Northeast Online News 24

Northeast Online News 24 Your North, Your news.

"Stay informed about the latest news and developments from the Northeast region and beyond with Northeast Online News24 - your trusted source for timely and accurate news coverage."

Cikar Dimokuraɗiyya Shekaru 27: Tinubu Ya Yabawa Jaruman 12 gaYuni, Ya Kira 'Yan Najeriya Su Kare DimokuraɗiyyaShugaban ...
12/06/2026

Cikar Dimokuraɗiyya Shekaru 27: Tinubu Ya Yabawa Jaruman 12 gaYuni, Ya Kira 'Yan Najeriya Su Kare Dimokuraɗiyya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga 'yan Najeriya da su ci gaba da kare dimokuraɗiyya tare da ƙarfafa cibiyoyin gwamnati, yana mai cewa ƙasar ta samu mafi tsawon lokacin mulkin farar hula a tarihinta.

A jawabin da ya gabatar domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, Shugaba Tinubu ya ce shekaru 27 da s**a gabata sun nuna cewa Najeriya na iya gudanar da sauye-sauyen mulki cikin lumana ta hanyar zaɓe da bin doka.

Ya kuma yi kira ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), jami'an tsaro da jam'iyyun siyasa da su tabbatar da cewa zaɓukan da za a gudanar a jihohin Ekiti da Osun sun kasance cikin gaskiya da adalci.

Shugaban ya yabawa Majalisar Tarayya, bangaren shari'a, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula bisa rawar da suke takawa wajen kare dimokuraɗiyyar ƙasar.

Tinubu ya kuma yi amfani da damar wajen tunawa da marigayi MKO Abiola, Kudirat Abiola, Shehu Musa Yar'Adua, Gani Fawehinmi da sauran fitattun mutane da s**a taka rawa a gwagwarmayar dawo da mulkin dimokuraɗiyya.

Haka kuma ya sanar da cewa gwamnatin tarayya za ta sauya sunan Cibiyar Nazarin Man Fetur da ke Kaduna zuwa Jami'ar Kimiyyar Kasa da Fasahar Injiniya ta Janar Shehu Musa Yar'Adua domin girmama gudummawar marigayin.

Shugaban ya kuma bayyana sunayen wasu fitattun 'yan gwagwarmayar dimokuraɗiyya da sojojin da s**a mara wa gwagwarmayar baya waɗanda za a karrama da lambobin yabo na ƙasa.

Tinubu Ya Ware Naira Tiriliyan 5.41 Don Tsaro, Ya Amince da Ɗaukar Sabbin Jami'an Tsaro Sama da 50,000Shugaban Ƙasa Bola...
12/06/2026

Tinubu Ya Ware Naira Tiriliyan 5.41 Don Tsaro, Ya Amince da Ɗaukar Sabbin Jami'an Tsaro Sama da 50,000

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da s**a dace domin kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro a Najeriya.

A jawabinsa na Ranar Dimokuraɗiyya, shugaban ya bayyana cewa gwamnatin ta ayyana dokar ta-baci a bangaren tsaro tare da amincewa da ɗaukar sabbin jami'an 'yan sanda sama da 50,000 da kuma dubban sababbin sojoji.

Ya ce kasafin kuɗin shekarar 2026 ya ware Naira tiriliyan 5.41 domin tsaro, wanda shi ne mafi girma da aka taba warewa wannan bangare a tarihin ƙasar.

Tinubu ya ce sojojin Najeriya sun samu gagarumar nasara a yaƙi da ta'addanci, inda ya bayyana cewa an lalata wani babban sansanin kungiyar ISWAP a yankin Arege na Jihar Borno.

A cewarsa, yawan mutanen da ake kashewa sakamakon ta'addanci ya ragu da kashi 81 cikin ɗari idan aka kwatanta da shekarar 2015, yayin da sama da 'yan ta'adda 13,000 s**a mutu a cikin shekara guda.

Sai dai shugaban ya ce har yanzu gwamnati tana bai wa masu son mika wuya dama ta hanyar shirin Operation Safe Corridor, inda ya ce sama da mutane 124,000 daga cikin mayaƙa da iyalansu s**a ajiye makamansu tun daga shekarar 2023.

Ya kuma gargadi 'yan bindiga, masu garkuwa da mutane da masu ɗaukar nauyin ta'addanci da su mika wuya ko kuma su fuskanci cikakken ƙarfin gwamnatin Najeriya.

