07/05/2025
KUNDIN RAYUWATA...
Sunana Usman, ni ɗan garin tsafe ne, a jihar Zamfara. Ko zan manta komi ba zan manta lokacin da nake da shekaru takwas a rayuwa ba, lokacin Damina ne, ƙamshin ƙasa da yabanya ya sa rayuwar ta ke da matuƙar daɗi a lokacin. Babana ke riƙe min hannu a duk lokacin da zai kai ni makaranta, yana mai tsantseni Kar na shiga cikin taɓo ko na ɓata Kaya da ƙasa.
Ranar kamar kullum ya ce "Usman ka yi karatu da kyau sannan ka zama mai gaskiya hakan zai sa ka zama nagari"
Ya kan faɗi haka ne da murmushinsa da ba zan taɓa mantawa ba.
"Toh Babana" shine amsar da na bashi, haka ya kai ni har ajinmu ya tafi yana ɗaga min hannu, ashe ranar ne zan masa gani na ƙarshe.
An fito break ne baffa na ya zo ya ɗauke ni, ashe mota ta buge Babanmu mai motar ya tsere, a kan idona aka sanya shi a rami aka rufe aka ce in tsaya in masa addu'a.
Ban fahimci giɓin da na samu ba sai da na dena zuwa makaranta, abinci ya nemi ya gagare mu, ƙarshe dai awannin da ya kamata in yi a aji su nake yi bakin tasha ina siyar da wake da shinkafa
Rayuwarmu na tafiya, kullum maganar babana na min yawo amma ta ina zan cika masa burinsa yayin da mu ke neman na abinci. Kwatsam Allah ya hada ni da wani mutumi daga neman canji a tasha, shi ya hada ni da ƴar uwarsa mamba a gidauniyar Nisaau Ahlil Jannah Charity Foundation, cikin ikon Allah aka ba ni form na cika su ka sani a makaranta su na biya min kudin makaranta.
Ba zan iya fadin farincikin da muka shiga ba ni da mahaifi na da ƴan uwana. Karatu na bai tsaya a primary ba, yanzu haka ina jss 3 na makarantar sakandire, kuma ba a taɓa tsallake term ba a biya min ba. A duk lokacin da na rubuta sunana sai na sha na yi godiya ga NAJCF, don su ne silar.
Ya mai karatu,
Ban san daga ina kake ba, ban san sunanka ba amma na san kana da zuciyar da za ta taimaka min da yara irina da ke karkashin Education sponsorship na Nisaau Ahlil Jannah Charity Foundation, da kaɗan din da kuke sanyawa na ɗauki hanyar cika burina na son zama injiniya.
Sadakar da kuke sanyawa a 0334993079, Nisaau Ahlil Jannah cha. Fdn, Gtbank ne ta zama silar tseratar da ni ta kuma canza rayuwata.
Allah ya fi mu yabawa ya muku tanadi mai girma da alheri a duniya da ƙiyama.