Sabuwar Duniya

Sabuwar Duniya Dedicated to activism. Not affiliated with any person. Sharing quotes, ideas & analysis for awareness and justice. In God we trust.

17/01/2026

Alhamdulillah

Ko dai Æmurka ta Sayi Arewa?Wani ɗan Majalisar Amurka, Riley Moore, ya fito ya ce wai harin da Amurka ta kai a Najeriya ...
27/12/2025

Ko dai Æmurka ta Sayi Arewa?

Wani ɗan Majalisar Amurka, Riley Moore, ya fito ya ce wai harin da Amurka ta kai a Najeriya ya hana kai farmaki kan Kiristoci a lokacin Kirsimeti. A lokaci guda kuma, shugaban Najeriya ya tabbatar da cewa an kai harin ne da amincewar gwamnatinsa.

Abubuwan Lura:

• Meye haɗin Sokoto garin Musulmi da Kirismeti, ko dai suna son su isar da saƙon cewa Musulmin Arewa na kæshë Kiristocin Najeriya?

• Meye haɗin ƙaramar hukumar Jabo a Sokoto da yaƙar ta'addanci, ko dai suna nufin nan ne cibiyar ’yan ta'addan Najeriya?

• Meye haɗin ISIS da ta'addancin da ake fama da shi a Arewa, ko dai bandits (su Bello Turji) suke nema aka samu kuskure?

Idan da gaske manufar ita ce yakar ’yan ta’adda, me ya sa ba a mayar da hankali kan sanannun wuraren da suke fakewa ba, kamar: Dajin Sambisa, Dajin Rugu, Dajin Kamuku, Dajin Kuyan Bana (Sububu), Dajin Birnin Gwari, Dajin Mandara, da Dazuzzukan Lake Chad Basin?

Wannan makirci ne ake shirya wa Arewa, kuma ba ’yan ta'adda suke yaƙa ba; Musulmi suke yaƙa, domin inda suke hari ba cibiyar ta'addanci bane, kuma ba cibiyar Kiristoci bane b***e a ce suna ƙoƙarin kare su, daman suna da agenda ta ganin bayan Musulunci, kuma da yardar Allah ba za su yi nasara ba.

Shugabannin cikin gida da na waje kowa da akwai manufar da yake son cimma wa, kuma har ’yan uwansu Kiristoci ba kaunarsu suke ba; kawai suna wasa da hankalinsu ne, daga ƙarshe wawayen dake jin daɗi da Kirista ma ji daɗinsu; kowa zai gane kurensa in dai ba a gyara ba.

Shin kun taɓa ganin ƙasar da Æmurkæ ta shiga da nufin gyara s**a zauna lafiya?

Abin da ya faru a Sokoto ya kamata kowa ya tsaya ya yi tunani mai zurfi. Idan har manufar Æmurka ita ce kawo ƙarshen ta’...
26/12/2025

Abin da ya faru a Sokoto ya kamata kowa ya tsaya ya yi tunani mai zurfi. Idan har manufar Æmurka ita ce kawo ƙarshen ta’addanci, to da ina ya kamata a fara? A Arewa maso Yamma, kowa ya san cewa barazanar tsaro mafi muni ita ce ’yan fashi da masu garkuwa da mutane, ba wai wasu ƙungiyoyi da ba su mamaye yankin ba(ISIS).

Duk da haka, abin da aka gani ya bambanta da wannan fahimta. An kai hari a wurin da ba shi ne cibiyar ayyukan masu garkuwa da mutane ba, alhali manyan jagororin bandit suna nan suna yawo ba tare da an tabo su ba. Wannan ya sa mutane da dama ke tambaya: shin wannan aiki da gaske yana da alaƙa da tsaro ne, ko kuwa akwai wata manufa dabam a bayan fage?

