23/06/2026
Wata kungiyar Fulani ta yi kira ga Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, da su dauki mataki kan fitaccen mai rajin kare muradun Yarabawa, Sunday Igboho, bisa zargin kalamai da ayyukan da kungiyar ta ce na iya tayar da hankalin jama'a da kawo barazana ga zaman lafiya.
Kungiyar ta bayyana cewa akwai bukatar gwamnati ta sanya baki domin hana duk wani abu da ka iya haddasa rashin jituwa tsakanin kabilu da al’ummomi a kasar nan. Ta ce dole ne a tabbatar da cewa kowa yana bin doka da oda domin kare hadin kai da zaman lafiyar Najeriya.
A cewar kungiyar, matakin da take nema ba wai na nuna wariya ba ne, illa tabbatar da cewa babu wanda zai kasance sama da doka, komai matsayinsa ko tasirinsa a cikin al’umma.
Kungiyar ta kuma jaddada cewa shugabannin kasar da na jihar Oyo suna da alhakin tabbatar da zaman lafiya da kare hakkin kowane dan kasa ba tare da la’akari da kabila ko addini ba. Ta bukaci gwamnati ta gaggauta daukar matakin da ya dace domin kauce wa duk wani rikici da ka iya tasowa.
Daga Bakin Kungiyoyin Fulani Masu Kishin Zaman Lafiyar Nigeria,