SAKON SHUGABA BOLA AHMED TINUBU A RANAR DIMOKURAƊIYYA TA 12 GA YUNI, 2026'Yan uwana ’yan Najeriya,A yau muna bikin dimok...
12/06/2026

SAKON SHUGABA BOLA AHMED TINUBU A RANAR DIMOKURAƊIYYA TA 12 GA YUNI, 2026

'Yan uwana ’yan Najeriya,

A yau muna bikin dimokuraɗiyya da kuma juriyar ruhin ɗan Najeriya. Tsawon shekaru 27 a jere tun daga ranar 29 ga Mayu, 1999, al’ummarmu ta ci gaba da zaɓar shugabanninta ta hanyar akwatin zaɓe, tana ganin sauyin mulki cikin lumana, tare da warware sabani a kotuna da majalisun dokoki maimakon ta hanyar tashin hankali.

Dimokuraɗiyyarmu ba cikakkiya ba ce, amma tamu ce. Don haka wajibi ne mu ci gaba da kare ta tare da ƙarfafa ta.

A kwanaki masu zuwa, jihohin Ekiti da Osun za su gudanar da zaɓe. Ina kira ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), jami’an tsaro da dukkan masu ruwa da tsaki su tabbatar da cewa an gudanar da waɗannan zaɓuka cikin lumana da gaskiya. Dimokuraɗiyya tana raunana idan jama'a s**a rasa amincewa da tsarin zaɓe.

Ga Majalisar Tarayya, Bangaren Shari’a, ’Yan Jarida da Kungiyoyin Farar Hula: ku ne ginshiƙan da ke kare jamhuriyarmu. Ku ci gaba da s**ar gwamnati idan ya dace, ku yi sabani da ni idan kuna da hujja, amma kada ku daina yarda da Najeriya.

Ga matasanmu, Najeriya ita ce gidanku kuma makomarku. Ku gina ta a nan, ku kirkiri sababbin fasahohi a nan, ku yi aiki a nan, ku kuma kada kuri’a a nan. Manyan ƙasashe ba su samu ci gaba ba saboda mutanen da s**a gudu daga matsaloli, sai dai saboda waɗanda s**a tsaya s**a warware su.

Ina miƙa gaisuwa ta musamman ga dakarunmu, jami’an ’yan sanda da jami’an tsaro saboda sadaukarwar da suke yi. Haka kuma ina godiya ga sarakunan gargajiya, malamai da shugabannin al’umma saboda rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya da sulhu.

A yau muna tunawa da juriyar ’yan Najeriya da s**a ƙi yin kasa a gwiwa wajen kare ’yanci da dimokuraɗiyya. Muna girmama waɗanda s**a fuskanci tsangwama, kurkuku, gudun hijira har ma da rasa rayukansu domin al’ummomin gaba su more dimokuraɗiyya.

Muna kuma tunawa da shugabannin ƙwadago, ’yan jarida, masu fafutuka, ɗalibai, mata, ƙwararru, shugabannin siyasa da sojoji da s**a taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da dimokuraɗiyya a ƙasarmu.

Duk da cewa wannan shekarar ta zo da alhini sakamakon sace yaranmu a jihohin Oyo da Borno, muna ci gaba da addu’ar dawowarsu lafiya. Domin dimokuraɗiyya ba za ta yi ƙarfi ba idan babu tsaro.

Saboda haka gwamnatinmu ta ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro tare da amincewa da lɗaukar sabbin jami’an ’yan sanda sama da 50,000 da kuma dubban sababbin sojoji. Kasafin kuɗin shekarar 2026 ya ware Naira tiriliyan 5.41 domin tsaro, mafi girma a tarihin Najeriya.

Mun ci gaba daga matakin horaswa tare da ƙasashen abokan hulɗarmu kamar Amurka da Faransa zuwa matakin kai farmaki daidai kan wuraren da ’yan ta’adda suke. A yankin Arege da ke Jihar Borno, mun lalata babban sansanin jagorancin ISWAP.

Yawan mutanen da ake kashewa sakamakon ta’addanci ya ragu da kashi 81 cikin ɗari idan aka kwatanta da shekarar 2015. Fiye da ’yan ta’adda 13,000 aka kawar a cikin shekara guda da ta gabata.

Sai dai har yanzu muna buɗe ƙofa ga waɗanda s**a yanke shawarar mika wuya. Tun daga shekarar 2023, sama da mutane 124,000 daga cikin mayaƙa da iyalansu sun ajiye makamansu ta hanyar shirin Operation Safe Corridor.

