IRM Foundation

IRM Foundation About IRM Foundation
Founded in 2008 by Alh.

Ibrahim Rilwan Muhammad, IRM Foundation is a non-profit focused on improving humanity through:
✅ Health
✅ Education
✅ Agriculture
✅ Humanitarian Services

Motto:Making Life Better

IRM Foundation Ta Saka Manyan Jigo-Jigon APC na Kaduna ta Arewa Cikin Shirin Kiwon Lafiya na KADCHMAGidauniyar IRM Found...
22/12/2025

IRM Foundation Ta Saka Manyan Jigo-Jigon APC na Kaduna ta Arewa Cikin Shirin Kiwon Lafiya na KADCHMA

Gidauniyar IRM Foundation, ƙarƙashin jagorancin wanda ya kafa ta kuma mai ba Gwamnan Jihar Kaduna shawara na musamman kan harkokin jin kai, Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad, ta ɗauki nauyin saka manyan jigo-jigon jam’iyyar APC na Kaduna ta Arewa cikin shirin kiwon lafiyar jihar Kaduna, KADCHMA

Wannan shiri na daga cikin ƙoƙarin tallafawa manufofin Gwamnatin Jihar Kaduna wajen rage wa jama’a nauyin kuɗin kula da lafiya, tare da tabbatar da cewa al’umma, musamman ma mambobin jam’iyyar APC na Kaduna ta Arewa, suna samun ingantacciyar kulawa a asibitoci.

Yayin jawabin sa a wajen taron kaddamar da shirin, Alhaji Ibrahim ya jaddada muhimmancin haɗin kai da ɗaukar alhakin juna wajen samar da lafiyar al’umma. Ya ce:

“Lafiya dukiya ce, kuma gwamnati kaɗai ba za ta iya ɗaukar nauyin biyan bukatun kowa ba. Don haka akwai buƙatar masu hali su tashi tsaye wajen tallafawa kokarin gwamnati.”

Ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirye-shiryen jin kai da dama da IRM Foundation ke aiwatarwa, domin rage raɗaɗin matsalolin tattalin arziki da ake fuskanta a ƙasar. Haka kuma ya yi kira ga mambobin jam’iyya da su ci gaba da kasancewa tsintsiya madaurinki ɗaya, tare da jajircewa wajen ci gaban jam’iyyar da kuma goyon bayan sake zaɓar Gwamnan Jihar Kaduna Senator Uba Sani a lokacin da ya dace.

A nasa jawabin, shugaban ƙaramar hukumar Kaduna ta Arewa, Hon. Muhammad Gambo Zion, ya jinjinawa Alhaji Ibrahim bisa wannan gagarumin tallafi, tare da kira ga sauran manyan jami’an jam’iyyar da su ƙara ƙaimi da tsare-tsaren da za su inganta walwala da jin daɗin mambobin jam’iyya.

Wasu daga cikin waɗanda s**a amfana da shirin sun bayyana godiyarsu ga IRM Foundation, tare da yin alkawarin ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a zaɓen shekara ta 2027.

21/12/2025

Jawabin Mai Girma Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad, mai ba Gwamnan Jihar Kaduna shawara kan harkokin jin kai kuma shugaban gidauniyar IRM Foundation, a wajen taron Iyayen Jam’iyyar APC na karamar hukumar Kaduna ta Arewa, wanda aka gudanar a yau a Stonhedge Hotel, Bank Road, cikin garin Kaduna.

Alhaji Ibrahim Rilwan Ya Halarci Taron Iyayen Jam’iyyar APC Na Karamar Hukumar Kaduna ta ArewaMai ba Gwamnan Jihar Kadun...
21/12/2025

Alhaji Ibrahim Rilwan Ya Halarci Taron Iyayen Jam’iyyar APC Na Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa

Mai ba Gwamnan Jihar Kaduna shawara kan harkokin jin kai, kuma shugaban gidauniyar IRM Foundation, Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad, ya halarci taron Iyayen Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, wanda ya gudana a yau a Stonehedge Hotel, Bank Road, cikin garin Kaduna.

Shugaban Iyayen Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, Hon. Aminu Abdulmumin Zaria, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna hanyoyin da za su ci gaba da marawa Gwamnan Jihar Kaduna baya, tare da goyon bayan manyan shirye-shirye da tsare-tsaren ci gaba da gwamnati ta sanya a gaba domin amfanin al’umma.

Ya kara da cewa irin wannan taro na kara karfafa zumunci, hada kai da kuma inganta fahimtar juna a tsakanin shugabanni da mambobin jam’iyyar domin tabbatar da dorewar ci gaba a jihar.

IRM Foundation Ta Rabawa Mutane 1,040 Tallafi a Kaduna ta ArewaGidauniyar IRM Foundation ƙarƙashin jagorancin mai ba Gwa...
21/12/2025

IRM Foundation Ta Rabawa Mutane 1,040 Tallafi a Kaduna ta Arewa

Gidauniyar IRM Foundation ƙarƙashin jagorancin mai ba Gwamnan Jihar Kaduna shawara kan harkokin jin kai, Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad, ta gudanar da shirin rabon tallafi ga al’umma 1,040 a Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa.

Tallafin ya haɗa da inshorar lafiya ta KADCHMA, buhunan shinkafa, takin zamani na noma, shirin koyar da sana’o’in hannu, tare da ba da kuɗin jari domin taimakawa mutane su farfaɗo da sana’o’insu da kuma inganta tattalin arzikin gidajensu.

