27/08/2025
Alhamdullah Alhamdullah Alhamdullah
Karin Bayani:
Tun da fari, binciken jaridar Daily Nigerian ya zargi Daraktan Sashen Huldar Fadar Gwamnati, Abdullahi Ibrahim Rogo, da karkatar da kuɗaɗen gwamnati da s**a kai Naira biliyan 6 da miliyan 500 ta hanyar amfani da wasu kamfanoni.
Rahoton ya nuna cewa hukumar ICPC da EFCC sun gano yadda aka juyar da kuɗin tsakanin watan Nuwamba 2023 zuwa Fabrairu 2025, ta hanyar kamfanonin H&M Nigeria Limited, A.Y. Maikifi Petroleum da kuma Ammas Oil and Gas Limited, ta hanyar kwangilolin bogi.
A cewar rahoton, wani ɓangare na kuɗin an chanza su ne zuwa dalar Amurka ta hannun masu canjin kuɗi, sannan aka mika wa Rogo.
Binciken ya kuma bayyana bayanan asusun banki na Rogo, inda aka gano shigar kudi sama da biliyan 3 da miliya 6 a cikin wata shida kacal a asusun sa da ke Alternative Bank. Haka kuma an samu sama da Naira biliyan 2 a asusunsa na Zenith Bank, sai dai naira miliyan 39.3 kacal ce ta rage bayan da bayanan asusun ya nuna an kwashe ragowar kudaden.
Rahoton na Daily Nigerian y ace, tuni wata Babbar Kotun Tarayya dake Kano ƙarƙashin Mai Shari’a M.N. Yunusa ta bayar da umarnin daskarar da asusun da kuma kwace sama da Naira Miliyan 142 da aka tabbatar da karkatar dasu aka yi.
Sai dai a martanin da ta fitar, Gwamnatin Jihar Kano ta musanta dukkanin wannan zarge-zargen.
A cewar kakakin gwamnatin jihar Sanusi Bature Dawakin Tofa, rahoton na Daily Nigerian “An ƙirƙire shi ne da gangan domin bata sunan gwamnati da kuma wasu manyan jami’anta.”
Gwamnatin ta ce babu wata shaida mai inganci da ke tabbatar da badakalar, inda ta kara da cewa hukumar ICPC ko EFCC ba su gurfanar da Ibrahim Rogo a gaban kotu ba, b***e a tabbatar da laifinsa.
Ta bayyana rahoton a matsayin yunkurin siyasa da nufin lalata martabar gwamnatin Abba Kabir Yusuf.
Haka kuma gwamnatin ta yi kira ga mazauna jihar da su yi watsi da rahotannin da ta ce “na bogi” ne, tana mai jaddada cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da gudanar da al’amuran ta cikin gaskiya