Ga ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da masu ɗaukar nauyin ta’addanci: ku mika wuya ko ku fuskanci cikakken ƙarfin gwamnatin Najeriya. Wannan damar ba za ta kasance a buɗe har abada ba.

A irin wannan lokaci, bai kamata mu riƙa ɗora laifi kan wata ƙabila ko wani yanki ba. Laifi ba shi da ƙabila. Dole ne mu kasance a haɗe domin makiyan Najeriya za su zama tarihi nan ba da jimawa ba.

Ranar 12 ga Yuni tana da matsayi na musamman a tarihin ƙasarmu. Ba wai kawai ranar zaɓe ba ce, rana ce da ta nuna yiwuwar gina Najeriya guda ɗaya.

Muna tunawa da Marigayi Cif M.K.O. Abiola wanda ya samu karɓuwa daga kowane sashe na Najeriya ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba. Muna kuma tunawa da Marigayiya Kudirat Abiola da sauran jaruman dimokuraɗiyya.

Muna tunawa da Gani Fawehinmi, Bola Ige, Alfred Rewane, Abraham Adesanya, Anthony Enahoro, Balarabe Musa, Dan Suleiman, Beko Ransome-Kuti, Frank Kokori, Arthur Nwankwo, Chima Ubani, Shehu Musa Yar’Adua da sauran jarumai maza da mata da s**a sadaukar da kansu domin tabbatar da ’yancin da muke morewa a yau.

Jaruman 12 ga watan Yuni sun samar mana da ’yancin siyasa. Nauyin da ke kanmu yanzu shi ne samar da ’yancin tattalin arziki.

Dimokuraɗiyya dole ne ta bayyana a rayuwar jama'a, a damar da matasa ke samu, a bunƙasar noma, a ci gaban ’yan kasuwa da kuma mutuncin ma’aikata.

Gyaran tattalin arzikin da muka fara bai kasance domin sauƙi ba, sai dai domin ya zama wajibi.

Tun daga shekarar 2023, waɗannan gyare-gyare sun dawo da kwanciyar hankali ga tattalin arzikin ƙasa. Kuɗaɗen shiga na gwamnati sun ƙaru, an rage almundahana, an ƙara gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen jama'a, kuma amincewar masu zuba jari ta dawo.

Zuba jari ya ƙaru a fannoni kamar noma, makamashi, masana’antu, fasaha, ma’adinai, sufuri da masana’antun kirkira.

Haka kuma ƙarfin tace mai a cikin gida ya ƙaru, wanda ke taimakawa wajen ƙarfafa tsaron makamashi da rage dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje.

Lokacin da muka hau mulki, bangaren wutar lantarki na fama da matsaloli masu yawa. Don magance wannan matsala, na rattaba hannu kan Dokar Wutar Lantarki da ta bai wa jihohi damar samarwa, rabawa da kuma sarrafa wutar lantarki.

Hukumar Kula da Samar da Wutar Lantarki ta Ƙasa tana aiki don rage matsalar rashin mita, tare da shirin tara Naira tiriliyan 4 domin biyan tsofaffin basuss**a a bangaren.

A yankunan karkara, an samar da wutar lantarki ta hanyar mini-grid da sauran hanyoyi domin hidimta wa al’ummomi, jami’o’i, kasuwanni da asibitoci.

Domin wutar lantarki hakki ne da ya kamata kowane ɗan Najeriya ya mora.

Duk da nasarorin da aka samu, har yanzu muna sane da cewa ’yan Najeriya da dama suna fuskantar matsin rayuwa.

Saboda haka muna mai da hankali wajen rage hauhawar farashi, ƙara samar da abinci, samar da ayyukan yi, da inganta rayuwar jama'a.

Mun fara fita daga yanayin rashin tabbas zuwa kwanciyar hankali. Mataki na gaba shi ne hanzarta ci gaba tare da tabbatar da cewa kowane gida, kowace al’umma da kowane yanki ya amfana da shi.

Domin dimokuraɗiyya dole ne ta bayyana a aljihun jama'a.

Domin tabbatar da cewa jama'a suna jin tasirin dimokuraɗiyya kai tsaye, gwamnatinmu ta himmatu wajen tabbatar da cikakken ’yancin cin gashin kan ƙananan hukumomi 774 na ƙasar nan.

Matsalolin rashin tsaro da wasu kalubalen ci gaba sun samo asali ne daga rushewar tsarin mulki a matakin ƙasa. Saboda haka Ajandar Sabunta Fata tana nufin tabbatar da cewa kowane ɗan Najeriya ya amfana da gwamnati.

