Alheri TV

Alheri TV Sabuwar Tasha ce ta Hausa da za ta dinga yin shirye shirye Kala Kala, da kuma sabbin sahihan labarai na nishadi da ilmantarwa domin ta zamo ALHERI TV
(1)

Rahama Sidi Ali fitacciyar jarumar masana'antar fina-finan Hausa ta Kannywood ce wadda aka haifa a ranar 22 ga Yuli, 198...
16/06/2026

Rahama Sidi Ali fitacciyar jarumar masana'antar fina-finan Hausa ta Kannywood ce wadda aka haifa a ranar 22 ga Yuli, 1989 a Jihar Kaduna, Najeriya.

Ta taso a Kaduna inda ta yi karatun firamare da sakandare kafin ta ci gaba da karatu a Kaduna Polytechnic.

Ta fara harkar fim tun tana matashiya, inda fim ɗinta na farko ya kasance Far Mace, sannan ta fito a wasu fina-finai da shirye-shiryen talabijin da s**a haɗa da Matar Abokina, Kwana Casa'in, da sauran ayyukan Kannywood.

Sai dai ta samu gagarumar ɗaukaka ne a shekarar 2019 bayan ta taka rawar Umma (Mahaifiyar Maryam) a cikin shahararren shirin talabijin na Labarina

Wanda ya sanya ta zama sananniya a faɗin Arewacin Najeriya saboda kwarewarta wajen nuna halayen uwa mai tausayi, tarbiyya da hikima duk da cewa shekarunta ba su kai na irin rawar da take takawa ba.

A hirarraki daban-daban da ta yi, Rahama ta bayyana cewa mutane da yawa sun riƙa ɗaukarta a matsayin tsohuwa saboda yadda take fitowa a matsayin uwa a cikin Labarina.

Dangane da rayuwarta ta kashin kai, ta bayyana cewa har yanzu ba ta yi aure ba, amma tana fatan yin aure a nan gaba, sannan ta taɓa cewa ba za ta iya auren ɗan fim ba saboda tana da tsananin kishi.

Baya ga nasarar da ta samu a fina-finai, Rahama Sidi Ali ta shahara saboda sauƙin kai, mutunta masoyanta da kuma hulɗa da su ta kafafen sada zumunta, lamarin da ya ƙara mata farin jini.

A yau, ana kallonta a matsayin ɗaya daga cikin fitattun jaruman Kannywood masu taka rawar uwa.

Kuma tana ci gaba da ba da gudummawa wajen haɓaka masana'antar fina-finan Hausa tare da kasancewa abin koyi ga matasa masu sha'awar harkar fim

Kylian Mbappé Ya zama Dan wasan da ya fi kowa zura kwallye  a taqagar kasar Faransa 🇫🇷Inda a yanzu yana da kwallaye 58 g...
16/06/2026

Kylian Mbappé Ya zama Dan wasan da ya fi kowa zura kwallye a taqagar kasar Faransa 🇫🇷
Inda a yanzu yana da kwallaye 58 ga Les Bleus yana da shekaru 27 kacal, ya zarce tarihin da ya gabata na kwallaye 57 da Olivier Giroud ya ci!

Cin kwallaye 58 a wasanni 99 kacal ga Faransa

Ga sabon tarihi na ban mamakiMikel Oyarzabal ya zama ɗan wasa na farko tun daga shekarar 1966 da ya buga fiye da minti 3...
15/06/2026

Ga sabon tarihi na ban mamaki
Mikel Oyarzabal ya zama ɗan wasa na farko tun daga shekarar 1966 da ya buga fiye da minti 30 a wasan Kofin Duniya na FIFA ba tare da ya taɓa ƙwallo ko sau ɗaya ba. 🇪🇸❌
Wannan abin mamaki ya faru ne a wasan da Spain ta tashi kunnen doki 0-0 da Cape Verde, inda Oyarzabal ya shafe mintuna 30 na farko ba tare da samun wata hulɗa da ƙwallon ba. Wannan ya zama sabon tarihi mara daɗi a bayanan Kofin Duniya tun lokacin da aka fara tattara irin waɗannan ƙididdiga a 1966.

Kotun Koli ta kasar Saudiyya ta sanar da cewa ranar Talata, 16 ga Yuni, 2026, ita ce 1 ga Muharram 1448AH, wanda ke nuna...
15/06/2026

Kotun Koli ta kasar Saudiyya ta sanar da cewa ranar Talata, 16 ga Yuni, 2026, ita ce 1 ga Muharram 1448AH, wanda ke nuna fara sabuwar shekarar Musulunci.

