita daga Masallacin.

A lokacin sai Umar yace ina Abdullahi yake? wato ina 'dansa? sai Abdullahi ya matso kusa yace "gani nan Ya Baba".

Yace kaje gidan Manzon Allah (S.A.W) ka sanar da Nana Aisha abinda ya faru dani a Masallaci yanzu, Abu Lu'ulu'u Al'majusiy ya soke ni da Mashi, kuma kace da ita ina rokon alfarma anjima kadan zan cika, idan na cika ta taimake ni da filin dake cikin dakin ta a binne ni a gefe da Manzon Allah (S.A.W) gefe da Abubakar Siddeeq.

Da aka je aka fada mata sai tace "Ayya, wallahi na tanadi sauran wannan filin ne domin idan na rasu a binne ni kusa da mijina da Babana, amma wallahi zan fifita Umar akan kaina, duk ranar dana rasu a binne ni a makabartar Baqee'a, kaje kace masa na amince".

Abdullahi Bin Umar ya koma Masallaci, sai Umar ya hango shi, yace ku tambayi Abdullahi menene Aisha tace?
Sai aka ce ta fadi abinda kake so, yace Alhamdulillah.
A lokacin Sayyidina Umar yana tallafe a jikin kafadar wani talaka daga cikin talakawan sa, sai ya cika.

Lessons:

1. Ashe Sahabbai basa son shugabanci, sai dai in ya zama musu dole, basa kaunar 'ya'yan su akai, saboda suna kallon ukubar da masu mulki zasu shiga ranar Qiyama.

2. Musulunci bai koyar da zalunci ko nuna fin karfi ba, filin da za'a

29/05/2026

Allah ya mana tsari daga cikinsu
Sunnah zallah Sheikh Lawan Abubakar Shu'aib Triumph

29/05/2026

ALLAHU Akbar
buwayi Sarkin kyauta

28/05/2026

Allah ya gafarta wa Dr

Subhanallah...A hudubar da Mallam yake yi na Sallar Idi ina kallon live.Sai na ga wani abun da ya tayar min da hankali.Y...
27/05/2026

Subhanallah...

A hudubar da Mallam yake yi na Sallar Idi ina kallon live.

Sai na ga wani abun da ya tayar min da hankali.

Ya jefa ni a cikin wani tunani mai zurfi.
Ya tunatar da ni cewa, yau fa da muke sanye da sababbin kaya...

Wasu Makabarta za su je a binne su, ba Masallacin Idi ba.

Idan kun lura, akwai gawa a gefen Mallam a cikin makara.

Wannan bawan Allah, watakila yana da burin tashi da safiyar nan da ransa.

Watakila har sababbin kayan Sallah ya dinka don yayi murnar yau da iyalansa.

Amma Allah Ya kaddara cewa likkafani ne zai zama suturarsa ta yau.

Wallahi mu ji tsoron Allah.
Mutuwa ba ta duba girman rana ko lokacin biki.

Allah Ya kyautata namu karshen.

Allah ya jikan wannan mamucin ya masa Rahma.
UMAR ALIYU DAHIRU ✍️

BARKA DA SALLAHAbubuwa Goma Da Za A Kiyaye Ranar Idi1. Yin Godiya Ga AllahRanar idi rana ce ta farin ciki da godiya ga A...
27/05/2026

BARKA DA SALLAH

Abubuwa Goma Da Za A Kiyaye Ranar Idi

1. Yin Godiya Ga Allah

Ranar idi rana ce ta farin ciki da godiya ga Allah bisa ni’imominSa da damar ibada da Ya ba mu.

2. Yin Sallah Da Wuri

A kula da halartar sallar idi cikin tsafta, nutsuwa da ladabi tare da sauraron huɗuba.

3. Sanya Tufafi Masu Tsabta

Musulunci yana son tsafta da ƙyau. A sanya tufafi masu kyau ba tare da alfahari ko nuna isa ba.

4. Yawaita Takbiri Da Ambaton Allah

A ranar idi a riƙa yawaita:
“Allahu Akbar, Allahu Akbar, La ilaha illallahu Wallahu Akbar, Allahu Akbar wa lillahil hamd.”

5. Ziyartar Iyaye Da ‘Yan Uwa

Idi lokaci ne na haɗin kai da ƙarfafa zumunci tsakanin dangi da abokai.

6. Faranta Ran Marayu Da Talakawa

A tuna da mabukata ta hanyar kyauta, abinci da taimako domin su ma su yi farin ciki.

7. Gujewa Saɓo Da Alfasha

Kada a mai da ranar idi ranar rawa ta batsa, shaye-shaye, ko aikata abin da zai fusata Allah.

8. Kiyaye Mu’amala Tsakanin Maza Da Mata

A guji cuɗanya mara kyau, tsiraici da duk wani abu da zai iya jawo fitina.

9. Gujewa Ɓarna Da Rikici

Idi ba ranar faɗa, tashin hankali ko ɓata dukiya ba ce. A kiyaye zaman lafiya da mutunta juna.

10. Tuna Da Ma’anar Idi

Idi ba tufafi da abinci kawai ba ne; rana ce ta ibada, farin ciki halal da ƙarfafa soyayya tsakanin al’umma.

Idan aka kiyaye waɗannan abubuwa, ranar idi za ta kasance ranar albarka, farin ciki da haɗin kai. Allah Ya sa mu dace da kiyaye dokokinSa a kowace rana, ba ranar idi kawai ba.

30/01/2026

Address

Bauchi
ADA

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sunnah zallah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Sunnah zallah:

Share