Aitaam Foundation

Aitaam Foundation Helping each other

24/04/2026
‎Neman Taimakon gaggawa!‎‎Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh. ‎‎Al’ummar Musulmi masu daraja, kamar yadd...
12/04/2026

‎Neman Taimakon gaggawa!

‎Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh.

‎Al’ummar Musulmi masu daraja, kamar yadda wannan Mu’assasa ta marayu ta ɗauki alƙawarin yin aikin taimakon Marayu da marasa galihu yau ma ga wani aikin taimakon ya ƙara samuwa, wannan bawan Allah da kuke kallo a cikin waɗannan hotunan yana kwance a asibitin Dakta Bello cikin halin jinya kuma yana mai buƙatar taimakon gaggawa.

‎Kamar yadda Allah Ta'ala ya taimake mu ya bar mu da ran mu da lafiyar mu, ya ku al’ummar Musulmi mu taimaki wannan bawan Allah, mai taro mai sisi, ka da mu manta Allah Ta'ala yana faɗa a cikin Alƙur'ani mai girma; 'Bismillahir Rahmanir Rahim' .

‎“مَن جَاءَ بِالْحَسَنَةِ فَلَهُ عَشْرُ أَمْثَالِهَا”

‎Duk wanda ya zo da aiki nagari (kyakkyawan aiki), to yana da lada sau goma makamancin sa.

‎Falalar Allah mai yawa ce, wannan aya tana nuna cewa Allah ba ya sakawa daidai da aikin mutum, sai dai yana ƙara masa lada. Aiki ɗaya na alheri zai iya zama lada sau goma ko ma fiye.

‎Sadaka ba ta kaɗan, sannan kuma ba ta yawa, mu taimaki wannan bawan Allah muma Allah zai taimake mu.

‎Account Number;
‎8060881219
‎Abdulrahman Ibrahim
‎Palmpay

‎Rahoto daga;
‎Mustapha Muhammad ɗaya daga cikin Media Team na 'Aitaam Foundation' dake Unguwar Jaba ƙaramar hukumar Sabon Garin Zariya.

‎Wasalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh.

‎Tallafin gaggawa zuwa ga Marayu!‎‎Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh;‎‎'Yan’uwa masu daraja muna son sa...
03/04/2026

‎Tallafin gaggawa zuwa ga Marayu!

‎Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh;

‎'Yan’uwa masu daraja muna son sake tunatar da kan mu game da amanar kula da marayu da Allah Ta'ala ya ɗora mana.

‎Maraya ba mujarradin yaro ne kawai ba - yaro ne da ya rasa gata, kulawa da kariya. Amma Allah ya ba mu dama, domin mu zama dalilin murmushinsa, mu zama hasken rayuwarsa.

‎Kamar yadda Allah Ta'ala ya kawo a cikin Alƙur'ani mai girma, Bismillahir Rahmanir Rahim; Suratul Baqarah (2:220)

‎وَيَسْأَلُونَكَ عَنِ الْيَتَامَىٰ ۖ قُلْ إِصْلَاحٌ لَّهُمْ خَيْرٌ ۖ

‎Kuma suna tambayarka game da marayu. Ka ce: gyara al’amuransu (da kyautata musu) shi ne mafi alheri.

‎Ya ci gaba da cewa a cikin Suratul Balad (90:14-15)

‎أَوْ إِطْعَامٌ فِي يَوْمٍ ذِي مَسْغَبَةٍ، يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ

‎“Ko ciyarwa a ranar yunwa - ga maraya makusanci.”

‎Allah ya sanya ciyar da maraya cikin manyan ayyukan alheri.

‎Ya ci gaba da cewa a cikin Suratud Duha (93:9)

‎فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ

‎To amma maraya, ka da ka wulaƙanta shi.” Umarni ne kai tsaye na tausayi da kula da maraya.

‎Ya ci gaba da cewa a cikin Suratul Ma’un (107:1-3)

‎أَرَأَيْتَ الَّذِي يُكَذِّبُ بِالدِّينِ، فَذَٰلِكَ الَّذِي يَدُعُّ الْيَتِيمَ

‎Ka ga wanda yake ƙaryata addini.? Shi ne wanda yake tursasa maraya.” Nuni a kan cewa rashin kula da maraya alama ce ta rashin tausayi da raunannan imani.