Muna girmama Marigayi Janar Shehu Musa Yar’Adua saboda hangen nesa da gudummawar da ya bayar wajen gina Najeriya mai haɗin kai.

A saboda haka, gwamnatin tarayya ta amince da sauya sunan Cibiyar Nazarin Man Fetur da ke Kaduna zuwa Jami’ar Kimiyyar Kasa da Fasahar Injiniya ta Janar Shehu Musa Yar’Adua.

Haka kuma na amince da karrama wasu fitattun ’yan Najeriya da s**a fuskanci tsangwama, kurkuku, gudun hijira da wahalhalu domin kare dimokuraɗiyya da s**a hada da;

Barista Ayoka Lawani
Tunde Fagbenle
Oladele Alake
Olatunji Bello
Louis Odion
Segun Babatope
Sam Omatseye
Sir Ademola Osinubi
Bola Bolawole
Lade Bonuola
Femi Kusa
Debo Adeniran
Cif Ayo Opadokun
Cif Ralph Obiora
Ose Osayande
Barista Osa Director
Farfesa Sylvester Odion-Akhaine
Marigayi Dakta Arthur Nwankwo
Dakta Osagie Obayuwana
Dakta Joe Okei-Odumakin
Barista Titus Mann
Joe Igbokwe
Richard Akinnola
Marigayi Ben Charles-Obi
George Mbah
Dakta Niran Malaolu
Manjo Janar Ishola Williams (Mai Ritaya)
Femi Aborisade
Jenkins Alumona
Gbemiga Ogunleye
Muyiwa Adekeye
Babajide Kolade-Otitoju
Ike Okonta

Haka Kuma Muna Girmama Sojojin Da S**a Taka Rawa A Gwagwarmayar 12 ga Yuni da s**a hada da;

Manjo Janar M. A. Garba
Birgediya Janar Lawal Ja’afaru Isa
Kanal Umar Farouk Ahmed
Kanal Sambo Dasuki
Kanal Lawan Gwadabe
Birgediya Janar Jonathan Ndam Temlong
Kanal Musa Shehu
Manjo Janar Chris Eze
Manjo Janar Harris Dzarma
Kanal Isa Jibrin
Manjo Janar Joseph Oshanupin
Kanal Olusegun Oloruntoba, Olugbede na Masarautar Gbede
Laftanar Kanal Happy Kefas Bulus
Kanal J. Okai
Kanal Emmanuel Ndubueze
Laftanar Kanal Yakubu Mu’azu
Birgediya Yahaya Abubakar, Etsu Nupe na yanzu, wanda tuni yake da lambar yabon ƙasa ta CFR.

Za a fitar da cikakken jerin sunayen waɗanda za a karrama tare da lambobin yabon ƙasa da za a ba su a cikin kwanaki masu zuwa.

’Yan uwana ’yan Najeriya,

Shekaru 27 da s**a gabata, mutane da yawa sun yi shakku cewa dimokuraɗiyya za ta dawwama a Najeriya saboda bambance-bambancenmu.

A yau kuwa, waɗannan bambance-bambancen ne suke ƙarfafa dimokuraɗiyyarmu.

Hanyar gaba ba mai sauƙi ba ce. Amma 12 ga Yuni tana tunatar da mu cewa ’yan Najeriya ba sa karyewa. Za mu iya lanƙwasawa, za mu iya zubar da jini, amma ba za mu rushe ba.

Mu sabunta alkawarinmu cewa wahalhalun jarumanmu na baya ba za su tafi a banza ba, kuma mulkin jama'a, na jama'a kuma domin jama'a ba zai gushe daga wannan ƙasa ba.

Allah Ya albarkaci jaruman dimokuraɗiyyarmu.

Allah Ya albarkaci Tarayyar Najeriya.

Allah Ya ci gaba da albarkatar mu baki ɗaya.

Barka da Ranar Dimokuraɗiyya.

BOLA AHMED TINUBU, GCFR
Shugaban Ƙasa kuma Babban Kwamandan Rundunar Sojojin Tarayyar Najeriya.

Manufofin Gwamnatin Tinubu na Tare da Matasan NajeriyaMataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa ...
11/06/2026

Manufofin Gwamnatin Tinubu na Tare da Matasan Najeriya

Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa shirye-shirye da manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu an shirya suna ta yadda za su mori matasan Najeriya, saboda gwwmnati na amfani da sabbin dabaru wajen magance matsalolin zamani na wannan karni na 21.

