15/05/2026
Wlh yanzu ne lkcn da mu Al'ummar Maru ya kamata mu nunawa mutanen nan mun San ciwon kanmu saboda kyale mu da sukayi cikin matsalar tsaro. Sun barmu da kariyar kanmu kullum mu ne fafatawa da yan ta'adda, ba bacci. Sai dai kash matasa da ya kamata mu dauki matakin mune kullum cin mutuncin juna saboda wadannan mutanen. Akwai hanyoyin da ya kamata mubi:
1. Kin fitowa zabe har sai sunyi aikin da ya wajaba garesu akan tsaro
2. Duk dan siyasar da ke kan mulki kuma yake son musake zabensa ya fada muna gudummuwar da ya bamu akan matsalar tsaro da sauran abubuwan cigaba.
3. Duk dan siyasar dake son mu zabesa karo na farko ya fada muna alkawari a rubuce abubuwan da zai muna akan matsalar tsaro da sauran abubuwan cigaba.
Idan ba da wadannan sharuddan ba kowa yayi zamanshi gida ranar zabe.