Al-ihsan Educational Foundation For Orphans

Al-ihsan Educational Foundation For Orphans Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Al-ihsan Educational Foundation For Orphans, Charitable organisation, Memphis, TN.

Muhimmancin ilimantar da marayaIlimantar da maraya yana da matuƙar muhimmanci ga rayuwarsu da kuma cigaban al’umma baki ...
05/06/2026

Muhimmancin ilimantar da maraya

Ilimantar da maraya yana da matuƙar muhimmanci ga rayuwarsu da kuma cigaban al’umma baki ɗaya. Ga wasu daga cikin muhimmancin hakan:

Ba su damar dogaro da kansu
Ilimi yana taimaka wa maraya su samu sana’a ko aiki mai kyau domin su iya kula da rayuwarsu ba tare da dogaro da wasu ba.

Kare su daga talauci da rashin tarbiyya
Yara marayu idan ba su samu ilimi ba, suna iya fadawa cikin bara, aikata laifi ko shiga mummunar hanya. Ilimi yana ba su kyakkyawar makoma.

Gina kyawawan halaye
Ilimi yana koyar da tarbiyya, ladabi, girmama na gaba da kuma sanin addini da al’ada mai kyau.

Ƙara musu kwarin gwiwa
Maraya da s**a samu ilimi suna jin cewa su ma suna da daraja a cikin al’umma, hakan yana ƙara musu ƙarfin guiwa da fata a rayuwa.

Taimakawa cigaban ƙasa
Idan aka ilimantar da marayu, za su zama likitoci, malamai, injiniyoyi da sauran masu amfani ga al’umma a gaba.

Cika umarnin addini da jinƙai
Addinin Musulunci da sauran addinai suna ƙarfafa kula da marayu da taimaka musu, musamman wajen ba su ilimi da tarbiyya mai kyau.

Rage yawan yara marasa galihu a t**i
Ilimantar da maraya yana rage yawan yara masu yawon bara ko zaman banza a t**i.

NEMAN TAIMAKOTana da yara Hudu (4), babu cin yau babu na gobe, haka zalika yara hudu basa zuwa makaranta duk saboda kunc...
10/04/2025

NEMAN TAIMAKO

Tana da yara Hudu (4), babu cin yau babu na gobe, haka zalika yara hudu basa zuwa makaranta duk saboda kunci na rayuwa, babu miji ya rasu, ga gidan da suke ciki shima ya samu matsala.
Yarinya ta farko ya kamata a Kaita primary amman Babu dama, ta biyu kuma SS 1 zata shiga shima rashin ƙarfi ya hana, sai ta uku ita junior school za'a Kaita itama Babu dama , hatta abincin da zasu ci yauma babu.

Ƴan uwa duk wanda ya yayewa wani ƙunci shima Allah zai yaye masa nasa ƙuncin
Sunanan a gandun Sarki, Gbs Road, malam madori Lga

8131870045
Opay
Muhammad Sani

Duk wanda ya tura ya Turo receipt saboda updating

MUNA NEMAN TALLAFIN UNIFORM NA GGSS MALAM MADORI.Kamar yanda muka nemi tallafin yanda zaa mayar da wata baiwar Allah mak...
08/01/2025

MUNA NEMAN TALLAFIN UNIFORM NA GGSS MALAM MADORI.

Kamar yanda muka nemi tallafin yanda zaa mayar da wata baiwar Allah makaranta bayan daukar lokaci da rasuwar mahaifinta, da hakan tasa bata samu halartar ajin gaba ba, cikin ikon Allah an samu nasarar kaita Babbar Sakandiren yan mata ta Malam Madori (GGSS Malam Madori).

abin da muke kara neman tallafinku akai shi ne Uniform musamman na karatun yamma, wannan ita ce babba cikin matsalolin da Khadija Dawaki ke fuskanta a yanzu.

Muna fatan zame mata silar warwarar wannan matsala kafin komawa makaranta, domin rabauta da ladan tallafawa marainiya da Allah ke bayarwa ga bayin da s**a yi hakan.

Mun gode.
08100503426.
Al-ihsan Educational Foundation For Orphans

Al-ihsan Educational Foundation For OrphansHadejia, Jigawa State08100503426babaalhajimuhd@gmail.comDear Esteemed Support...
04/27/2025

Al-ihsan Educational Foundation For Orphans
Hadejia, Jigawa State
08100503426
[email protected]
Dear Esteemed Supporter,
REQUEST FOR SUPPORT TOWARDS THE EDUCATION OF KHADIJA GARBA, A 16-YEAR-OLD ORPHAN FROM KALGWAI VILLAGE, AUYO L.G.A
Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuhu,
I pray this letter meets you in good health and prosperity.
I am writing on behalf of Al-Ihsan Educational Foundation to humbly request your support for Miss Khadija Garba, a 16-year-old orphan from Kalgwai Village in Auyo Local Government Area. Following the death of her father, Khadija was forced to abandon her education after completing Junior Secondary School five years ago.
Today, with strong determination and hope, Khadija wishes to return to school and pursue her Senior Secondary education. However, due to her family's financial hardship, she cannot afford the basic requirements to resume schooling.
We are appealing to kind-hearted individuals, politicians, businessmen, and organizations to assist in supporting Khadija with:
School uniform
Textbooks, exercise books
Other essential learning materials
Your support, no matter the size, will make a tremendous difference in the life of this young girl, giving her the opportunity to realize her dreams and contribute positively to society.
We believe that helping one child is helping an entire generation. Your generosity will not only change her life but will also be a great investment in our community’s future.
May Allah (SWT) continue to bless you abundantly and reward your kindness both in this life and the Hereafter.
Thank you for your consideration and support.
Yours faithfully,
Baba Alhaji Muhammad
Founder, Al-Ihsan Educational Foundation

