Alheri TV

Alheri TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Alheri TV, No.7 Gidan Alhaji Ado, U/Dabai street Kano, Kano.
(1)

Sabuwar Tasha ce ta Hausa da za ta dinga yin shirye shirye Kala Kala, da kuma sababbin Fina finan Hausa da sabon series mai suna ALHERI TV daga ALI RABI'U ALI DADDY

Jaruman kannywood sun shiga siyasa, amma shi Ali Rabiu Ali Daddy, takara yake yi maimakom bin 'Yan siyasar kawai. Ko me ...
12/05/2026

Jaruman kannywood sun shiga siyasa, amma shi Ali Rabiu Ali Daddy, takara yake yi maimakom bin 'Yan siyasar kawai. Ko me ya ja ra'ayinsa shiga siyasa?

Wata sabuwa, Iran ta gudanar da atisayen soji ba tare da sanarwa ba
12/05/2026

Wata sabuwa, Iran ta gudanar da atisayen soji ba tare da sanarwa ba

A yau ne za a goge raini, kuma gwarzon Saudiyya zai bayyana tsakanin Ronaldo da Benzema. Za a fafata wasa ne da ba'a tab...
12/05/2026

A yau ne za a goge raini, kuma gwarzon Saudiyya zai bayyana tsakanin Ronaldo da Benzema. Za a fafata wasa ne da ba'a taba ganin kalarsa ba a gasar Saudi Pro league, inda Ronaldo zai nemi lashe kofinsa na farko shi kuma Benzema zai nemi na biyu. Wa kuke yiwa fatan nasara

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da bayar da naira miliyan 265 ga alhazan bana su 3,620 daga jihar domin tallafa musu da bu...
11/05/2026

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da bayar da naira miliyan 265 ga alhazan bana su 3,620 daga jihar domin tallafa musu da bukatunsu na yau da kullum a Saudiyya yayin aikin Hajji.

kowane mahajjaci zai samu Riyal 200.

NDC ta hana kwankwaso tikitin takarar shugaban kasa, amma hakan bai ba shi haushi ba.Kwankwaso ya goyi bayan miƙa tikiti...
09/05/2026

NDC ta hana kwankwaso tikitin takarar shugaban kasa, amma hakan bai ba shi haushi ba.
Kwankwaso ya goyi bayan miƙa tikitin takarar shugaban kasa na NDC ga yankin Kudu

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana goyon bayansa ga matakin jam’iyyar NDC na mika tikitin takarar shugaban kasa na shekarar 2027 ga yankin Kudancin Nijeriya.

Kwankwaso ya ce wannan matakin ya dace da tsarin adalci, daidaito da kuma rabon mulki tsakanin yankunan kasar nan domin tabbatar da hadin kai a cikin jam’iyyar da kasa baki daya.

Dalilin da ya sa shugaban Jam'iyyar PRP Ya ajiye aiki da Gwamnatin Tinubu ya rungumi jam'iyyar Malam Aminu Kano, don cet...
08/05/2026

Dalilin da ya sa shugaban Jam'iyyar PRP Ya ajiye aiki da Gwamnatin Tinubu ya rungumi jam'iyyar Malam Aminu Kano, don ceto Al'ummar Nigeria.

