13/07/2026
S**ar Atiku: Akwai Rashin Hankali Da Rashin Tarbiyya A Kalaman Suwaiba Aslam - Imrana Nas
An bayyana kalaman da wata mata mai suna Suwaiba da ake wa lakabi da Aslam ta yi akan mai girma tsohon mataimakin shugaban ฦasa kuma ษan takarar shugabancin ฦasa a ฦarฦashin jam'iyyar ADC Alhaji Atiku Abubakar a matsayin kalamai na rashin hankali da rashin tarbiyya da bai k**ata su fito daga bakin mace ba
Bayanin haka ya fito ne daga bakin shugaban rundunar talakawan Nijeriya kuma jigo a tafiyar Atiku Abubakar Alhaji Imrana Nas, lokacin da yake jawabi a yayin wani taron manema labaru da ya kira a Kaduna
Imrana Nas ya ฦara da cewar da ace Suwaiba tana da hankali kuma ta san abin da take yi, to k**ata ya yi lokacin da taga abubuwan da take zargi sun canza a matsayinta ta wadda ta shafe shekaru da dama a cikin tafiyar Atiku, da sai ta janye jikinta kawai a daina ganinta hakan zai fi yi mana ciwo, amma sakin baki da ta rinฦa yi a kafafen watsa labarai hakan ya nuna rashin tarbiyya
"Suwaiba kin nuna ba ki da tarbiyya bisa ga kalamanki na cewar wai za ki fasa ฦwai! Wannan kalma ta yi muni ace ta fito daga bakin mace, shin ba za kiyi tunanin cewa za a yi miki wata fassara ta daban ba, wanda zai iya shafar mutuncin 'ya'yan ki da 'yan uwanki ko iyayenki gaba ษaya? Ni nasan mahaifinki abokin kasuwanci na ne a Kaduna Mutumin Kirki ne, na san ba zai ji dadi da waษannan kalaman naki ba masu sanya zargi da tuhuma!"
"Daga ฦarshe ina kira da babbar murya ga Suwaiba da ta yi gaggawar janye kalaman da ta yi, sannan ta yi hanzarin ganin mai girma Alhaji Atiku Abubakar ta nemi gafarar wadannan kalaman da ta yi, ni Imrana Nas ina umartar ki da ki yi haka a matsayina na ubanki abokin mahaifinki "