Ya yi wannan bayani ne yayin ganawa da shugabannin kungiyar City Boy Movement a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, inda ya jaddada cewa gwamnati na daukar matasa a matsayin ginshikin ci gaban kasa da kuma makomar dimokuradiyya.

Shettima ya ce gwamnatin Tinubu na daukar matakai masu wahala amma masu muhimmanci don farfado da tattalin arziki da kuma tabbatar da ci gaba mai dorewa, yana mai cewa nasarar gyare-gyare na bukatar hakuri, jajircewa da goyon bayan ‘yan kasa.

Ya kuma bayyana cewa dimokuradiyya ba ta tsaya kan zabe kadai ba, tana bukatar shigar jama’a da kuma hadin kai wajen kare manufofin da ke kawo ci gaba ga kasa.

Mataimakin Shugaban Kasa ya yabawa kungiyar City Boy Movement bisa kokarinta na wayar da kan jama’a da kuma karfafa goyon bayan gwamnati, yana mai jaddada muhimmancin ladabi, amana da hadin kai a siyasa da shugabanci.

Kungiyar wadda Hon. Francis Oluwatosin Shoga, ke jagaranta ta yi alkawarin ci gaba da zagayawa fadin Najeriya domin tattara goyon baya ga sake zaben Shugaba Tinubu a shekarar 2027.

Gwamnatin Tarayya ta ba da hutu ranar Juma’a domin bikin shekaru 27 na cigaban dimokiraɗiyya ba tare da katsewa baGwamna...
11/06/2026

Gwamnatin Tarayya ta ba da hutu ranar Juma’a domin bikin shekaru 27 na cigaban dimokiraɗiyya ba tare da katsewa ba

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata domin bikin cika shekaru 27 da Nijeriya take gudanar da mulkin dimokiraɗiyya ba tare da katsewa ba.

Babbar Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, ita ta bayyana haka cikin takardar manema labarai da ta rattaba wa hannu a ranar Alhamis a Abuja.

Ajani ta ce Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya ba da sanarwar hutun a madadin Gwamnatin Tarayya.

Tunji-Ojo ya sake jaddada aniyar gwamnati na kare da kuma bunƙasa ƙa’idojin dimokiraɗiyya, ciki har da bin doka da oda, gaskiya da riƙon amana, ɗaukar nauyi, da kuma shugabanci mai haɗa kowa da kowa.

Ya tabbatar da cewa Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro da abin ya shafa, za su ci gaba da ɗaukar matakan da s**a dace domin tabbatar da tsaro da kuma ƙarfafa zaman lafiyar cikin gida a Nijeriya.

Ministan ya bayyana cewa samun yanayi mai cike da tsaro da kwanciyar hankali yana da matuƙar muhimmanci domin dimokiraɗiyya ta bunƙasa tare da tabbatar da cigaban ƙasa mai ɗorewa.

Ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan ranar hutun wajen yin nazari kan matsayin su na ‘yan ƙasa tare da sabunta jajircewar su wajen kare kyawawan ɗabi’u da ƙimomin ƙasa.

Ya ce, “Yayin da muke bikin wannan rana mai tarihi, muna kira ga kowane ɗan Nijeriya da ya kasance mai bin doka, ya mutunta cibiyoyin da ke ɗorewar dimokiraɗiyyar mu, tare da tuna cewa ƙarfin kowace dimokiraɗiyya yana ta’allaƙa ne ga halaye da ɗabi’un ‘yan ƙasar ta.”

Tunji-Ojo ya ƙara da cewa ranar 12 ga Yuni tana da muhimmin matsayi a tarihin Nijeriya, domin tana girmama jarumtaka, juriya da sadaukarwar waɗanda s**a bayar da gudunmawa wajen kafa mulkin dimokiraɗiyya a ƙasar nan.

“Har yanzu abin da muka gada daga gare su yana ci gaba da zama abin koyi wajen tsara ƙimomi da nauyin da ya rataya a wuyan ƙasar Nijeriya,” inji shi.

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci k...
10/06/2026

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci kusan dazukan anan da dama wuraren kiyon dabbobi ne. To, bayan da aka kirkiri Abuja, an tanadi wurare da aka tsara jama'a za su zauna, tare da wuraren ofisoshi da wuraren gina kasuwanni da sauran wuraren more rayuwa, amma aka manta a keɓe tare da inganta inda dabbobi za su yi kiwo.

