Kaduna State of Nigeria Students' Union Egypt.

Kaduna State of Nigeria Students' Union Egypt. It's a page that focuses on bringing to you the nitty-gritty of organization and it's members day-today activities and accomplishments.

January 1 2026.BARKA DA SABUWAR SHEKARA.A madadin Ƙungiyar Ɗaliban Jihar Kaduna a Masar, muna taya dukkan ɗaliban Jihar ...
01/01/2026

January 1 2026.

BARKA DA SABUWAR SHEKARA.

A madadin Ƙungiyar Ɗaliban Jihar Kaduna a Masar, muna taya dukkan ɗaliban Jihar Kaduna murnar shigowar sabuwar shekara, tare da miƙa sakon fatan alheri ga dukkan ɗaliban Najeriya baki ɗaya. Muna roƙon Allah Ya sanya wannan shekara ta kasance mai albarka, cike da nasarar karatu, lafiya, kwanciyar hankali, da cigaba ga kowa.

Yayin da muke shiga wannan sabuwar shekara, muna kira ga kowane ɗalibin Najeriya da ya kasance cikin haɗin kai, zumunci, da kishin ƙasa. Ƙarfimmu tana cikin kasancewa tare, ba tare da la’akari da bambancin jihohi, kabilu, ko akidu ba, cikin girmamawa da ɗaukar alhaki na bai ɗaya. Ku tuna cewa kowane ɗalibin Najeriya a Masar jakada ne na ƙasarmu, Najeriya. Don haka, halayyarmu, maganganunmu, da ayyukanmu suna da matuƙar muhimmanci. Mu kasance masu bin doka, masu tarbiyya, kuma abin koyi a kowane lokaci.

Haka kuma, muna jaddada muhimmancin sabunta IQAMA (residence permit) a kan lokaci. Batun Iqama ba zaɓi ba ne, abu ne mai matuƙar muhimmanci. Ɗaliban da har yanzu ba su sabunta Iqaman su ba ana shawartarsu da su ɗauki wannan lamari da muhimmanci ba tare da jinkiri ba. A halin yanzu, irin waɗannan ɗalibai su rage yawo ba tare da dalili ba, su guji wuraren da ake yawan kamawa, su kuma kasance masu taka tsantsan har sai an kammala daidaita matsayinsu.

Yayin da jarrabawar zangon farko ke farawa, muna yi wa dukkan ɗalibai fatan alheri da nasara. Ku yi shiri sosai, ku mai da hankali, ku kuma ba da iyakar ƙoƙarinku. karatunku amana ce gare ku, ga iyayenku, da kuma ƙasarku.

A ƙarshe, muna sake yi muku barka da sabuwar shekara. Allah Ya sanya wannan shekara ta kasance ta haɗin kai, ɗaukar nauyi, da manyan nasarori.

Sa hannu:
Zakariyyah Zaria
Secretary General KADSSUE

🎙: Abdulkarim Shehu Abbas
PRO KADSSUE

January 1, 2026HAPPY NEW YEAR On behalf of the Kaduna State Students Union in the Arab Republic of Egypt, we warmly feli...
01/01/2026

January 1, 2026

HAPPY NEW YEAR

On behalf of the Kaduna State Students Union in the Arab Republic of Egypt, we warmly felicitate with all Kaduna State students and, by extension, all Nigerian students on the commencement of a new year. We pray that this year brings clarity of purpose, academic excellence, good health, and progress for us all.

As we move forward, we call on every Nigerian student to uphold unity, brotherhood, and patriotism. Our strength lies in standing together across states, tribes, and beliefs with mutual respect and shared responsibility. Let us remember that every Nigerian student in Egypt is an ambassador of our great nation. Your conduct, speech, and choices matter. Be law-abiding, disciplined, and exemplary at all times.

We also wish to strongly remind all students of the importance of renewing their residence permits promptly. Residency matters are not optional they are critical. Students who are yet to renew their permits are advised to take this seriously without delay. In the interim, such students should minimize unnecessary movement, avoid areas known for arrests, and remain cautious until their status is regularized. Compliance protects you and safeguards the collective image of Nigerian students.

As the first semester examinations begin, we wish all students the very best of luck and outstanding success. Prepare well, stay focused, and give your best. Your academic journey is a trust to yourselves, your families, and your country.

Once again, Happy New Year. May this year be defined by unity, responsibility, and achievement.