A wata hira da aka yi da Dr. Hakeem Baba Ahmad ya ce:-

Dalilin da yasa ba zan sake yin aiki a gwamnatin Tinubu ba – Hakeem Baba-Ahmed
Baba-Ahmed ya ce ya ajiye aikinsa ne saboda gwamnatin Tinubu ba ta nuna ƙwazo da himmar gyara Najeriya ba.
Tsohon Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu Shawara ta Musamman kan Harkokin Siyasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya ce bai yi nadamar yin aiki da shugaban ƙasar ba, amma ba zai sake amincewa ya koma aikin ba idan aka sake ba shi damar.
An naɗa Baba-Ahmed a shekarar 2023 domin ya yi aiki a ƙarƙashin ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan harkokin siyasa. Sai dai ya yi murabus daga mukaminsa a watan Afrilu.
Yayin da yake magana a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis, Baba-Ahmed ya ce ya sauka daga mukaminsa ne saboda gwamnatin Tinubu ba ta nuna ƙwarin gwiwa wajen gyara Najeriya ba.
Ya ce bai yi nadamar yin aiki da Tinubu ba.
Sai dai da aka tambaye shi ko zai sake karɓar irin wannan damar idan aka ba shi, sai ya amsa da cewa: “Ta yadda gwamnatin Tinubu ke tafiya yanzu — a’a.”
Ya ƙara da cewa: “Ban yi nadamar shiga gwamnatin ba. Na fita ne saboda babu damar yin aiki yadda ya kamata. Ban ga wutar himma ba, ban ga jajircewa da ƙoƙarin gyara ƙasar da aka lalata ba. Abin da na gani shi ne ƙasar na ƙara tabarbarewa.”
Tsohon mai ba shugaban ƙasa shawarar ya ce ba zai iya ci gaba da aiki da gwamnatin da, a ra’ayinsa, ta rasa amincewar jama’a wajen kawo sauyi ba — musamman wajen magance talauci da rashin tsaro a Arewa, waɗanda ya ce sun ƙara muni a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
Ya kuma ce duk da cewa shugaban ƙasar ya nemi ganawa da shi kai tsaye, ya ƙi amincewa saboda zai gaya masa abubuwan da watakila ba zai so ji ba — ciki har da shawarar kada ya sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a shekarar 2027.
Baba-Ahmed ya ce Tinubu ya kamata ya goyi bayan wani matashi mai kuzari daga cikin jam’iyyarsa domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027, maimakon neman wa’adi na biyu da kansa.
‘Ban yi wani aiki ba’
Baba-Ahmed ya bayyana takaicinsa cewa duk da irin gudunmawar da zai iya bayarwa ta fuskar shawarwarin siyasa — wanda shi ne dalilin naɗa shi — bai samu damar bayar da wata muhimmiyar gudunmawa ba.
Ya ce: “A’a, ban yi wani aiki ba. Ya kamata in zama mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa a ofishin mataimakin shugaban ƙasa, amma ban ba da wata shawara ba.”
Dangane da matsayar Arewa kan Tinubu, Baba-Ahmed ya ce abin da Arewa kawai ke so shi ne shugaban ƙasa ya magance matsalolin yankin.
Ya lissafo rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi, da shaye-shaye a matsayin matsalolin da mutanen Arewa ke son Tinubu ya magance.

TARIHI YA SAKE RUBUTU: Cristiano Ronaldo ya kai ƙwallaye 100 a Saudi Pro League! Fitaccen tauraron duniya, Cristiano Ron...
08/05/2026

TARIHI YA SAKE RUBUTU: Cristiano Ronaldo ya kai ƙwallaye 100 a Saudi Pro League!

Fitaccen tauraron duniya, Cristiano Ronaldo, ya sake kafa wani babban tarihi a gasar Saudi Pro League bayan ya kai:

ƙwallaye 100 a gasar Saudiyya!
Guda 100 cikin wasanni 105 kacal

Abin da ya fi ɗaukar hankali shi ne yadda Ronaldo ya cimma wannan tarihi cikin sauri:

ƙwallaye 100 cikin wasanni 105 kacal

Wannan kididdiga na nuna irin:
ƙwarewarsa wajen zura ƙwallo
daidaitonsa

da kuma yadda har yanzu yake cikin matakin koli duk da shekaru da ya yi a ƙwallon ƙafa.

Kofin liga na ƙara matsowa

Baya ga wannan tarihi na mutum ɗaya, ƙungiyarsa na ci gaba da matsowa kusa da lashe kofin liga, abin da ke ƙara sa kakar ta zama ta musamman gare shi.

“Machine” har yanzu yana aiki

Magoya baya da masana sun ci gaba da mamakin yadda Ronaldo ke ci gaba da karya tarihi duk inda ya je:

a Ingila
Spain
Italy
yanzu kuma Saudiyya

Wani sabon milestone
Wannan ba shi ne karo na farko da Ronaldo ke shiga tarihi ba — amma duk lokacin da ya yi hakan, yana ƙara tabbatar da dalilin da ya sa ake kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin: 🐐 mafi girman ‘yan wasan da s**a taɓa taka ƙwallo.

Shekaru na wucewa… amma Cristiano Ronaldo na ci gaba da yin abin da ya fi so — zura ƙwallaye da kafa tarihi.

Yan Najerya na bukatar sake shiri, musamman in aka yi la'akari da abinda gwamnati ta ce:-"Ba za mu taɓa mayar da tallafi...
07/05/2026

Yan Najerya na bukatar sake shiri, musamman in aka yi la'akari da abinda gwamnati ta ce:-
"Ba za mu taɓa mayar da tallafin man fetur ko ƙayyade farashinsa ba - Gwamnatin Nijeriya

Ministan kudi na Nijeriya Taiwo Oyedele ya jaddada cewa gwamnatin Tinubu ba za ta taba mayar da tallafin man fetur da ta janye a baya, ko kuma kayyade farashinsa ba.

