El-hakimee Trust News

El-hakimee Trust News Domin samun ingan taccen labarai masu inganci

27/03/2025

Resolve you NIMC issue

Hukumar sadarwa ta amince da ƙarin kuɗin kiran wayaA farkon wannan makon ne kuma hukumar sadarwa ta Najeriya NCC ta amin...
26/01/2025

Hukumar sadarwa ta amince da ƙarin kuɗin kiran waya

A farkon wannan makon ne kuma hukumar sadarwa ta Najeriya NCC ta amince da buƙatar kamfanonin sadarwa na ƙara kuɗin kiran waya.

A cikin wata sanarwar da NCC ta fitar ranar Litinin, ɗauke da sa hannun kakakin hukumar, Reuben Mouka, ta ce an bayar da izinin ƙarin ne bisa ga ikon da take da shi a ƙarƙashin sashe na 108 na dokar sadarwar Najeriya ta 2003 (NCA), don daidaitawa da kuma amincewa da farashi da kuma cajin kuɗaɗen da kamfanonin sadarwa ke yi.

Sanarwar ta ce kamfanonin sadarwa sun miƙa wannan buƙata ce sak**akon yanayin da ake samu a kasuwa.

Waiwaye: Zuwan Buhari da Obasanjo kotun Paris, da ƙarin kuɗin kiran wayaWannan maƙala ce da kawo muku muhimman batutuwan...
26/01/2025

Waiwaye: Zuwan Buhari da Obasanjo kotun Paris, da ƙarin kuɗin kiran waya

Wannan maƙala ce da kawo muku muhimman batutuwan da s**a faru a Najeriya cikin makon da muke bankwana da shi

Buhari da Obasanjo sun gabatar da shaida a kotun Paris

A farkon makon nan ne tsoffin shugabannin Najeriya biyu, Olusegun Obasanjo da Muhammadu Buhari s**a bayyana a gaban wata kotun cinika a ta ƙasa da ƙasa da ke birnin Paris na a ƙasar Faransa domin bayar da bahasi dangane da kwangilar aikin gina cibiyar samar da wutar lantarki ta Mambilla da ke jihar Taraba.

Wani kamfani mai suna Sunrise Power ne dai ya kai gwamnatin Najeriya ƙara kan saɓa ƙa'idojin kwangilar, inda yake neman gwamnatin ta biya shi dalar Amurka biliyan biyu da miliyan 300 a matsayin diyya na asarar da aka janyo masa.

Obasanjo da Buhari sun bayar da shaida kan abin da ya sani dangane da wannan kwangila da aka bayar da ita a 2003, lokacin tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo.

Rashford zai rage albashi don komawa Barca, Madrid ta bi sahun masu neman DuranMarcus Rashford na shirin amincewa da rag...
26/01/2025

Rashford zai rage albashi don komawa Barca, Madrid ta bi sahun masu neman Duran

Marcus Rashford na shirin amincewa da rage masa albashi don komawa Barcelona daga Manchester United, Real Madrid ta zama kungiya ta baya-bayan nan da ta nuna sha'awar daukar dan wasan gaban Aston Villa Jhon Duran, Newcastle United na shirin sabunta kwantiragi na dogon lokaci ga Alexander Isak.

Dan wasan gaban Manchester United Marcus Rashford, mai shekara 27, a shirye yake a rage masa albashi a kokarinsa na komawa Barcelona a watan Janairu. (Daily Star)

Za a iya taimakawa Barcelona wajen siyan dan wasan Ingila Rashford idan dan wasan bayan Denmark Andreas Christensen, mai shekara 28, ya bar kungiyar. (Mundo Deportivo)

Manchester United ta nemi a sanar da ita makomar dan wasan gaban Chelsea da Faransa Christopher Nkunku, mai shekara 27 (ESPN)

Daraktan Napoli Giovanni Manna ya tabbatar da cewa kungiyar na zawarcin Garnacho da dan wasan gaban Borussia Dortmund na kasar Jamus Karim Adeyemi, mai shekara 23 (Football Italia)