04/23/2025

WATA YARINYA DAGA ƘAUYEN KALGWAI TA ZO TANA NEMAN A SAKA A MAKARANTA, TUN BAYAN MUTUWAR MAHAIFINTA TA RASA WANNAN DAMAR

Ina zaune a wurin aiki, sai aka ce ana nemana, ko da na fito na tarar da Yarinya matashiya, na tambayeta abin ke tafe da ita, sai ta shaidamin cewa, zuwa ta yi atemaka a sakata a makarantar Sakandiren Madani Elleman, sakamakon tun lokacin da mahaifinta ya rasu, mahaifiyar ta bata da halin kaita makaranta, hakan ta sa tun bayan kammala Junior a shekarar 2021 ta ke zaune a gida.

Abokan karatunta yanzu haka tuni s**a kammala Babbar Sakandare. Na gamsu da irin bayanan da ta zo dasu, domin a yanda ire-iren ta suke gudun karatu, ta sa na gamsu lallai ta na so kuma za'a temaka mata da duk abin da ya kamata.

Nan take na tuntuɓi wata baiwar Allah a Elleman domin jin yanda tsarin makarantar yake, take kuwa ta haɗani da matemakin shugaban makarantar, na kirashi muka kuma tattauna game da lamarin, ya kuma buƙaci mai tsaye mata (Guidance) domin ta hannunsa ne kawai zasu iya bata gurbin karatu.

Na rubuta mata lambar wayata da zumbar ta kaiwa mahaifiyar ta kirani domin ƙarƙarewa, da zarar ta kira zan sanar da matemakin shugaban makarantar.

Da haka muke nema mata tallafinku na littafan Rubutu, Jaka, Kayan Makaranta da duk abin da Allah ya h**e.

Za'a iya amfani da bayanan Banki wajen bayar da gudunmawar.

8100503426
Opay/Monie Point
Baba Alhaji Muhammad.

Allah ya miki Rahama yasa bakin wahalar kenan
03/22/2025

Allah ya miki Rahama yasa bakin wahalar kenan

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN, LA ILAHA ILLA ANTA SUBHANAKA INNI KUNTU MINAZZALIMIINWannan da kuke gani Guiwa ce ta...
03/09/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN, LA ILAHA ILLA ANTA SUBHANAKA INNI KUNTU MINAZZALIMIIN

Wannan da kuke gani Guiwa ce ta wata yarinya da Allah ya jarabceta da ciwo, tun tana matakin ɗingishi mahaifanta suna tunanin ko sanyi ne, an yi bakin ƙoƙari wajen yi mata magani, amma kullum ciwo ƙara ta'azzara yake.

ko da s**a je Asibiti, sai aka ɗorasu akan magani, shi ma dai maimakon sauƙi ya samu, sai rage zafin ciwon kawai aka samu, tare da ta'azzarar girman guiwar kamar yanda kuke gani.

Abin tausayin shine, mahaifan wannan yarinya suna cikin halin rashi da ƙoƙorin ya za'a yi a rayu, ga kuma irin jarrabawar ɗiyarsu ta tsinci kan ciki, kuma shekarun yarinyar bai wuce 14 ba.

Likita ya shaida cewa, bazai yiwu ayi mata aiki a Hadejia ba, dole sai anje Asibitin Dala, domin akwai yiwuwar cutar daji ce ta shigeta (CANCER).

Da haka muke roƙa mata gudunmawar al'ummar musulmai da ku temaka ku tayamu ceto rayuwar wannan yarinya.
ana so aje Asibitin Dala domin gwaji da kuma yin aiki, kudin gwajin ma a yauzu wani tashin hankalin ne, domin baa san me zaa tarar ba.

ku tallafa da gudunmawarku ta Bayanan Banki kamar haka:
6820982974,
BABA ALHAJI MUHAMMAD,
Moniepoint MFB
a tuntubi waɗannan numbobi domin ƙarin bayani akai.
08100503426, 07036478823, 07068756358.
Don Allah a temaka, Agajin gaggawa!

NA TATTAUNA DA MAHAIFAN YARINYAR DA TALLA KE HANA TA ZUWA MAKARANTACikin ikon Allah, yau na samu damar zuwa gidansu ɗali...
02/24/2025

NA TATTAUNA DA MAHAIFAN YARINYAR DA TALLA KE HANA TA ZUWA MAKARANTA

Cikin ikon Allah, yau na samu damar zuwa gidansu ɗalibar da muka samu labarin yanda ƙaramin ƙarfi ke ƙoƙarin rabata da makaranta, yanda ta zaɓi ta yi talla akan karatu, duk da cewa ba wai karatun ne bata so ba, sai don ba ta da wani zaɓin.

Mun tattauna game da matsaloli da dama, wanda duka basu wuce matsalar samun wadataccen abinci da kayan karatu ba, na yi ƙoƙarin shawo kan yarinyar da ta yarda a maida ita makaranta, tare da alƙawarta mata cewa, zamu ɗauke mata biyan kowa ne irin kuɗi da za'a iya buƙata da abin da zata ci in sha Allah.

Jama'a a taya da addu'a wajen cika wannan alƙawari, tare da gudunmawarku.

Allah ya mana jagora.

Address

Memphis, TN

Telephone

+19016089083

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al-ihsan Educational Foundation For Orphans posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share