10/03/2026
PRESS RELEASE
SANARWA KAN CI GABAN BINCIKE A KAN KISAN HALIFA (CHURI)
Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuhu.
Ƙungiyar Kabara Community Security, Education & Development Association (KCSEDA)
na sanar da dukkan mambobinta da al’ummar gari halin da ake ciki dangane da binciken da ake gudanarwa kan mummunan lamarin kisan Halifa (Churi) tare da jikkatar wasu daga cikin al’ummar unguwarmu.
Bayan ƙungiyar ta miƙa takardar ƙorafi ga hukumar ‘yan sanda domin a buɗe cikakken bincike kan wannan lamari mai tayar da hankali, muna farin cikin sanar da cewa an fara samun gagarumin ci gaba a binciken.
A ranar 07 ga Maris, 2026, jami’an Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya rashi jahar Kano sun samu nasarar k**a wani wanda ake zargi da hannu a cikin wannan lamari.
A halin yanzu, ana tsare da wanda ake zargin a Sashen Binciken Kisan Kai (Homicide Section) na Bompai Police Headquarters, inda ake ci gaba da gudanar da bincike domin gano dukkan waɗanda ke da hannu a cikin wannan laifi.
Ƙungiyar KCSEDA na yaba wa jami’an tsaro bisa gaggawar da s**a nuna wajen ɗaukar mataki da kuma ƙoƙarin da suke yi na tabbatar da adalci.
Muna kuma tabbatar wa al’umma cewa ƙungiyarmu za ta ci gaba da bibiyar wannan lamari da matuƙar kulawa har sai an tabbatar da cikakken adalci ga marigayi Halifa (Churi) da kuma waɗanda s**a jikkata.
Haka kuma muna kira ga dukkan mambobin ƙungiya da al’ummar yankin da su kasance masu haƙuri, kwanciyar hankali da bin doka, tare da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai domin samun nasarar binciken.
A ƙarshe, muna godewa Allah Maɗaukakin Sarki bisa wannan muhimmin ci gaba, tare da roƙonSa Ya tabbatar da adalci, tsaro da zaman lafiya a cikin al’ummarmu.
Issued by:
Comrade Yahaya Yau Abdullahi
Secretary General
Kabara Community Security, Education & Development Association (KCSEDA)
Date: 08 March 2026