Newcastle United na shirin ba wa dan wasan gaban Sweden Alexander Isak, mai shekara 25 sabon kwantiragi na dogon lokaci a bazara. (Sunday Telegraph)

Real Madrid ta bi sahun Paris St-Germain da Al-Nassr wajen neman dan wasan Aston Villa da Colombia Jhon Duran mai shekaru 21. (Footmercato French)

Dan wasan gaba na Slovenia Benjamin Sesko zai fi son komawa Arsenal a kan Chelsea ko Manchester United amma RB Leipzig ba ta son siyar da dan wasan mai shekaru 21 a kasuwar musayar 'yan wasa ta Janairu. (Talksport)

Bayer Leverkusen na zawarcin dan wasan tsakiyar Aston Villa Emiliano Buendia. Kulob din na Jamus yana neman lamuni tare da zabin siyan dan wasan Argentina mai shekaru 28 (Sky Sport Germany)

Kocin Fenerbahce Jose Mourinho na son dauko dan wasan Barcelona dan kasar Sipaniya Ansu Fati, mai shekara 22, a matsayin aro domin bunkasa kungiyarsa ta lashe gasar. (AS Spanish)

Chelsea ta amince da tayin Yuro miliyan 12 daga Lazio kan dan wasan tsakiyar Italiya Cesare Casadei, mai shekara 22, a yarjejeniyar da ta kunshi kashi 25% na cinikin. (Sport Italy)

Ana alakanta dan wasan gaban Lyon da Algeria Said Benrahma, mai shekara 29 da Ipswich amma yana tattaunawa kan komawa Neom SC, wadda ke mataki na biyu a gasar Saudi Arabiya. (Footmercato French)

Me ya sa ake taƙaddama tsakanin gwamnan Bauchi da Ministan harkokin wajen Najeriya?Ministan harkokin wajen Najeriya, Yus...
26/01/2025

Me ya sa ake taƙaddama tsakanin gwamnan Bauchi da Ministan harkokin wajen Najeriya?

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar ya mayar wa gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed martani bisa wasu kalamai da gwamnan ya yi a kan shi.

Hakan na zuwa ne kwana É—aya bayan BBC ta sanya tattaunawar da ta yi da gwamnan na jihar Bauchi, inda ya kare manufofinsa tare da mayar da martani kan s**ar da ministan ya yi wa gwamnatin jihar.

Ƴan siyasan biyu dukkaninsu sun fito ne daga jiha ɗaya - Bauchi - da ke arewa maso gabashin Najeriya, kuma sun daɗe suna jan zarensu a harkar siyasa.

A wata tattaunawa da ta gabata, Tuggar ya ce "jihar Bauchi ta samu kuɗi sama naira biliyan 8.8 a watan Oktoba da kuma naira biliyan 9 a watan Nuwamba, amma babu wani abu da aka gani a ƙasa a jihar".

Haka nan ministan ya soki lamirin shirin gwamnatin Bauchi na raba filayen noma, inda ya ce gwamnan na "amfani da kuÉ—in da jihar ke samu wajen sayen kadarori da kuma filaye daga hannun talakawa".

Lokacin da aka tambaye shi kan zargin rashin gudanar da ayyuka da kuɗaɗen da jihar ke samu, gwamna Bala Mohammed ya ɗora wani ɓangare na laifin a kan faɗuwar darajar naira idan aka kwatanta da dala.

Sannan ya ƙalubalanci ministan da cewa zai iya duba irin ayyukan da gwamnatin jihar Bauchi ke yi kasancewar ana wallafawa a ƙasidu.

Sai dai ya yi zargin cewa ministan na ƙoƙarin kare shugaban ƙasar Najeriya, Bola Tinubu ne bayan s**ar da gwamnan ya yi masa a kwanakin baya.