Signed:
Zakariyyah Zaria
Secretary General KADSSUE

🎙: Abdulkarim Shehu Abbas
PRO KADSSUE

June 14, 2025.SAKON TA’AZIYYA DAGA ƘUNGIYAR DALIBAN JIHAR KADUNA A MISIRA KAN RASUWAR TSOHON SHUGABAN KASA, MUHAMMADU BU...
14/07/2025

June 14, 2025.

SAKON TA’AZIYYA DAGA ƘUNGIYAR DALIBAN JIHAR KADUNA A MISIRA KAN RASUWAR TSOHON SHUGABAN KASA, MUHAMMADU BUHARI.

Inna lillahi wa inna ilayhi raji’un
Ƙungiyar Daliban Jihar Kaduna a Ƙasar Masar na bayyana alhini da jimami kan rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Muhammadu Buhari (rtd), wanda Allah ya karɓi rayuwarsa. Muna miƙa ta’aziyyar mu ga iyalansa, al’ummar Najeriya baki ɗaya, da kuma ɗaliban Najeriya mazauna ƙasar Masar.

Marigayin ya rayu rayuwa ta sadaukarwa da bautar ƙasa, tun daga lokacin da ya shiga aikin soja har zuwa lokacin da ya riƙe shugabancin ƙasa. Ko da yake tarihin rayuwarsa na iya bambanta ra’ayoyi, amma babu shakka ya taka rawa mai muhimmanci wajen gyaran Najeriya bisa fahimtarsa da hangen nesansa. Yayi rayuwa mai cike da ƙoƙari da gaskiya, yana neman zaman lafiya da ci gaba ga ƙasarmu.

Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki ya jikan sa, ya yafe masa kurakuransa, ya sanya kabarinsa cikin lambun Aljanna. Allah ya bai wa iyalansa da dukan ’yan Najeriya haƙuri da ƙarfin zuciya wajen jure wannan babban rashi.

Ya Allah, Ka gafarta masa, Ka yi masa rahama, Ka yafe masa, Ka karɓe shi cikin mafificiyar matsuguni, Ka faɗaɗa masa kabarinsa, Ka wanke shi da ruwa, ƙanƙara da sanyi, Ka tsarkake shi daga zunubi kamar yadda ake tsarkake farin kaya daga datti. Ya Allah, Ka sanya kabarinsa ya zama lambun Aljanna, Ka azurta shi da Aljannar Firdausi ba tare da wata wahala ba.

Allah Ya jikansa da rahamarsa. Allah Ya tsare Najeriya da zaman lafiya da haɗin kai.

Sa Hannu:
Muhammad Fatihu Sunusi
Ag. President KADSSU Egypt.

June 14, 2025.CONDOLENCE MESSAGE ON THE DEMISE OF FORMER PRESIDENT MUHAMMADU BUHARIInna lillahi wa inna ilayhi raji’un (...
14/07/2025

June 14, 2025.

CONDOLENCE MESSAGE ON THE DEMISE OF FORMER PRESIDENT MUHAMMADU BUHARI

Inna lillahi wa inna ilayhi raji’un (Indeed, to Allah we belong and to Him we shall return).

With hearts heavy with sorrow and submission to the will of Almighty Allah, the Kaduna State Students Union in Egypt extends its deepest condolences to the family of former President Muhammadu Buhari, the people of Nigeria, and the entire Nigerian students in Egypt on the sad news of his passing.

President Muhammadu Buhari was a towering figure whose life was dedicated to the service of our great nation. A man of integrity, discipline, and strong belief, his leadership left a lasting legacy in the history of Nigeria. While opinions may differ in the pages of history, we recognize the immense burden of national responsibility he carried with dignity and resilience. His life was one of service, first as a soldier and then as a statesman, always striving for a more secure and accountable Nigeria.

To his beloved family, we pray that Allah (SWT) grants you strength and patience during this difficult time. To all Nigerian students in Egypt and Nigerians across the globe, we share in your grief, and we stand united in remembrance of a man whose presence shaped our national journey.

We pray: “O Allah, forgive him and have mercy on him, pardon him and grant him noble accommodation. Expand his entrance, and cleanse him with water, snow, and ice, and purify him from sins as a white garment is purified from dirt. O Allah, make his grave a garden from the gardens of Paradise and grant him Al-Firdaus without reckoning.”