‎Ya ƴan’uwana masu daraja mu tuna da ƙaramin taimakon da za mu bayar yana iya saka shi ya koma makaranta, saka shi ya ji ana ƙaunarsa, saka shi ya samu kyakkyawar makoma.

‎Ya zo a littafin Mizanul Hikma;

‎عن رسول الله (ص): إن في الجنة دارا يقال لها دار الفرح لا يدخلها إلا من فرح يتامى المؤمنين

‎ميزان الحكمة: ج2 ، ص1291

‎Daga Manzon Allah (SAW): "Lalle a cikin Aljanna akwai wani gida da ake kiransa gidan farin ciki; ba wanda zai shiga cikinsa sai wanda ya faranta ran marayu muminai."

‎Mizanul Hikmah: Juzu’i na 2, shafi na 1291.

‎A yanzu muna da ƙananan yara marayu da ke buƙatar tallafin mu. Ka da mu yi sakaci wannan aiki ba na kowa ba ne - na waɗanda Allah ya zaɓa ne.

‎Muna kira ga kowa ku ba da gudunmawa gwargwadon iko, ku shiga cikin wannan alheri. Allah ya saka da Alkhairinsa, ya sanya a cikin mizani na alkhairi.

‎Domin Tallafawa ga Account Number;
‎8060881219
‎Abdurrahman Ibrahim (Ma’aji).

‎Rahoto daga;
‎Mustapha Muhammad ɗaya daga cikin Media Team na 'Aitaam Foundation' dake Unguwar Jaba ƙaramar hukumar Sabon Garin Zariya.

‎Wassalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh.

03/04/2026

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI
Yan uwa masu daraja,
Muna so mu sake tunatar da kanmu game da amanar kula da marayu da Allah Ya dora mana.
💔 Maraya ba wai yaro ne kawai ba — yaro ne da ya rasa gata, kulawa da kariya.
🤲 Amma Allah Ya ba mu dama: mu zama dalilin murmushinsa
mu zama hasken rayuwarsa
👉 Ka tuna: Ko ƙaramin taimako da ka bayar yana iya:
saka shi ya koma makaranta
saka shi ya ji ana ƙaunarsa
saka shi ya samu kyakkyawar makoma
📌 A yanzu muna da ƙananan yara marayu da ke buƙatar tallafin mu.
Kada mu yi sakaci.
🔥 Wannan aiki ba na kowa ba ne — na waɗanda Allah Ya zaɓa ne.
👉 Muna kira ga kowa:
Ku bada gudunmawa gwargwadon iko
Ku shiga cikin wannan alheri
Allah Ya saka da mafificin alheri 🤲
Ya sanya a cikin mizani na alkhairi.
Nagode sosai

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHIAlhamdulillah 🤲 mun samu nasarar kammala shirinmu na farko na Saukar Alƙur’ani cikin nasa...
02/04/2026

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI
Alhamdulillah 🤲 mun samu nasarar kammala shirinmu na farko na Saukar Alƙur’ani cikin nasara.
Wannan nasara ba ƙarama ba ce — amma ita ce farkon tafiyar mu.
👉 Yanzu lokaci ya yi da za mu fara ainihin aikin da muka kafa wannan foundation akai — kula da marayu.
📌 Mun gano: Yara marayu guda 2 (mata), masu shekara 7
Suna karatu a makarantar Islamiyya Abubakar Gumi dake unguwar Jaba.
💔 Halin da suke ciki:
Suna buƙatar hijab na makaranta
Suna buƙatar kuɗin makaranta (₦500 per term)
Suna buƙatar uniform na boko
Suna buƙatar takalmi
Suna buƙatar littafai
🤲 Wannan dama ce daga Allah gare mu.
👉 Ka yi tunani: ₦500 kawai na iya sa yaro ya ci gaba da karatu.
👉 Idan muka haɗa kai: za mu iya sauya rayuwarsu gaba ɗaya.
📢 Muna kira ga dukkan members:
Kowa ya bada gudunmawa gwargwadon iko
Ko da ₦500 ne, yana da tasiri
👉 Za a rika tura gudunmawa kamar yadda aka saba
(screenshot + suna)
🔥 MU KAFA FOUNDATION DOMIN IRIN WANNAN LOKACI
Kada mu bari wannan dama ta wuce mu.
Allah ya saka da alheri 🤲

Assalamu Alaikum;Kamar yadda sanarwa ta gabata a wannan Gidauniya ta Aitaam 'مؤسسة الأيتام' a tsakanin membobin wannan g...
02/04/2026

Assalamu Alaikum;

Kamar yadda sanarwa ta gabata a wannan Gidauniya ta Aitaam 'مؤسسة الأيتام' a tsakanin membobin wannan gidauniya cewa za a dinga gudanar da saukar karatun Alƙur'ani mai girma a duk Larabar ƙarshen wata.