Ya ce "Wataƙila yana yi ne domin kare shugaban ƙasa saboda mun faɗi abin da ya k**ata a gyara, shi ya sa shi kuma yake s**a."

A makonnin da s**a gabata an ji yadda gwamnan na Bauchi ya soki shugaban Najeriya, Bola Tinubu a lokacin da ya karɓi baƙuncin wani sanannen malamin addinin Musulunci na ƙasar, wanda ake wa kallon ɗaya daga cikin magoya bayan shugaban ƙasar.

Wasu takardu da aka kwarmata sun ce Amurka ta dakatar da tallafi ga duniya25 Janairu 2025Ma'aikatar harkokin wajen Amurk...
26/01/2025

Wasu takardu da aka kwarmata sun ce Amurka ta dakatar da tallafi ga duniya

25 Janairu 2025

Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta dakatar da kusan dukkannin tallafin da take bai wa ƙasashen waje da take bayarwa tare da tsayar da sabon tallafin da gwamnatin Biden ta shirya bayarwa, k**ar yadda wata takarda da aka aikewa jami'ai da ofisoshin jakadancinta a ƙasashen duniya.

Takardar wadda aka kwarmata ta dai na zuwa ne bayan da shugaba Trump ya bayar da umarnin dakatar da dukkan wani tallafi na kwanaki 90 har zuwa lokacin da za a sake yin duba ga tsarin tallafin.

Amurka ce dai ƙasar da ta fi bayar da tallafi a duniya, inda take tallafawa da kuɗin da s**a kai dala biliyan 68 a 2023 k**ar yadda alƙaluman gwamnati s**a nuna. Sabuwar dokar za ta shafi komai k**a daga tallafi domin cigaba da tallafin soji ga ƙasashen duniya.

Sai dai kuma dakatarwar ba ta shafi aikewa da taimakon gaggawa na abinci da tallafin soji ga Isra'ila da Misra. BBC ta tabbatar da sahihancin takardun da aka kwaramata

Dave Harden, tsohon darektan hukumar bayar da agaji na Amurka a Gabas ta Tsakiya, ya shaida wa BBC cewa umarnin "na da matuƙar muhimmanci", inda ya ce hakan ka iya dakatar da yawan tallafin kuɗi da kaya da na abinci da Amurka ke bai wa ƙasashen duniya, a daidai lokacin da ake sake duba tsarin.

Ya ce dakatarwar za ta shafi abubuwan cigaba da dama k**ar shirin samar da tsaftataccen ruwan sha da muhalli.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito cewa dakatar da tallafin ka iya shafar ƙasar Ukraine wadda ta karɓi mak**ai na biliyoyin daloli lokacin Joe Biden.

Sakataren harkokin wajen na Amurka, Marco Rubio ya ce dakatarwar za ta bai wa sabuwar gwamnatin dama yin duba na tsanaki wajen ganin cewa tallafin yana tafiya yadda ya k**ata sannan bisa tsarin Donald Trump kan ƙasashen waje.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun ƙarin yawaitar shigar tallafin abinci zuwa Gaza bayan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas da ma sauran ƙasashen duniya da ke fama da yunwa sak**akon rikici k**ar Sudan.

Rubio ya ce an bai wa ƙasar Isra'ila da Misra ɗagi dangane da kuɗaɗen da ake buƙata ga sojojin ƙasashen biyu k**ar albashi.

Shaidu da s**a tura wa kamfanin dillancin labarai na Anadoul bidiyoyin abin da ya faru sun ce an tabbatar da mutuwar mut...
26/01/2025

Shaidu da s**a tura wa kamfanin dillancin labarai na Anadoul bidiyoyin abin da ya faru sun ce an tabbatar da mutuwar mutane aƙalla 15, ciki har da yara uku.

Premier League result: Manchester City 3-1 ChelseaManchester City have beaten Chelsea 3-1 in the Premier League as Pep G...
25/01/2025

Premier League result: Manchester City 3-1 Chelsea

Manchester City have beaten Chelsea 3-1 in the Premier League as Pep Guardiola beats his former assistant Enzo Maresca for the second time this season.