Akwai gandun daji guda huɗu da faɗin su ya kai hekta 33 a Abuja da aka ware tun da, sannan tun da aka ware waɗannan gandun dajin a wancan lokacin da aka kirkiri Abuja, ba a taɓa yin wani abu na inganta wurin ta yadda za a maida makiyaya wurin ba.

Tun bayan kafa ma’aikatar kula da bunƙasa kiyon dabbobi kusan shekara biyu da s**a wuce, ma’aikatar ta kulla alaƙa tare da Hukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya ta yadda za a inganta waɗannan wurare da ke yankunan ƙauyen Kau, Karshi da sauran wurare da ke Abuja.

Muna aiki tare da masu ruwa da tsaki wajen inganta waɗannan gandun dajin, sannan a duba yiwuwar maida makiyaya wurin sannu a hankali."

— Idi Muktar Maiha, Ministan Bunƙasa Kiyon Dabbobi, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai na Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026 da aka gudanar a ranar Talata, 9 ga Yuni, 2026.

An Bayyana Babban Sauyin da aka samu a Abuja, Inda aka Sanar da Kammala Ayyuka Wanda  Za'a  Fara Kaddamarwa Daga Sati Ma...
10/06/2026

An Bayyana Babban Sauyin da aka samu a Abuja, Inda aka Sanar da Kammala Ayyuka Wanda Za'a Fara Kaddamarwa Daga Sati Mai Zuwa Don Bikin Cika Shekaru 3 da Tinubu Yayi Akan Mulki

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa manyan ayyukan gine-gine da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar a Abuja sun kammala kuma sun shirya domin kaddamarwa, yayin da ake shirin bikin cika shekaru uku na mulkinsa.

Wike ya bayyana hakan ne yayin duba wasu muhimman ayyuka a Abuja, inda ya ce gwamnatin Tinubu ta nuna ƙudirin gaske wajen sauya fasalin babban birnin ƙasa ta hanyar inganta hanyoyi, gadoji da sauran ababen more rayuwa.

A cewarsa, dukkanin ayyukan da aka duba sun kai matakin kammalawa da ya kai kashi 100 cikin 100, yana mai cewa hakan hujja ce ta cewa an kawo ci gaba mai ma’ana ga al’umma.

Daga cikin ayyukan da aka duba akwai gadar Jahi–Gwarimpa, hanyar filin jirgin sama zuwa Kuje, hanyar Kuje zuwa Gwagwalada, titunan Outer Southern Expressway, da kuma gyaran ƙofar shiga birnin Abuja (Abuja City Gate).

Wike ya bayyana jin daɗinsa kan ingancin aikin da kamfanonin kwangila s**a yi, inda ya ce ayyukan za su inganta zirga-zirga tare da rage cunkoso da wahalar tafiya a birnin Abuja da kewayenta.

Ya ce musamman hanyoyin Airport zuwa Kuje da Kuje zuwa Gwagwalada sun rage tsawon lokacin tafiya tsakanin birni da yankunan da ke kewayen Abuja, abin da ya ce ya inganta rayuwar mazauna sosai.

Ministan ya kuma yaba da gyaran da aka yi wa Abuja City Gate, yana mai cewa hakan zai ƙara wa birnin Abuja martaba a idon duniya a matsayin babban birni na zamani.

Ya ƙara da cewa ana shirin fara kaddamar da ayyukan a mako mai zuwa, inda ya ce shugabannin gwamnati daban-daban za su wakilci Shugaba Tinubu wajen buɗe wasu daga cikin ayyukan.

Wike ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su taimaka wajen bayyana irin ci gaban da ake samu a FCT, yana mai cewa abin da ake yi a Abuja yana nuna yadda gwamnati ke kawo sauyi ga rayuwar al’umma.

A cewarsa, an kuma shirya fara wasu sabbin ayyukan hanyoyi a nan gaba domin ci gaba da bunƙasa ababen more rayuwa a babban birnin tarayya.

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Kan Ebola, Ya Amince da Naira Biliyan 10 Don Shirin Bada KariyaShugaban Bola Ahm...
09/06/2026

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Kan Ebola, Ya Amince da Naira Biliyan 10 Don Shirin Bada Kariya

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa Kwamitin Musamman na Fadar Shugaban Ƙasa kan Shirin Kariya daga Cutar Ebola da Sauran Barazanar Lafiyar Jama’a, tare da bayar da umarnin sakin naira biliyan 10 domin shirye-shiryen gaggawa.