May the Almighty count him among the righteous, accept his good deeds, and forgive his shortcomings. Ameen.
May Nigeria continue to rise in peace, unity, and strength.

Signed:
Muhammad Fatihu Sunusi
Ag. President KADSSU Egypt.

🕊️ SANARWA TA MUSAMMAN DAGA KADSSU EGYPT 🕊️Ƙungiyar Daliban Jihar Kaduna a Misra ta bayyana alhini da jimami dangane da ...
23/06/2025

🕊️ SANARWA TA MUSAMMAN DAGA KADSSU EGYPT 🕊️

Ƙungiyar Daliban Jihar Kaduna a Misra ta bayyana alhini da jimami dangane da mummunan harin da ya faru a Mangu, Jihar Filato, wanda ya yi sanadiyyar rasa rayukan wasu matafiya daga Zariya.

Muna jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa, tare da yin kira ga hukumomi da su tabbatar da ganin adalci ya yi aiki. Mutanen Zariya sun dade suna rayuwa cikin zaman lafiya da haɗin kai, ba su cancanci hakan ba.

Muna tare da al’umma a cikin wannan juyayi. Allah ya ba mu zaman lafiya.

PRESS STATEMENT FROM THE KADUNA STATE STUDENTS UNION IN EGYPTThe Kaduna State Students Union in Egypt is deeply saddened...
22/06/2025

PRESS STATEMENT FROM THE KADUNA STATE STUDENTS UNION IN EGYPT

The Kaduna State Students Union in Egypt is deeply saddened by the recent tragic incident in Mangu Local Government Area of Plateau State, where innocent travelers from Zaria, Kaduna State, were attacked and killed. These individuals, reportedly on their way to attend a wedding, lost their lives in a horrific act of mob violence. We extend our heartfelt condolences to the families of the deceased and all affected, especially our fellow students from Sabon Gari Local Government and the entire Kaduna State student community.

As a student body representing peace-loving citizens abroad, we firmly condemn this senseless act. The people of Zaria have always embraced unity and peaceful coexistence, welcoming Nigerians from every background without discrimination. It is truly heartbreaking to see such a community subjected to this level of cruelty and injustice. Zaria has never retaliated in the face of provocation, and we believe such a peaceful people deserve protection, not violence.

We respectfully call on the Governor of Kaduna State, His Excellency Senator Uba Sani, The Honorable speaker, House of Representatives Rt. Hon. Tajuddeen Abbas, to follow up on this matter and ensure that justice is served. We also urge the Plateau State Government to take full responsibility and provide compensation to the affected families. This tragedy must not be ignored or forgotten, it must be addressed with the seriousness it deserves to prevent future occurrences.

Finally, we call on the Emir of Zazzau, His Highness Amb. Ahmed Nuhu Bamalli, to lend his voice in consoling the people and advocating for justice. To all Kaduna State students in Egypt, we share in your grief. Let us remain united, hopeful, and committed to peace, even in the face of sorrow.

Sign.
Sh*tu Abbas Ubandawaki
President KADSSU Egypt.

📢: Abdulkarim Shehu Abbas
P. R. O

Bayani akan mukamin PRO 2
17/05/2025

Bayani akan mukamin PRO 2

Ƙungiyar Ɗaliban Jihar Kaduna a Ƙasar Masar (KADSSUE).Takaitaccen Bayanin Taron Zaman ShugabanniMay 16,  2025An gudanar ...
17/05/2025

Ƙungiyar Ɗaliban Jihar Kaduna a Ƙasar Masar (KADSSUE).
Takaitaccen Bayanin Taron Zaman Shugabanni
May 16, 2025

An gudanar da zaman shugabanni na ƙungiyar Ɗaliban Jihar Kaduna a Masar cikin nasara tare da halartar manyan mambobi na shugabancin ƙungiyar. An fara taron da addu’ar buɗewa, sannan shugaban ƙungiyar, Comrade Abbas Sh*tu, ya gabatar da jawabi inda ya jaddada muhimmancin ƙarfafa tsarin aiki da haɗin kai a tsakanin shugabanni.

