HQ Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command

HQ Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from HQ Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command, Community Organization, Katsina.

10/06/2026

CUTUTTUKAN ZUCIYA DA MAGANIN SU - Episode 3

Wannan shiri ne na wa'azi, tarbiyya, gyaran zuciya da ilmantarwa, ga jami'an Hisbah da kuma al'umma baki ɗaya, kan muhimmin sha'anin Abinda ya Shafi gyara da tsarkake Zuciya.

Mai Gabatarwa:
Sheikh Alkali Bilyaminu Muhammad Balarabe [Hafizahullah]

Commander General – Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command,
Shugaban Majalisar Malamai Na Jibwis, a Ƙaramar Hukumar Katsina.

Ku yi Following, Liking, Comments da Sharing, domin ’yan uwa al'umma su amfana, sakon kuma ya isa ga kowa.

✍️ Maaruf Ahmad
Asst. Director, ICT HQ Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command

Yanzu da muke da rayuwa, yanzu ne muke da damar gyara halayenmu. Mukoma ga Allah kafin lokaci ya ƙure mana. Allah ka yaf...
09/06/2026

Yanzu da muke da rayuwa, yanzu ne muke da damar gyara halayenmu. Mukoma ga Allah kafin lokaci ya ƙure mana. Allah ka yafe mana. 🤲🥹

07/06/2026

GUZURI ZUWA GA ƊAN HISBAH - Cigaban Episode 11

Aikin Hisbah a zamanin Sayyidna Uthman ibn Affan (RA)

Wannan Shiri ne na wa’azi, tarbiyya da ilmantarwa ga jami’an Hisbah da kuma al'umma baki ɗaya.

Wanda Marigayi Sheikh Dr. Army Shehu Ladan (Rahimahullah) ya gabatar a lokacin rayuwarsa.

Marigayi Sheikh Dr. Army Shehu Ladan shi ne Divisional Commandant na Malumfashi, kuma Shine
State Amirud-Da’awah na Lajnatul Hisbah Association of Nigeria, Katsina State Command.

Muna addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa,
Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa.

Allah Ya ba iyalai, almajirai da dukkan masu alaka da shi
haƙurin jure wannan babban rashi.

✍️ Maaruf Ahmad
Assistant Director ICT HQ Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command

👉 Ku yi Following, Liking da Sharing, domin ‘yan uwa da al’umma su amfana,
kuma saƙon ya isa ga kowa.

ZIKIRI (Ambaton ALLAH) yana haifar da samuwar yabo daga ALLAH da kuma mala'iku ga mai yinsa, ALLAH yana alfahari da masu...
04/06/2026

ZIKIRI (Ambaton ALLAH) yana haifar da samuwar yabo daga ALLAH da kuma mala'iku ga mai yinsa, ALLAH yana alfahari da masu ambaton Sa.

Yana da kyau a kullum ka kwana da wannan tunani kai matafiyi ne a duniya, kuma ka zo ne domin neman guzuri ta hanyar bau...
03/06/2026

Yana da kyau a kullum ka kwana da wannan tunani kai matafiyi ne a duniya, kuma ka zo ne domin neman guzuri ta hanyar bautawa Ubangijinka Allah, domin samun tsira a Ranar Sakamako.

28/05/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Bilal Maikudi Murtala, Abu Hamnat, Engr Aminu Inuwa Gaya, Umar D Musa, Souleyman Ibn Alhaji Illiassou, Waliyyi Abubakar, Abdullahi Adamu, Nura Abdullahi, Muhammad Abdulkareem, Abdurrahman Ibrahim, Abdulallahi Aliyu, Umar Maibasira, Ibrahim Abdullahi Maifada, Mohammed Naseer, Abdulhakim Gambo, Ibrahim Kallil, Alamin Muhmd Assalafi, Abdullahi Lawal, Salman Abubakar Alhaji, Itz Real Sardauna, Sadik Usman

BARKA SALLAH
28/05/2026

BARKA SALLAH

Happy Eid El Kabir 2026
28/05/2026

Happy Eid El Kabir 2026

Takabbalallahu minna wa minkum
27/05/2026

Takabbalallahu minna wa minkum

Lajnatul Hisba Ta Ƙara wa Jami’anta Kusan 30 Girma a KatsinaShugaban Hisba Ya Tunatar da Falalar Azumin Ranar Arfah, hak...
26/05/2026

Lajnatul Hisba Ta Ƙara wa Jami’anta Kusan 30 Girma a Katsina

Shugaban Hisba Ya Tunatar da Falalar Azumin Ranar Arfah, haka kuma, Ƙungiyar Lajnatul Hisba Association Of Nigeria reshen jihar Katsina ta gudanar da wani gagarumin taro na ƙara wa jami’anta girma, inda aka ɗaukaka kusan jami’ai 30 zuwa manyan muƙamai daban-daban domin ƙarfafa ayyukan hukumar a faɗin jihar.

An gudanar da taron ne ranar Litinin 25 ga watan Mayu 2026 a Masallacin Khandahar da ke cikin birnin Katsina, tare da halartar ɗimbin jama’a da s**a haura mutum 250, ciki har da malamai, shugabannin al’umma, jami’an Hisba da sauran masu ruwa da tsaki.

Shugaban Lajnatul Hisba Association Of Nigeria reshen karamar Hukumar Katsina, DC. Malam Kabir Muhammad Jihadi (Abu Sudais), wanda ya jagoranci taron, ya bayyana cewa ƙara wa jami’an girma na daga cikin hanyoyin ƙarfafa musu guiwa domin su ci gaba da gudanar da ayyukansu cikin gaskiya, riƙon amana da kishin addini.

Ya ce ƙungiyar Hisba na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan al’umma kan kyawawan ɗabi’u, tabbatar da zaman lafiya, da kuma yaƙi da munanan dabi’u a tsakanin matasa da sauran jama’a.

A jawabin nasa, Malam Kabir Muhammad Jihadi ya yi kira ga al’umma musamman matasa da su kasance masu kishin ƙasa da addini, tare da tabbatar da cewa sun zaɓi shugabanni nagari a zaɓen shekarar 2027.

“Ya kamata al’umma su zaɓi mutanen kirki masu gaskiya da riƙon amana, waɗanda za su yi aiki domin cigaban jama’a da ƙasa baki ɗaya,” in ji shi.

Haka kuma, shugaban ya yi kira ga musulmai da su yi amfani da kwanakin ibada wajen neman kusanci ga Allah, musamman ta hanyar azumin ranar Arfah, wanda ya ce yana daga cikin ibadun da ke da falala mai yawa a addinin Musulunci.

Ya tunatar da mahalarta taron muhimmancin haɗin kai da zaman lafiya tsakanin al’umma, yana mai jaddada cewa cigaban kowace al’umma ba zai samu ba sai da haɗin kai da biyayya ga dokoki da koyarwar addini.

Taron ya gudana cikin lumana da nasara, inda mahalarta s**a bayyana jin daɗinsu da irin yadda ƙungiyar Hisba ke ƙoƙarin bunƙasa ayyukanta a jihar Katsina.

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HQ Lajnatul Hisbah Association of Nigeria Katsina State Command posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share