A cewar sanarwar da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, kuɗaɗen za su taimaka wajen ƙarfafa shirye-shiryen Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Ƙasa (NCDC) da kuma ayyukan da s**a shafi tunkarar duk wata barazanar gaggawa ga lafiyar al’umma.

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne zai jagoranci sabon kwamitin, wanda zai haɗa da wakilai daga ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati daban-daban, da kuma wakilan jihohi.

Matakin ya biyo bayan sake bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da kuma Uganda.

Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa ya jagoranta domin nazarin irin shirin da Najeriya ta yi da kuma dabarun da za su hana cutar shiga ƙasar.

Daga cikin mahalarta taron akwai wakilai daga Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN), Hukumar Shige da Fice (NIS), Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (NCAA), da gwamnatin jihar Legas.

Shugaban ƙasar ya kuma umarci dukkan jihohin da ke da filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa da kuma manyan hanyoyin shiga ƙasar daga ƙasashen waje da su gabatar da tsare-tsarensu, buƙatun kuɗi da irin tallafin da suke buƙata domin aiwatar da matakan kariya cikin haɗin gwiwa.

A cikin matakan da aka sanar za a ɗauka akwai ƙara tsaurara binciken fasinjoji a dukkan filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa, ciki har da duba zafin jiki da tsara yadda jama’a ke shiga da fita.

Haka kuma za a ƙarfafa sa ido kan fasinjojin da ke shigowa ta wasu hanyoyin jiragen sama da gwamnati ta ayyana a matsayin masu haɗari, ciki har da Air Uganda, RwandAir, Air Tanzania, Air Angola, Kenya Airways da Ethiopian Airlines.

Gwamnatin ta ce za a gaggauta bude cibiyoyin killace marasa lafiya da wuraren tura waɗanda ake zargin sun kamu da cutar a filayen jiragen saman Legas da Abuja, kafin daga baya a faɗaɗa tsarin zuwa sauran filayen jiragen saman ƙasar.

Sauran matakan sun haɗa da wajabta cike bayanan lafiyar matafiya ta hanyar tsarin QR Code kafin su iso ƙasar idan sun fito ko s**a bi ta ƙasashen da aka ayyana masu haɗari, da kuma tsaftace dakunan tashi da saukar jirage, wuraren kaya da sauran sassan filayen jiragen sama.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci kwamitin da ya tattauna da hukumomin tsaro, diflomasiyya da sufurin jiragen sama kan yiwuwar ɗaukar ƙarin matakan da s**a shafi zirga-zirgar jirage daga ƙasashen da cutar ta bulla ko waɗanda aka sanya cikin jerin masu haɗari.

Bugu da ƙari, kwamitin zai duba yiwuwar ware wasu filayen jiragen sama ko tashoshi na musamman domin karɓar jiragen da ake ganin suna da haɗari, tare da nazarin sauya lokutan saukar wasu jirage domin rage haɗuwar fasinjojin da ake sa ran za su buƙaci ƙarin bincike da sauran matafiya.

Labari Cikin Hoto:Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwam...
06/06/2026

Labari Cikin Hoto:

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwamnan Jihar Kwara, Malam AbdulRahman AbdulRazaq; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris; tsohon Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari, tare da sauran manyan baƙi suna daga cikin fitattun mutanen da s**a halarci sallar Juma’a ta musamman da aka gudanar domin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana. An gudanar da wannan zaman addu’a ne a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, 2026, a Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kan jama’a da hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanciGwamnatin Tarayya ta yi kira ga ...
05/06/2026

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kan jama’a da hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ’yan Nijeriya da kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tsaro da su ƙarfafa haɗin gwiwa a tsakanin su wajen yaƙi da ta’addanci da sauran nau’o’in tsauraran ra’ayoyi da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja a wajen wani babban taron manema labarai.

Ya ce yaƙi da ta’addanci yana buƙatar haɗin kan ƙasa baki ɗaya ba tare da la’akari da bambance-bambancen siyasa da ƙabila da addini ko yanki ba.

Ministan ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana kira ga ’yan ƙasa da kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci, domin duk wani hari da aka kai wa ɗan Nijeriya ɗaya tamkar an kai shi ne ga dukkan ’yan Nijeriya. Ta’addanci ba ya da ƙabila ko addini ko wata alaƙa da siyasa. Manufar sa ita ce haddasa ɓarna kawai.”

Ya bayyana cewa wannan ne ya haifar da ƙaddamar da gangamin , wanda ke kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci da sauran laifuffuka.

Idris ya kuma tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da ƙoƙarin ganin an ceto dukkan ɗalibai da malamai da aka sace a hare-haren da s**a faru a jihohin Oyo da Borno.