Noni Madueke opened the scoring for Chelsea in the third minute after an error from Man City debutant Abdukodir Khusanov. Josko Gvardiol responded for the hosts in the 42nd minute, sliding home a rebound after Robert Sanchez denied Matheus Nunes.

Erling Haaland then gave City their first lead of the match in the 68th minute, lifting a simple finish over Sanchez after the keeper came too far off his line. Phil Foden put the game beyond Chelsea's reach with a clinical finish in the 87th minute after strong hold-up play by Haaland.

Abin da ke sa matasa faÉ—awa shaye-shayeJami'in hukumar ta NDLEA ya ce akwai abubuwa da dama da ke jafa matasa cikin sabg...
25/01/2025

Abin da ke sa matasa faÉ—awa shaye-shaye

Jami'in hukumar ta NDLEA ya ce akwai abubuwa da dama da ke jafa matasa cikin sabgar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a Najeriya da s**a haɗa da.

Rashin kula daga iyaye: A lokuta da dama rashin kula da yara daga ɓangaren iyaye ne ke jefa wasu matasan shaye-shaye.

''A wannan lokaci da muke ciki iyaye suna da sakaci sosai dangane da yaransu'', k**ar yadda jami'in ya bayyana.

''A wasu lokutan rabuwar aure tsakanin ma'aurata kan sa yaro ta taso ba tare da samun kulawar da ta dace daga iyayensa ba, sai ka ga wani lokaci yana wajen mahaifinsa, wani lokaci kuma a wajen mahaifiyarsa'', in ji shi.

Miyagun abokai: Hausawa na cewa zama da maÉ—auki kanwa ke kawo farin kai, a lokuta da dama abokai ne je jafa wasu matasa harkar shaye-shaye, a cewar jami'in.

Gurɓacewar rayuwa: Abdullahi Sardauna ya ce gurɓacewar rayuwa na daga cikin abubuwan da ke ƙara ruruwar matsalar shaye-shaye tsakanin matasa, musamman a ƙasashen Afirka.

''Yadda rayuwar yanzu ta koma, inda inda ka je za ka taras ana rikici-rikice, babu zaman lafiya, to hakan ya sa matasa da dama sun faÉ—a harkokin shaye-shaye'', in ji shi.

Sauƙin samun kayan maye: Wani abu da ke ƙara sanya matasa faɗawa harkar shan miyagun ƙwayoyi shi ne saukin samunsu k**ar yadda jami'in hukumar NDLEA ya bayyana.

''Misa sholisho, wanda ake facin tayar mashin ko ta keke, a kowane shagon gyara za ka same shi, sannan magungunan tari suma a kowane shagon sayar da magunguna za ka samu'', in ji shi.

Zaman banza: ɗaya daga cikin manyan matsalolin da ke haifar da shan ƙwaya shi ne rashin sana'a.

''Yaro ya riƙa zama a cikin marasa aikin yi, sai ya fara tunanin koyon abin da takwarorinsa marasa aikin yi ke yi, wato shaye-shaye''.

'Kayan mayen da aka fi sha a Najeriya'

Jami'in hukumar ta NDLEA ya ce abin da masu ta'ammali da ƙwaya s**a fi amfani da shi a Najeriya ya danganta da inda mutanen suke.

''Abin nan ne da Hausawa ke cewa kowane allazi da nasa amanu, kowane yanki da irin kayan mayen da aka fi samu a wajen'', a cewarsa.

Ya ƙara da cewa a yankin arewa maso gabashin Najeriya, galibi masu ta'ammali da ƙwaya sun fi amfani da tabar wiwi, da magungunan tari na ruwa da ƙwayoyi irin su tramadole, saboda saukin samunsu da kuma araharsu.