Sanarwar ta biyo bayan tabbatar da ganin jinjirin watan Muharram, lamarin da ya kawo karshen shekarar 1447AH tare da bude sabuwar shekarar Hijira ta 1448AH ga Musulmai a Saudiyya da wasu kasashe da ke bin tsarin ganin wata na kasar.

Jam'iyyar ADC Ta yi barazanar shiga kotu kan batun soke rijistar ta.Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta yi Al...
15/06/2026

Jam'iyyar ADC Ta yi barazanar shiga kotu kan batun soke rijistar ta.
Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta yi Allah-wadai da wani hukuncin da ake zargin Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke na neman cireta daga rijista, inda ta bayyana matakin a matsayin barazana ga dimokuradiyyar Nijeriya tare da gargadin cewa bai kamata a yi amfani da bangaren shari’a wajen raunana jam’iyyun adawa ba.
A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar na Ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Litinin, jam’iyyar ta zargi wasu jami’an gwamnati da goyon bayan yunkurin kawar da ita da sauran jam’iyyun adawa daga fagen siyasa

Tsuguno ba ta kare baKotu ta umarci INEC ta soke rajistar ADC da wasu jam’iyyu huɗuBabbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta u...
15/06/2026

Tsuguno ba ta kare ba
Kotu ta umarci INEC ta soke rajistar ADC da wasu jam’iyyu huɗu

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta soke rajistar jam’iyyar ADC da wasu jam’iyyu huɗu.

Mai shari’a Peter Lifu ne ya yanke hukuncin a ranar Litinin, inda ya ce jam’iyyun sun gaza cika wasu sharuddan da kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada ga jam’iyyun siyasa.

A ganin ku wadanne ne ragowar?

Kwankwaso ya kara matso da Dansa kusa da Gwamnati. Kamar yadda masu bibiyar sha'anin siyasa ke cewa bayan fitar da sanar...
15/06/2026

Kwankwaso ya kara matso da Dansa kusa da Gwamnati. Kamar yadda masu bibiyar sha'anin siyasa ke cewa bayan fitar da sanarwa a yammacin ranar litinin da ta tabbatar da Comrade Gwarzo ya dauki Mustapha Kwankwaso a mataimakinsa a takarar Gwamnan Kano ta NDC.

Jamʼiyyar ce ta sanar da hakan ta hannun Kakakin tafiyar Kwankwasiyya Dr. Habib Sale Mailemo.

Ana ta magana akan ganin hoton Adam A Zango da Aisha Humaira.Wannan tsohon hoto ne da aka dauka yayin gudanar da wani fi...
15/06/2026

Ana ta magana akan ganin hoton Adam A Zango da Aisha Humaira.
Wannan tsohon hoto ne da aka dauka yayin gudanar da wani film tun lokutan baya.
Mu fadi Alkhairi ko mu yi shiru

Da alama dai tsuguno ba ta kare ba a jam'iyyar ADC.Tun bayan kammala zabukan fitar da gwani a jam'iyyar ADC, tsohon mata...
15/06/2026

Da alama dai tsuguno ba ta kare ba a jam'iyyar ADC.
Tun bayan kammala zabukan fitar da gwani a jam'iyyar ADC, tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar da sauran masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ke ta fadi-tashin shawo kan tsohon gwamnan jihar Rivers Rotimi Amaechi da ya amince da yi wa Atiku takarar mataimakin shugaban kasa.

Tun da fari dai jaridun Najeriya sun wallafa labarin cewa Amaechi ya amince da marawa Atiku baya a matsayin mataimaki, to amma har ya zuwa wannan lokaci ba a cimma matsaya ba.

An fara rade radin soyayya ta dawo sabuwa tsakanin Adam A Zango da Fati Washa, domin ana ta ganin sababbin hotunan jarum...
14/06/2026

An fara rade radin soyayya ta dawo sabuwa tsakanin Adam A Zango da Fati Washa, domin ana ta ganin sababbin hotunan jaruman yana yawo mabanbanta kuma cikin fara'a da walwala. Amma a gaskiya hotunan a na daukar su ne a yayin da ake shirin film, sai dai kawai akwai shakuwa mai karfi tsakaninsu wanda ya sa a duk lokacinda s**a hadu dole ne sai an tuna da.
Amma wasu na ganin yakamata a rage musamman yadda Matar Jarumin ta yanzu kasancewarta 'Yar masana'antar ce ta kannywood, domin kar ta ji ba dadi. Amma wasu na ganin hakan ba komai ba ne, tunda ai ..Kowa ya sai rariya...
Fata dai Allah Ya sa mu ji Alheri

Address

No. 7 Gidan Alhaji Ado, U/Dabai Street Kano
Kano

Telephone

+2348088827172

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alheri TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share