08/05/2026
Dalilin da ya sa shugaban Jam'iyyar PRP Ya ajiye aiki da Gwamnatin Tinubu ya rungumi jam'iyyar Malam Aminu Kano, don ceto Al'ummar Nigeria.
A wata hira da aka yi da Dr. Hakeem Baba Ahmad ya ce:-
Dalilin da yasa ba zan sake yin aiki a gwamnatin Tinubu ba – Hakeem Baba-Ahmed
Baba-Ahmed ya ce ya ajiye aikinsa ne saboda gwamnatin Tinubu ba ta nuna ƙwazo da himmar gyara Najeriya ba.
Tsohon Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu Shawara ta Musamman kan Harkokin Siyasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya ce bai yi nadamar yin aiki da shugaban ƙasar ba, amma ba zai sake amincewa ya koma aikin ba idan aka sake ba shi damar.
An naɗa Baba-Ahmed a shekarar 2023 domin ya yi aiki a ƙarƙashin ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan harkokin siyasa. Sai dai ya yi murabus daga mukaminsa a watan Afrilu.
Yayin da yake magana a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis, Baba-Ahmed ya ce ya sauka daga mukaminsa ne saboda gwamnatin Tinubu ba ta nuna ƙwarin gwiwa wajen gyara Najeriya ba.
Ya ce bai yi nadamar yin aiki da Tinubu ba.
Sai dai da aka tambaye shi ko zai sake karɓar irin wannan damar idan aka ba shi, sai ya amsa da cewa: “Ta yadda gwamnatin Tinubu ke tafiya yanzu — a’a.”
Ya ƙara da cewa: “Ban yi nadamar shiga gwamnatin ba. Na fita ne saboda babu damar yin aiki yadda ya kamata. Ban ga wutar himma ba, ban ga jajircewa da ƙoƙarin gyara ƙasar da aka lalata ba. Abin da na gani shi ne ƙasar na ƙara tabarbarewa.”
Tsohon mai ba shugaban ƙasa shawarar ya ce ba zai iya ci gaba da aiki da gwamnatin da, a ra’ayinsa, ta rasa amincewar jama’a wajen kawo sauyi ba — musamman wajen magance talauci da rashin tsaro a Arewa, waɗanda ya ce sun ƙara muni a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
Ya kuma ce duk da cewa shugaban ƙasar ya nemi ganawa da shi kai tsaye, ya ƙi amincewa saboda zai gaya masa abubuwan da watakila ba zai so ji ba — ciki har da shawarar kada ya sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a shekarar 2027.
Baba-Ahmed ya ce Tinubu ya kamata ya goyi bayan wani matashi mai kuzari daga cikin jam’iyyarsa domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027, maimakon neman wa’adi na biyu da kansa.
‘Ban yi wani aiki ba’
Baba-Ahmed ya bayyana takaicinsa cewa duk da irin gudunmawar da zai iya bayarwa ta fuskar shawarwarin siyasa — wanda shi ne dalilin naɗa shi — bai samu damar bayar da wata muhimmiyar gudunmawa ba.
Ya ce: “A’a, ban yi wani aiki ba. Ya kamata in zama mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa a ofishin mataimakin shugaban ƙasa, amma ban ba da wata shawara ba.”
Dangane da matsayar Arewa kan Tinubu, Baba-Ahmed ya ce abin da Arewa kawai ke so shi ne shugaban ƙasa ya magance matsalolin yankin.
Ya lissafo rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi, da shaye-shaye a matsayin matsalolin da mutanen Arewa ke son Tinubu ya magance.