Sannan kuma jami'in ya ce akwai wasu abubuwan da ke sa maye waÉ—anda ba su cikin jadawalin Majalisar Dinkin Duniya irin su Akurkura da haÉ—a magi da lemon Laksara da sholisho da madarar sukudaye da sauransu.

Girman matsalar shaye-shaye a Najeriya

''Alƙaluman hukumar yaƙi da ta'ammali da miyagun ƙwayoyi ta Majalisar Dunya, (UNODC) na 2018 sun nuna cewa yawan masu shaye-shaye a Najeriya ya kai miliyan 14.3 ne shaye-shayen miyagun ƙwayoyi daban-daban a ƙasar'', in ji jami'in na NDLEA.

Ya ƙara da cewa ƙiyasin hukumar ta UNODC, ya kuma ce duk inda ka samu mutum huɗu masu ta'ammali da ƙwaya a Najeriya to guda ɗaya daga ciki mace ce.

Sannan kuma ya ce alƙaluman sun nuna cewa a cikin 'yan Najeriya takwas, mutum guda daga cikin na cutuwa saboda alaƙa da masu ta'ammali da ƙwaya.

Haka kuma jami'in ya yi kira ga iyaye da su sanya idanu kan 'ya'yansu domin tabbatar da cewa ba su faÉ—a wannan mummunar É—abi'a ba.

Alamomi 10 da za ku gane idan ƴaƴanku sun fara shaye-shayeShaye-shayen miyagun ƙwayoyi matsala ce da ta jima tana ci wa ...
25/01/2025

Alamomi 10 da za ku gane idan Æ´aÆ´anku sun fara shaye-shaye

Shaye-shayen miyagun ƙwayoyi matsala ce da ta jima tana ci wa al'umma tuwo a ƙwarya, musamman a Najeriya da sauran ƙasashen Afirka.

Gwamnatoci a matakai daban-daban sun sha ɓullo da matakan yaƙi da ɗabi'ar, ciki har da kafa hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya ta NDLEA.

Galibi dai matasa ne s**a fi faÉ—awa tarkon É—abi'ar ta shaye-shaye.

Kuma a lokuta da dama shaye-shayen kan haifar da wasu munanan É—abi'u, k**ar sace-cace, da dabanci da sauran laifuka.

Hukumar NDLEA dai ta ce matasa ne rukunin al'umma da ke kan gaba wajen ta'ammali da miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

Yadda za a gane mai shaye-shaye
Abdullahi Sardauna, babban mataimakin kwamandan hukumar NDLEA mai kula da k**a masu laifi da horas da ma'aikatan hukumar reshen jihar Borno, kuma tsohon jami'i mai kula da fadakarwa da gyaran halin masu ta'ammali da ƙwaya na hukumar ya shaida wa BBC wasu alamomi guda 10 da iyaye za su lura da su domin gane yaransu sun fara shaye-shaye, k**ar haka:

1 - Sauyawar É—abi'a

Abu na farko da iyaye za su lura da shi, shi ne sauyawar halayyar Æ´aÆ´ansu, k**ar yadda jami'in ya bayyana.

''Idan a baya yaronka yana da ladabi da biyayya, sai kuma daga baya ka fahimci ya daina, ya kuma koma wasu É—abi'u marasa kyau to ya k**ata ka zurfafa bincike a kansa'', in ji shi.

2 - Sauya abokai ko ƙawaye

Wata alamar da za ka iya gane yaronka ya fara ta'ammali da ƙwaya, ita ce ka ga ya sauya abokansa na arziki - da a baya ka san shi da su.

Ko kuma idan mace ce ta sauya ƙawayenta na arziki da ka santa da su, ta koma wasu, ba tare da wata hujja mai ƙarfi ba

''Yau ka ganshi da wannan, gobe ka gan shi da wannan, waÉ—anda kuma ba ka aminta da halayensu ba'', in ji shi.

3) Chanjin tsarin rayuwa

Idan yaro ko yarinya s**a fara shaye-shaye za su sauya yadda s**a saba gudanar da rayuwarsu a cewar jami'in hukumar ta NDLEA.