Abu ne sananne cewa ƙungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi kamar ISIS sun sha faɗa da bandits, a wasu lokuta har suna kubutar da mutanen da aka sace. Duk da cewa ba za a wanke su daga ta'addanci ba, tambayar ita ce: me ya sa aka mayar da hankali kansu, aka bar waɗanda ke haddasa babbar fitina?

Shekaru da dama tarihi ya nuna duk inda Æmurka ta shiga da nufin yaki da ta’addanci, sai dai tashin hankali ya karu ba dai ya ragu ba. Afghanistan, Iraq, Libya, Syria—duk misalai ne da s**a nuna cewa bayan kasa kamar Æmurka ta shiga da nufin samar da zaman lafiya, ƙasashe kan watse, makamai su bazu, rayukan fararen hula su salwanta.

A Najeriya ma, rashin tsaro ya samo asali ne daga gazawar cikin gida. Gwamnati ta kasa kare jama’a, ta bar gibin da wasu ke amfani da shi. Yanzu kuma ana iya amfani da wannan yanayi wajen karkatar da hankalin al’umma daga wasu muhimman batutuwan siyasa da tattalin arziki. Misali akan dauke hankalin al'umma wajen zartar da sabuwar dokar Haraji da Tinubu ya shirya bisa son zuciya.

Muna bukatar tsayayyen tsari daga shugabanninmu na Arewa—sarakuna, malamai, ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki—domin a fitar da yankin daga wannan mawuyacin hali. Idan aka ci gaba da yin shiru, fitinar sai ta shafi kowa. Allah Ya kiyaye.

WATA SABUWA: AMURKA TA KADDAMAR DA HARI CIKIN NIGERIAA daren yau da ya gabata, Shugaban Kasar Amurka Donald Trump ya bad...
26/12/2025

WATA SABUWA: AMURKA TA KADDAMAR DA HARI CIKIN NIGERIA

A daren yau da ya gabata, Shugaban Kasar Amurka Donald Trump ya bada umarni an kaddamar da wani gagarumin hari mai matukar muni kan ‘yan ta’addan ISIS a jihar Sokoto dake Arewa maso gabashin Nigeria.

Donald Trump yace harin ya shafi mafakar kungiyar ISIS ne a jihar Sokoto wadanda suke kai hari da kashe Kiristoci a Nigeria, yace idan ba su daina kisan Kiristocin Nigeria ba, za su fuskanci mummunan sakamako kamar yadda s**a fara gani a daren yau.

Trump yace wannan hari da Amurka tayi a jihar Sokoto duk duniya Amurka ne kadai ke da karfin iya kaddamar da harin, Kasar Amurka ba za ta bari tsattsauran ra’ayin ta’addancin Musulunci yayi karfi ba a Nigeria.

Amurka tayi amfani da sansanin Sojin ruwanta na USS Paul Ignatius dake Rota a Kasar Spain ta harbo hatsabibin makamin Missile mai gudu kamar walkiya mai suna "Tomahawk Missile" zuwa jihar Sokoto.

Sannan a cikin daren da ya gabata ma'aikatar kula da harkokin waje na Nigeria ta fitar da sanarwa jim kadan bayan kaddamar da harin, tace da amincewar Gwamnatin Nigeria aka kaddamar da harin domin a durkukusar da karfin 'yan ta'adda, kuma an dau matakin da zai kauce taba fararen hula.

Sai dai wani abin fashewa da ake zargin yana cikin tarkacen makami mai linzami da Amurka ta harba zuwa Sokoto yayi saukar bazata a garin Jabo karamar hukumar Tambuwal jihar sokoto duk a cikin daren yau da ya gabata kamar yadda zaku gani a hoto, bayan abin ya fashe mutanen garin sun gudu zuwa neman mafaka.

Zuwa yanzu dai ba'a san girman ta'adin da harin Amurka ya yiwa 'yan ta'adda a Sokoto ba, fatan mu kar a fake da wannan a taba wanda bai ji ba bai gani ba kamar yadda s**a saba yi a sauran Kasashen Musulmi.