Muhimman Abubuwan da Aka Cimma:
1. Nadawa da Sake Nadawa:
• An tabbatar da nadin wasu mutane a muƙamai masu mahimmanci domin ƙarfafa aikin ƙungiyar. Ga jerin waɗanda aka naɗa:
• Imam Zubairu Liman – An naɗa shi a matsayin Sabon Sakataren Kuɗi na ƙungiyar.
• Anas Sani Isah – An naɗa shi a matsayin Wakilin Ƙungiyar a Maraj Jadiidah.
• Abdulkarim Shehu Abbas – An naɗa shi a matsayin PRO I (Jami’in Hulɗa da Jama’a na Ɗaya) da kuma Shugaban Kwamitin Watsa Labarai.
• Abubakar Musa Aliyu – An naɗa shi a matsayin Mataimakin Shugaban Kwamitin Watsa Labarai, kuma Wakilin Ƙungiyar a Maraj Qadiimah.
2. Kaddamar da Kwamitin Watsa Labarai:
• An kaddamar da kwamitin watsa labarai tare da gabatar da mambobinsa. An bayyana musu nauyin da ke kansu da rawar da za su taka wajen yada ayyukan ƙungiyar da kuma inganta sadarwa tsakanin ɗalibai.
3. Tattaunawa da Bayyana Ra’ayoyi:
• An gudanar da tattaunawa mai ma’ana kan muhimman batutuwan da ke shafar walwalar ɗalibai.
• Daya daga cikin batutuwan da aka tattauna sosai shine farmakin ‘yan sanda akan ɗalibai da ke zama a ƙasar ba bisa ƙa’ida ba. Ƙungiyar ta yanke shawarar wayar da kan ‘yan uwa ɗalibai kan muhimmancin yin rajista da sabunta takardun zama (residence permit) domin kauce wa matsaloli da jami’an tsaro.
• An kuma gabatar da shawarwari da dama kan yadda za a ƙara ƙarfafa haɗin kai, sauƙaƙe sadarwa da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a cikin shugabanci.
4. Abin sha'awa:
• Zaman ya ƙare da haske mai daɗi, wanda ya haifar da yanayi na yau da kullun don haɗin kai da ƙarin tattaunawa tsakanin membobin.

Taron ya ƙare da jawabin rufewa da addu’ar karshe. An shawarci mambobin shugabanci da su fara aiwatar da aikinsu nan da nan cikin gaskiya da sadaukarwa.

✒️: Gen. Sec: Zakariyya Zaria
🔈: P.r.o I : Abdulkarim Shehu Abbas

Bangajiya da Godiya ga Baƙi da MahalartaAssalamu Alaikum wa Rahmatullah wa Barakatuhu.A madadin shugaban kungiyan daliba...
05/04/2025

Bangajiya da Godiya ga Baƙi da Mahalarta

Assalamu Alaikum wa Rahmatullah wa Barakatuhu.

A madadin shugaban kungiyan daliban jihar kaduna a masar (KADSSUE) Comr. Sh*tu Abbas Ubandawaki da wakilan Zartarwar sa, muna miƙa godiya ta musamman ga dukkan manyan baƙi, dattawa, shugabanni, da ‘yan uwa dalibai da s**a amsa gayyatar mu kuma s**a halarci Taron Sallah. Haƙiƙa, kasancewarku ya ƙara wa taron armashi, nishadi, da ƙima.

Mun yi murna, mun yi zumunci, kuma mun shakata tare cikin farin ciki. Wannan haduwa ta ƙara mana ƙauna da haɗin kai. Muna fatan za a ci gaba da irin wannan zumunci da haɗin gwiwa a nan gaba.

Allah ya saka da alheri, ya albarkaci rayuwarku, kuma ya sada mu da alheri a gaba.

Muna godiya ƙwarai!

🖊️: General secretary: ZAKARIYAA ZARIA
🔈:P.r.o:
ABDULKARIM SHEHU ABBAS

🌙✨ Eid Mubarak! ✨🌙Kaduna State Students in Egypt and all Nigerian students, we extend our warmest Eid greetings to you. ...
31/03/2025

🌙✨ Eid Mubarak! ✨🌙

Kaduna State Students in Egypt and all Nigerian students, we extend our warmest Eid greetings to you. May this blessed day bring joy, peace, and countless blessings. May our hearts be filled with gratitude, our unity grow stronger, and our prayers be answered.

May Allah’s mercy, guidance, and prosperity be with us all—now and always.

Address

Riyad 9 Shams Street Makram Abeed, Nasr City
Cairo

Telephone

+201141894870

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kaduna State of Nigeria Students' Union Egypt. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Kaduna State of Nigeria Students' Union Egypt.:

Share