Ministan ya bayyana haka ne a kasar Faransa, yayin tattaunawa da manyan 'yan kasuwa na duniya tare da shugaba Tinubu, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Valverde na real madrid ya karyata batun kutufo da Tchoumeni ya yi masa.A Hukumance: Fede Valverde ya saki sanarwa a sha...
07/05/2026

Valverde na real madrid ya karyata batun kutufo da Tchoumeni ya yi masa.
A Hukumance: Fede Valverde ya saki sanarwa a shafinsa na Instagram:

“Jiya na samu saɓani da wani abokin wasana lokacin da muke ɗaukar horo. Gajiya na fafatawar da muke da kuma takaicin rashin nasara ne yasa komai yayi tsamari a tsakanin mu.

A cikin ɗakin sanya tufafi, ire-iren waɗannan abubuwan suna faruwa domin yau da kullum tafi ƙarfin wasa, kuma galibi ana magance su ne a cikin gida ba tare da sun fito fili ba.

A bayyane yake cewa akwai wani a cikin mu da yake yaɗa jita-jita, kuma duba da cewa kakar wasan nan ba mu lashe kofina ba, Real Madrid tana fuskantar s**a kowanne lokaci, hakan yasa komai yake zama abun magana.

Yau ma mun sake samun rashin fahimta da wannan abokin wasan nawa. Yayin da muke cacar baki, cikin kuskure na bugi teburi, wanda hakan ya janyo min ɗan rauni a goshina wanda sai da ya buƙaci zuwa asibiti domin duba lafiyata. Babu wani lokaci da abokin wasa na ya mare ni, nima kuma ban mare shi ba, ko da yake na san sai yafi muku daɗi idan kunji cewa mun kaiwa juna hannu ko kuma da gangan hakan ta faru, amma dai hakan ba gaskiya ba ne.

Ina ba da haƙuri. Na shirya karbar dukkan wani hukunci da ƙungiyar nan ta yanke akan mu, bani da tantama cewa duk wani saɓani da zamu iya samu a wajen fili yana ƙarawa ne da zaran mun shiga filin wasa, kuma idan har akwai wanda zai kare ƙungiyar nan a cikin fili, to ni ne na farko. Bani da niyyar yin magana sai kakar wasa ta ƙare.

Na ji baƙin ciki da raɗadin shiga wannan yanayi da zai hana ni buga wasa na gaba saboda shawarar Likitoci. A kowanne lokaci ina bayar da dukkan ƙoƙarina ga ƙungiyar nan har zuwa ƙarshe, kuma hakan yana min ciwo fiye da kowa sakamakon rashin samun damar buga wasa. A shirye nake na haɗa kai da ƙungiya ta da kuma abokan wasa na kan duk wata shawara da s**a ga ya dace a ɗauka.

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya gana da shugaban jam’iyyar NDC na ƙasa, Hussaini Mairiga, domin maga...
06/05/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya gana da shugaban jam’iyyar NDC na ƙasa, Hussaini Mairiga, domin magance rikicin cikin gida da ya daɗe yana addabar jam’iyyar a jihar Kano.

Rahotanni sun ce ganawar ta mayar da hankali ne kan haɗa kan mambobin jam’iyyar tare da samar da mafita mai ɗorewa ga sabanin da ke tsakanin ɓangarori daban-daban.

An bayyana cewa, ɓangarorin biyu sun cimma matsaya guda kan muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai, domin ƙarfafa jam’iyyar gabanin zaɓuɓɓuka masu zuwa.

Wata majiya shaidawa KANO LIVE 24 cewa Masu ruwa da tsaki sun bayyana wannan mataki a matsayin wani gagarumin ci gaba da zai taimaka wajen farfaɗo da martabar jam’iyyar NDC a jihar Kano.

Vijay Thalapathy ya zama Chief Minister na Tamil Nadu. Daga yau, mulki ya dawo hannun "Thalapathy". A karshe dai  Vijay ...
04/05/2026

Vijay Thalapathy ya zama Chief Minister na Tamil Nadu. Daga yau, mulki ya dawo hannun "Thalapathy".

A karshe dai Vijay Thalapathy ne a matsayin Chief Minister na Tamil Nadu bayan jiran sakamako na kwanaki 10.

Congratulations Vijay ansha wuya fa sosai,ya sha tuggu irin na siyasa amma a ƙarshe yayi nasara

Address

No.7 Gidan Alhaji Ado, U/Dabai Street Kano
Kano

Telephone

+2348088827172

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alheri TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share