Sannan ya kamata Amurka ta dena cewa masu tsatsauran ra'ayin addinin Musulunci suna ka$he Kiristoci saboda banbancin addini, ki$an da akeyi a Nigeria bai da alaka da banbancin addini, Musulmai da Kiristoci duka ana ka$hewa.

~ Datti Assalafiy

Hoto mai magana.
24/12/2025

Hoto mai magana.

Kaɗan Daga Cikin Illolin HarajiAttajirin Afirka, Aliko Dangote ya yi bayani kan dalilin da ya sa farashin simintin kamfa...
23/12/2025

Kaɗan Daga Cikin Illolin Haraji

Attajirin Afirka, Aliko Dangote ya yi bayani kan dalilin da ya sa farashin simintin kamfaninsa ke ƙasa a ƙasashen waje fiye da abin da ’yan Najeriya ke saye a cikin gida.

Ya danganta bambancin farashin da yawan haraji da tsauraran ƙa’idoji da masana’antu ke fuskanta a Najeriya, wanda ke ƙara tsadar kayayyaki.

Dangote ya ce irin wannan matsala ne ke damun matatar mai na sa da ke Lagos, wanda duk da manufar sa na rage matsalar tsadan mai amma yana fuskantar s**a daga wasu ɓangarori daban-daban.

Ba abinda Harajin Tulumbu ke haifar wa, sai ƙara tsadar rayuwa.

21/12/2025
Matashi mai tunani ba ya zama kayan aikin ɓata gari, domin duk wanda ya san darajarsa ba ya bari a yi amfani da shi don ...
21/12/2025

Matashi mai tunani ba ya zama kayan aikin ɓata gari, domin duk wanda ya san darajarsa ba ya bari a yi amfani da shi don cutar da kansa da al’umma.

Wannan shi ne shugaban ƙasa da ya je Majalisar Ɗinkin Duniya, a gaban Yahudawa, ya kare Annabi Muhammad (S.A.W).Shi ne s...
20/12/2025

Wannan shi ne shugaban ƙasa da ya je Majalisar Ɗinkin Duniya, a gaban Yahudawa, ya kare Annabi Muhammad (S.A.W).

Shi ne shugaban ƙasa na farko a tarihin Masar da ya ja sallah a Masallacin Annabi (S.A.W) a Madina.

Shi ne shugaban ƙasa da ya buɗe wa Falasɗinawa iyakar ƙasar Masar saboda zaluncin da Yahudawa ke yi musu.

Shi ne shugaban ƙasa da a lokacinsa malaman addini, hafizan Al-Kur’ani, kuma ƙwararrun injiniyoyi a fannin kimiyya s**a samu girmamawa.

Shi ne shugaban ƙasa da ya fito da malamai da duk wanda aka daure bisa zalunci a mulkin Husni Mubarak.

Shi ne ya yi ƙoƙarin tafiyar da tsarin ƙasar Masar bisa koyarwar Musulunci.

Shi ne shugaban ƙasa da Larabawan da ke kawance da Amurka s**a haɗa baki da Isra’ila wajen kifar da gwamnatinsa.

Shi ne shugaban ƙasa da ya yi shahada a gidan yari, a hannun maƙiyan addinin Allah.

Shi ne shugaban ƙasa da aka hana ’yan uwansa da masoyansa damar sallatar gawarsa.

An haife shi a ranar 20/8/1951.
Ya zama shugaban ƙasa a ranar 30/6/2012.
An yi masa juyin mulki a ranar 3/7/2013.
Ya rasu a gidan yari a ranar 17/6/2019.

Shaheed Mursi (Rahimahullah).

Tarihi ba zai taɓa mantawa da kai ba, har abada.

Allah Ya ƙara masa rahama, Ya sanya Aljannar Firdausi ce makomarsa.

