21/04/2026
Cikin yarda Allah 20/4/2026, muka Sami damar wannan Empowerment/Awareness na Rabawa Yara 32 kudi da Ruwa leda daddai Masu Tallan Ruwa Amatsayin jari tare da wayar musu da kai a Nguru Yobe State, karkashin Dignity protection team Wanda ya kunsa Abubuwa Kamar Haka👇🏼
1-Muhimmancin Zuwa makaranta(karatu)
2-Wayakamata suna Mu'amala dashi(Tarbiya)
3-Muhimmancin Sana’a(kasuwanci)
Mungudanar da wannan tallafi badan goyan bayan yaran sucigaba da Talla, saidai dan taimokonsu da wasu shawarwari Wanda hakan zaitaimaka musu wajen gujewa fadawa wasu hanyoyi ta Dalilin Tallan.
Wannan jari zai taimakamusu wajen siyan wasu Kayan karatu Wanda mun fada musu cewa karatun yafi mashin manci, Duk da mun Sami yaran da wannan sana'ar suke taimakawa iyayensu agida.
Sannan Daga karshe Ina Mika sakon godeya zuwa ga Members namu dakuma Usman Salisu bisa gudun mawar da yabamu wajen gudanar Da wannan Taro Da kuma Wanda s**a Halakci Wannan taro mai Albarka tare da Addu'a Allah yacigaba da Hada fuskokinmu Aguraren Alkhairi.
Chrm.Adamu Abubakar Adamu Mainasara
Dignity protection team.