Da yake jawabi yayin taron, Daraktan Gidauniyar IRM, QS. Anas Muhammad, ya bayyana cewa manufar gudanar da shirin ita ce tallafa wa manufofin jin kai na gwamnatin Malam Uba Sani, tare da sauƙaƙa wa jama’ar Jihar Kaduna matsalolin rayuwa.

Shi ma Shugaban Sashen Yaɗa Manufofin Gidauniyar, Alhaji Kabir Muhammad Kabir Mohammed Babasidi ya bayyana cewa zuwa yanzu sun aiwatar da irin wannan tallafi a kananan hukumomi biyar a fadin jihar, tare da tabbatar da cewa za su ci gaba da wannan aiki domin tallafawa jama’a.

A nasa ɓangaren, Shugaban Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, Hon. Muhammad Gambo Zion, ya nuna farin cikinsa tare da bayyana cewa tallafin ya zo a daidai lokacin da ake bukata. Ya yi kira ga sauran masu hannu da shuni su kwaikwayi irin wannan aikin alheri domin rage radadin talauci a cikin al’umma. Ya kuma miƙa godiya ta musamman ga IRM Foundation bisa wannan gagarumin taimako.

5th December 2025JUMA’AT MESSAGEFrom: Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad (IRM)CEO, IRM FoundationHonorary Special Adviser on...
05/12/2025

5th December 2025
JUMA’AT MESSAGE
From: Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad (IRM)
CEO, IRM Foundation
Honorary Special Adviser on Humanitarian Affair to the Executive Governor of Kaduna State

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh.

On this blessed day of Juma’at, I extend my heartfelt greetings and prayers to the entire Muslim Ummah. May the peace and mercy of Allah (SWT) be upon every home, every family, and every community.

As we gather for today’s congregational prayers, let us renew our commitment to faith, unity, kindness, and service to humanity. Juma’at is a reminder of our responsibility to uphold justice, compassion, and brotherhood. May Allah strengthen our hearts with sincerity, increase us in knowledge, and guide us on the straight path.

Let us remember those in need, the sick, the orphans, the less privileged, and those facing challenges. May Allah ease their affairs and grant relief to all who call upon Him.
May He bless our leaders with wisdom, protect our state and nation, and grant us lasting peace, progress, and stability.

On behalf of IRM Foundation, we reaffirm our commitment to supporting education, empowering communities, and promoting the welfare of every citizen, especially the most vulnerable.

May Allah accept our prayers, forgive our shortcomings, and fill our lives with tranquility and blessings.
Ameen Ya Rabbal ‘Alameen.

Juma’at Mubarak to you all.

Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad (IRM)
CEO, IRM Foundation
Honorary Special Adviser to the Kaduna State Governor

Sakon Zagayowar Ranar Haihuwa ga Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad(Shugaban IRM Foundation)Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad,A...
28/11/2025

Sakon Zagayowar Ranar Haihuwa ga Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad
(Shugaban IRM Foundation)

Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad,
A wannan rana ta musamman, muna taya ka murnar zagayowar ranar haihuwarka. Ka kafa tarihin da yawancin mutane basa da ƙarfin hali ko jajircewa su kafa. Aiki ba magana ba, shi ya fi bayyana mutum, kuma aikinka a IRM Foundation ya riga ya tabbatar da kai mutum ne da ke maida al’umma gaba da zuciya ɗaya, ba don yabo ba, sai don alhakin da kake ji a ranka.

Allah Ya ƙara maka tsawon rai mai amfani, ya ba ka ƙarfi da nisan hangen da za su ci gaba da tura wannan gidauniya zuwa mataki mafi girma. Mu kuma muna fatan ka cigaba da kasancewa abin koyi ga matasa, da jagora wanda ba ya tsoron yanke shawara mai amfani — ko da kuwa tana da wuya.

Muna yi maka fatan alkhairi a yau da dukkan kwanakin da ke tafe.

Happy Birthday, Sir.
Allah Ya albarkace ka. 🎉

28/11/2025

Gidauniyar IRM Foundation Ta Rabawa Yaran Makaranta Takardu, Jakunkuna da Littattafai

24/11/2025

IRM Foundation at the support the organizers with 1 Million Naira

19/11/2025

A lokacin da Alhaji Kabir Mohammed Babasidi tare da wasu mukarraban IRM Foundation suke karɓar lambar yabo da Makarantar Aisha Ameer Health Care Institute ta bawa shugaban gidauniyar Alhaji Ibrahim Rilwan Muhammad mai bawa Gwamnan Jihar Kaduna Shawara Kan Harkokin Jin Kai

17/11/2025

Taron Yaye Dalibai 50 Da Gidauniyar IRM Foundation Ta Dauki Nauyin Karatunsu

An gudanar da bikin yaye dalibai 50 a makarantar Aisha Ameer Health Care Institute, Rigasa – Kaduna, a yau Asabar. Waɗannan dalibai su ne waɗanda IRM Foundation ta ɗauki nauyin karatunsu gaba ɗaya ƙarƙashin jagorancin Alh. Ibrahim Rilwan Muhammad, mai ba Gwamnan Kaduna shawara kan harkokin jinƙai.

17/11/2025

IRM Foundation

Address

A3 Gombe Road
Kaduna
800211

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when IRM Foundation posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share