12/02/2026
Kaji da Tsaba
Wata rana, Fir’auna ya shiga taron majalisar hakimansa riƙe da kaza.
Yana matse kazar nan da ƙarfi a ƙarƙashin hammatarsa. Yana cikin tafiya, kan ya ƙarasa kan karagar mulki da aka tanadar masa,sai ya fara fizge gashin kazar ɗaya bayan ɗaya. Kazar ta dinga tsala ihu saboda tsananin azabar da ke tattare da wanna izaya ta raahin imani, tana fafutukar ganin ta kuɓuta daga hannun Fir’auna. Amma Fir’auna bai sake ta ba, kuma bai damu da kukan da take yi ba—ya ci gaba da fizge gashin kawai hankalinsa kwance.
Hak8man da ke zauna a majalisar s**a ce masa: “Ya ya ka ke azabtar da wannan ƙaramar dabba haka? Ka sake ta mana.”
Amma Fir’auna bai saurari kowa ba ɗaha cikinsu, sai ma ya ƙara bayar da himma akan wannan ƙeta da ya ke yi.
Daga ƙarshe, bayan ya gama fizge dukkan gashin kazar, sai ya jefar da ita can gefe a ƙasa. Bayan haka nan, sai kuma ya ciro wasu ƴan ƙwayoyin hatsi a cikin wani adiko na alhariri daga aljihun gefen alkyabbarsa ya fara watsawa kazar a ƙasa. A wannan yanayin, kazar tana jin wata irin matsananciyar yunwa, sai ta fara kallon hannun Fir’auna tana dauraron ƙarar zubar tsabar akan ƙarau dake shinfiɗe a fadar.
Fir’auna ya kirata kusa da shi, yana ƙara watsa mata ɗan hatsin. Bayan ɗan lokaci, sai kazar ta zo ta zauna kusa da shi, tana cin waɗannan ƙwayoyin hatsin da ya zubar a ƙasa. Kazar da ta daɗe tana fafutukar tserewa daga hannun Fir’auna, yanzu kuma ta dawo ta zauna kusa da shi—don kawai ƴan ƙwayoyin hatsi da take son tsattsaga.
Duk hakiman da ke majalisar s**a tambaya cike da mamaki: “Mene ne wannan haka ya Shugaban mu?”
Fir’auna ya amsa musu da cewa: “Kamar yaɓda kuka ga kazar nan, to masu zaɓe ma haka suke. Tsawon shekaru huɗu da rabi, muna fige gashinsu da ransu. Sannan a cikin watanni biyar ko shida na ƙarshe, sai mu fara watsa musu ɗan hatsin da bai taka kara ya karya ba. Saboda wannan ɗan hatsin, masu zaɓe su kan mancewa da duk wani zalunci da muka yi musu a cikin shekaru huɗu da rabi—sai su sake zaɓenmu. Don haka za mu v8gaba da yunwatar da su muna figesu da ransu daga bisani idan lokaci ya karatu sai a kuma watsa musu tsaba. Wannan salo ne namu na gwanayen iya tafiyar da talakawa.”