Alkalam Authors, Kaduna State

Alkalam Authors, Kaduna State Kungiyar Marubuta ta Jihar Kaduna da aka kafa domin raya adabi da karfafa matasa

Alƙalam na gayyata!
16/04/2026

Alƙalam na gayyata!

Waɗannan su ne wasu daga cikin hotuna da aka ɗauka bayan kammala taron tattaunawa na Kungiyar marubuta ta Alkalam Author...
06/04/2026

Waɗannan su ne wasu daga cikin hotuna da aka ɗauka bayan kammala taron tattaunawa na Kungiyar marubuta ta Alkalam Authors, Kaduna State, wanda ya gudana a ofishinta dake Oyo Road, cikin garin Kaduna.

A yayin taron, an tattauna muhimman tsare-tsare da manufofi da ƙungiyar ke da su, musamman waɗanda ake sa ran cimmawa a cikin watanni masu zuwa. Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan inganta harkar rubuce-rubuce, haɗin kai tsakanin mambobi, da kuma bunƙasa harshen Hausa a matsayin ginshiƙin sadarwa da al’adu.

A ƙarshe, ƙungiyar Alkalam Authors ta miƙa tambaya ga al’umma:

“Shin kana alfahari da yarenka?”

Jin kadan da kammala taron wata wata na Ƙungiyar Alkalam ta jihar Kaduna.
09/02/2026

Jin kadan da kammala taron wata wata na Ƙungiyar Alkalam ta jihar Kaduna.

An kammala taron wata-wata na Ƙungiyar Marubuta ta Alkalam ta Jihar Kaduna tare da bada lambar girma ga 'Yar Kungiyar Fa...
04/01/2026

An kammala taron wata-wata na Ƙungiyar Marubuta ta Alkalam ta Jihar Kaduna tare da bada lambar girma ga 'Yar Kungiyar Fadila Lamido da ta ci gasar Hikayata ta BBC Hausa.

Member din Kungiyar Marubuta ta ALKALAM Fadila Lamido ce ta daya a gasar Hikayata ta bana. Faɗila Lamiɗo daga jihar Kadu...
11/12/2025

Member din Kungiyar Marubuta ta ALKALAM Fadila Lamido ce ta daya a gasar Hikayata ta bana.

Faɗila Lamiɗo daga jihar Kaduna.

Ta yi karatu a Kaduna, sannan tana da shaidar difloma, kuma matar aure da ƴaƴa.

Labarin "Tsalla Ɗaya" da marubuciyar ta rubuta ne ya zama gwarzon Hikayata ta bana.

Ta samu kyautar naira miliyan ɗaya da shaidar karramawa.

An kammala taron Kungiyar Marubuta ta Alkalam na wannan watan a Kaduna
08/12/2025

An kammala taron Kungiyar Marubuta ta Alkalam na wannan watan a Kaduna

An kammala taron Alkalam Authors na wata wata
02/11/2025

An kammala taron Alkalam Authors na wata wata

Kungiyar Marubuta ta Alkalam Kaduna Ta Ziyarci FRCN KadunaA yau Laraba, kungiyar Marubuta ta Alkalam Kaduna ta kai ziyar...
24/09/2025

Kungiyar Marubuta ta Alkalam Kaduna Ta Ziyarci FRCN Kaduna

A yau Laraba, kungiyar Marubuta ta Alkalam Kaduna ta kai ziyarar ban girma zuwa gidan rediyon FRCN Kaduna, inda ta gana da Shugaban kula da Karama FM, Alhaji Abdulrahman Nuhu Bello.

Shugabar kungiyar, Hajiya Umma Muhammad Rimaye, ta jagoranci tawagar inda ta bayyana cewa manufar wannan ziyara ita ce:
Sake farfado da alakar dake tsakanin kungiyar da gidan rediyo na Karama. Tattaunawa kan yadda za a ƙara zamanantar da ɗaba’in Hausa a wannan zamani.

Wannan mataki ya nuna yadda kungiyar ke ci gaba da jajircewa wajen tallafawa ci gaban harshen Hausa da kuma haɗa kai da kafafen yaɗa labarai domin ƙarfafa al’adu.

30/08/2025

Kungiyar Marubuta ta Alkalam Ta Gudanar Da Taron Karshe Wata a Kaduna

A yau, Asabar 30 ga watan Agusta, kungiyar Marubuta ta Alkalam Kaduna karkashin jagorancin Hajiya Umma Muhammad Rimaye ta gudanar da taron tattaunawa a ofishin Amana Press da ke titin Oyo Road, Kaduna.

Taron ya mayar da hankali ne kan muhimman batutuwa da kungiyar ke fatan aiwatarwa nan gaba domin inganta harkokin rubutu da bunkasa harshen Hausa.

A jawabinta, shugabar kungiyar, Hajiya Umma Muhammad Rimaye, ta jaddada cewa kungiyar na bude kofa ga duk wani marubuci ko mai sha’awar rubutu da ke son bayar da gudummawa wajen raya yaren Hausa da ci gaban adabi.

Kungiyar Marubuta ta Alkalam Ta Gudanar Da Taron Karshe Wata a KadunaA yau, Asabar 30 ga watan Agusta, kungiyar Marubuta...
30/08/2025

Kungiyar Marubuta ta Alkalam Ta Gudanar Da Taron Karshe Wata a Kaduna

A yau, Asabar 30 ga watan Agusta, kungiyar Marubuta ta Alkalam Kaduna karkashin jagorancin Hajiya Umma Muhammad Rimaye ta gudanar da taron tattaunawa a ofishin Amana Press da ke titin Oyo Road, Kaduna.

Taron ya mayar da hankali ne kan muhimman batutuwa da kungiyar ke fatan aiwatarwa nan gaba domin inganta harkokin rubutu da bunkasa harshen Hausa.

A jawabinta, shugabar kungiyar, Hajiya Umma Muhammad Rimaye, ta jaddada cewa kungiyar na bude kofa ga duk wani marubuci ko mai sha’awar rubutu da ke son bayar da gudummawa wajen raya yaren Hausa da ci gaban adabi.

Address

No. 1 Dendo Road
Kaduna
2348

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alkalam Authors, Kaduna State posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share