Najeriya ba ta gyaruwa sai biyun nan sun gyaru:1. Shugabanni2. MalamaiIn ba su gyaru ba, Najeriya ba za ta gyaru ba. Yad...
20/12/2025

Najeriya ba ta gyaruwa sai biyun nan sun gyaru:
1. Shugabanni
2. Malamai
In ba su gyaru ba, Najeriya ba za ta gyaru ba. Yadda Najeriya ta bace, kashi biyun nan ne s**a bata ta: da Miyagun Malamai da Miyagun Shugabanni.

WANENE MAI KARFI?Mai ƙarfi ba shi ne wanda yake da makami ba, ba shi ne wanda yake da mulki ko mukami ba, kuma ba shi ne...
19/12/2025

WANENE MAI KARFI?
Mai ƙarfi ba shi ne wanda yake da makami ba, ba shi ne wanda yake da mulki ko mukami ba, kuma ba shi ne wanda yake da kuɗi ko suna ba. Mai ƙarfi shi ne wanda yake da gaskiya.

Karya na iya yin amo na ɗan lokaci, amma gaskiya tana tafiya a hankali kuma tana kaiwa inda ƙarya ba za ta taɓa kaiwa ba. Mulki na iya tsoratarwa, amma gaskiya tana gina ƙwaƙwalwa da tunanin al’umma.

Wanda yake amfani da addini, kabila, ko ƙarya domin cimma buri na siyasa na iya samun riba a yau, amma gobe tarihi zai fallasa shi.

Ƙarfi na gaske shi ne tsayawa kan gaskiya koda kai kaɗai ne, faɗin abin da ya dace koda zai ɓata wa mutane rai, da ƙin sayar da lamiri domin riba ta wucin-gadi.

A ƙarshe, ba wanda ya taɓa doke gaskiya. Ana iya jinkirta ta, amma ba a iya kashe ta.

Don haka, kana son ka zama mai ƙarfi na yau, ko kuma na tarihi?

ABUN A YABA: Shugaban karamar hukumar Funtua a jihar Katsina, Honarabul Abdulmutallab Jibrin Goya, ya saya wa wani maray...
18/12/2025

ABUN A YABA: Shugaban karamar hukumar Funtua a jihar Katsina, Honarabul Abdulmutallab Jibrin Goya, ya saya wa wani maraya sabon takalmin soso tare da ba shi jarin ruwan leda.

A kan wannan babban al'amarin aka ɗau hoton yaro riƙe da takalmi ana yaɗawa; ba shakka an ci mutuncin wannan yaron, an ci amanar iyalansa, an wukanta danginsa, ko da yake laifinsu ne, domin bai wuce wani daga cikinsu ya ɗauki nauyinsa ba.

Kuma hakan abin kunya ne ga shugabannin Funtua, abin kunya ne ga mutanen Funtua, kuma abin kunya ne ga dangin yaron.

Kalubale gare mu: indai ba mu daina wulaƙanta kanmu ba, indai ba mu daina ƙasƙantar da kawunanmu a wajen masu mulki ba, indai ba mu daina yarda da cin mutuncin ’yan uwanmu ba, to a haka za mu ƙare cikin tozarci.

Wannan kyautar, a sirrance ya kamata a yi ta; kuma a matsayin ƙaramar hukuma, hakan babban abin kunya ne.

Wannan yaron at this level ilimi yake buƙata, ba tallar pure water ba. Kuma ba ina nufin hakan bai dace ba; a’a, komai da lokacinsa, kowane lokaci akwai abin da ya fi dacewa da shi.

Wannan ya zama darasi a gare mu: idan za mu tashi mu taimaki junanmu, mu tashi. Idan kuma za mu ci gaba da bari ana wulaƙanta ’yan uwanmu, mu bari. Amma mu sani, ƙarshe wulaƙancin a kanmu zai ƙare, domin wanda aka wulakanta ɗan uwanmu ne, kuma ɗan wani — uban wani.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sabuwar Duniya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share