''Alal misali da 'yarka ko É—anka sun saba yin barci da wuri, sai ka ga yanzu sun dawo ba sa barci da wuri sai lokaci ya ja, ko a baya sun saba ba sa barci da wuri, sai kuma daga baya s**a koma da wuri suke barci, ko kuma sun koma yin barcin a lokacin da ba su saba yi ba''.

''Ko kuma a baya suna tashi barci da wuri, amma sai ka ga yanzu ba su tashi sai lokaci ya ja, to ya k**ata ka zurfafa bincike'', in ji shi.

4) Chanji a cin abinci

Idan yaro ya fara shaye-shaye, cin abinsa ma kan sauya a cewar jami'in na NDLEA.

''Idan a baya ka san ɗanka ko 'yarka ba mai yawan cin abinci ba ce, sai kuma daga baya ka fahimci sun ƙara yawan abincin da suke ci, ko kuma baya suna da yawan ci, amma daga baya s**a rage ci, to nan ma ya k**ata ka bincika''.

5) Yawan ɓatan abubuwa a gida

Yawan ɓatan abubuwa a gida na daga cikin alamun da za ka iya zargin ɗanka ko 'yarka sun fara shaye-shaye, musamman idan ba shi da sana'ar.

"Yau an ajiye naira 50 ko 100 ta ɓata ba a ganta ba a cikin gida, gobe ma haka, to yana da kyau ka binciki 'yayanta'', in ji Abdullahi Sardauna.

Jami'in na NDLEA ya ce abubuwan da yara s**a fi sata a gida domin samun na shaye-shaye sun haɗa da abubuwan amfani, ko sutura ko k**ar sarƙar gwal ko awarwaro masu tsada.

6) Ƙarya

Ƙarya na daga cikin alamomin da za ka gane ɗanka ko 'yarka sun fara shaye-shaye.

''Zai riƙa yin abubuwan da bai saba ba, kuma idan ka tambaye shi zai riƙa yi maka ƙarya, to daga nan ya k**ata ka gane akwai abin da yake ɓoye maka'', a cewar Abdullahi Sardauna.

7) Saurin fushi

Wannan alama ce da za ka iya gane ɗanka ko 'yarka sun fara shaye-sayen miyagun ƙwayoyi.

''Abu kaÉ—an sai ka ga yaro ya fusata yana faÉ—a da abokansa ko da 'yan'uwansa ko da mutanen gari'', in ji Abdullahi Sardauna.

8) Jin haushin jami'an tsaro

Wannan ma wata alama ce da ke nuna cewa ɗanka ko 'yarka sun fara shaye-shaye a cewar jami'in hukumar yaƙi da miyagun ƙwayoyin.

''Za ka ga ko a talbijin ya ga jami'in tsaro, É—an sanda ko wani jami'in, sai ka ga yana fushi da shi, yana yawan zaginsa''.

9) Chanjin k**anni

Idan yaro ya fara shaye-shaye wasu da dama daga cikin k**anninsa za su sauya ba yadda aka san shi ba.

''Idan yaro fari ne , za ka ga ya fara rinewa yana komawa baƙi, fararen haƙoransa za su fara komawa baƙaƙe, fatarsa za ta fara tsagewa, musamman ƙafarsa, hannayensa za su koma baƙaƙe''.

10) Dawowa gida a makare

Na daga cikin alamomin yaro ya fara shaye-shaye ya riƙa dawowa gida a makare ba k**ar yadda ya saba a baya ba.

''Da ya saba da wuri yake dawowa gida, amma yanzu sai ka lura ba ya dawowa sai dare ya fara yi, to ya k**ata ka bincika''.

City are ready
25/01/2025

City are ready

Address

Gayawa Layin Gidan Alh Musa Dila Nasarawa Lga Kano State O
Kano
800001

Telephone

+2348034992065

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when El-hakimee Trust News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to El-hakimee Trust News:

Share