To, Alhamdulillah da yammacin jiya Laraba 1 ga watan Afrilu na shekarar 2026 Miladiyya, daidai da 13 ga watan Shawwal na shekarar 1447 Hijiriyya an gudanar da wannan sauka kamar yadda yake a tsarin tafiyar.

An fara wannan saukar ne da yammacin jiya a muhallin Masallacin Madrasatu Hidayatis-sibyan, inda bayan kammala saukar karatun Alƙur'ani mai girma hizifi Sittin (60), Maulana Sheikh Ahmad Abdul’azeez ya rufe muhallin mai albarka da addu'a, amma ka fin addu'a ya gabatar da kalmomin ƙarfafa ga ita tafiyar ta 'marayu' har yai nuni da ka da a taƙaita ga marayu kawai, akwai du’afa, amma marayu su zama sune 'ahammu' wajen fuskanta, Maulana sun ba da shawarwari mabambanta; Inda daga bisani s**a rufe wannan zama mai albarka da addu'o'insu masu albarka.

Bayan kammala addu'a, an gabatar da ƴar ƙwarya-ƙwaryar walima na godiya ga Allah Ta'ala da neman albarka Alƙur'ani mai girma a tafiyar, bayan an kammala ne aka watse, Alhamdulillah an yi lafiya an tashi lafiya.

Rahoto daga;
Mustapha Muhammad ɗaya daga cikin Media Team na 'Aitaam Foundation' dake Unguwar Jaba ƙaramar hukumar Sabon Garin Zariya.

Ga wasu hotuna da muka ɗauko daga muhallin taron!

Wasalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuh.

13/03/2026

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUH.

Ya ku ‘yan uwa mambobin AITAAM FOUNDATION, muna godiya ƙwarai da irin haɗin kai da goyon bayan da kuke baiwa wannan tafiya mai albarka ta kula da marayu da marasa galihu. Allah ya saka muku da alheri.

Domin neman taimakon Allah da samun albarka a cikin rayuwarmu da kuma ayyukan wannan foundation, mun yanke shawarar fara tsarin Saukar Al-Qur’ani duk Larabar ƙarshe ta kowane wata. Za mu riƙa yin wannan karatu ne domin:

• Neman taimakon Allah a cikin dukkan al’amuranmu
• Samun nasara da albarka a rayuwar membobinmu
• Yi wa marayu da marasa galihu addu’a
• Da kuma ƙarfafa dangantakarmu da Al-Qur’ani

Domin gudanar da wannan shiri cikin tsari, muna buɗe asusun gudunmawa domin sayen Al-Qur’ani da za a riƙa amfani da su wajen karatu da kuma rabawa ga masu buƙata.

Muna roƙon kowa ya ba da gudunmawa gwargwadon ikon da Allah ya ba shi, domin ko ƙaramin taimako yana iya zama babban alheri a wurin Allah.

Account Name: Abdurrahman ibrahim
Account Number: 8060881219
Bank: opay

Ku tuna cewa Manzon Allah ﷺ ya ce:

“Mafi alherin ku shi ne wanda ya koyi Al-Qur’ani kuma ya koyar da shi.”

Wannan dama ce ta samun lada mai yawa da kuma jawo rahamar Allah a rayuwarmu.

Allah ya sanya albarka a cikin wannan foundation, ya biya buƙatun membobinmu, ya sauƙaƙa mana al’amuran rayuwa, ya kuma sanya mu zama sanadiyyar alheri ga marayu da marasa galihu.

Jazakumullahu Khairan.

Address

Hausa Road
Zaria

Telephone

+2349032649321

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aitaam Foundation posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Aitaam Foundation:

Share