Ya ce: “Ina so in tabbatar wa da dukkan ’yan Nijeriya cewa dawo da kowane yaro da kowane malami da ke hannun masu garkuwa cikin ƙoshin lafiya yana ci gaba da kasancewa babban fifikon gwamnati. Shugaban Ƙasa ya bayyana ƙarara cewa babu wani yaro da ya kamata ya kasance a tsare, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa an gurfanar da masu hannu a waɗannan munanan laifuffuka a gaban shari’a.”

Ministan ya bayyana cewa hukumomin tsaro sun ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da gudanar da sintiri da kuma ayyukan ceto domin kuɓutar da waɗanda aka sace tare da hukunta masu hannu a lamarin.

Ya ce dakarun rundunar "Operation Hadin Kai" sun samu nasarori a Arewa-maso-gabas, inda s**a kashe 'yan ta’adda da dama tare da lalata sansanonin su da kuma ceto fararen hula.

A cewar sa, ayyukan tsaro a yankunan Arewa-maso-yamma da Arewa-ta-tsakiya da Kudu-maso-gabas da Kudu-maso-kudu sun taimaka wajen rusa sansanonin masu aikata laifi da tarwatsa ƙungiyoyin masu garkuwa da mutane da kuma ƙara kare muhimman kadarorin ƙasa.

Idris ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ta’addanci suna da alaƙa da ingantaccen haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da musayar bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da kuma haɗin gwiwa da ƙasashen waje.

Ya ce: “Abin da ya bambanta wannan tsarin da muke amfani da shi a yanzu shi ne haɗa matakan soji da ayyukan da s**a dogara da bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da haɗin gwiwa tsakanin yankuna da kuma sa hannun al’umma. Wannan cikakken tsari yana ci gaba da raunana ƙarfin ƙungiyoyin ’yan ta’adda da masu aikata laifuffuka.”

Ministan ya kuma yi nuni da nasarorin da aka samu a ɓangaren shari’a, ciki har da hukuncin da aka yanke wa waɗanda aka samu da hannu a harin ta’addancin da aka kai Cocin St. Francis da ke Owo a Jihar Ondo a watan Yuni 2022.

Ya ce Gwamnatin Tarayya ta kuma fara ɗaya daga cikin manyan shari’un masu laifin ta’addanci a tarihin ƙasar nan, inda ɗaruruwan waɗanda ake zargi suke fuskantar shari’a.

Ya ce: "Adalci yana daga cikin muhimman ginshiƙan tsaron ƙasa. Bayan matakan soji, gwamnati tana tabbatar da cewa duk masu hannu a ayyukan ta’addanci sun fuskanci hukuncin doka. Shari’un da ake yi wa waɗanda ake zargi da ta’addanci da kuma hukuncin da aka yanke wa wasu daga cikin su na aika saƙo ƙarara cewa ba za a ƙyale masu laifi su tsira daga hukunci ba.”

Ministan ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da bin ƙa’idojin aikin jarida wajen rahoto kan al’amuran ta’addanci.

Ya ce: “Yayin da ya kamata kafafen yaɗa labarai su ci gaba da bayar da rahotanni cikin sahihanci da nuna ƙwarewa, dole ne mu yi taka-tsantsan kada mu taimaka wa ’yan ta’adda wajen cimma manufofin su ba tare da sani ba. Aikin jarida mai ɗa’a na iya hana su samun irin shaharar da suke nema, tare da tabbatar da cewa jama’a sun samu sahihan bayanai.”

Ya buƙaci ’yan Nijeriya da su kasance masu sa ido tare da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai, sannan su guji yaɗa duk wani saƙo da ke ƙoƙarin haddasa rarrabuwar kai ta fuskar ƙabila ko addini ko siyasa.

Ministan ya sake jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a har sai an kawo ƙarshen ta’addanci da sauran munanan laifuffuka.

“Nijeriya ta sha fuskantar lokuta masu wuya a baya kuma ta fito daga cikin su da ƙarfin ta. Haka nan za mu shawo kan wannan ƙalubale. Idan muka haɗa kai tare da tsayawa tsayin daka kan manufar mu, za mu tabbatar da cewa ta’addanci ba shi da makoma a Nijeriya."

Taron ya samu halartar Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire; Sufeto-Janar na ’Yan Sanda wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya wakilta; Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, Janar Sama'ila Uba, da wasu manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki a lamarin.

Address

Maiduguri

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Northeast Online News 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share