12/05/2026
IBTILA'I: Matashi ɗan jihar Kano ya yanke gaban sa a Libya
Wani matashi ɗan asalin jihar Kano da aka baiyana sunan sa da Sani, ɗan unguwar Tukuntawa da ke ƙaramar hukumar Kumbotso, ya yanke gaban sa a ƙasar Libya, inda ya tafi domin neman kuɗi.
Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa matashin ya aikata hakan ne sakamakon karuwar ƙwaƙwalwa da ya kamu da ita a can ƙasar ta Libya.
Da ya ke shaidawa wannan jarida labarin da ya faru, kakakin ƙungiyar Northern Nigerian Organization (NNO), ƙungiyar ƴan Arewacin Najeriya mazauna Libiya, Abba Na-Gaida Fagge ya ce matashin ya samu larurar ƙwaƙwalwa yana watannin baya.
A cewar Fagge, kafin ya yanke gaban nasa, sun samu labarin cewa matashin ya tuka motar katafila a kamfanin da ya ke aiki, inda ya rushe wani gini, lamarin da ya sa mahukunta a kamfanin su ka bada umarnin killace shi.
Ya kara da cewa bayan an killace matashin ne sai kuma ba a san ya aka yi ba, sai ji aka yi ya na ihu, inda ya kara da cewa ko da aka zo aka duba sai aka gan shi kace-kace cikin jini.
"Bayan an kira mu, mu na zuwa ya rike ni wando da duk jini. Muna dubawa mu ka ya yanke gaban sa saura kadan ya rage ya fice daga jikin sa. Wannan lamari ya tayar mana da hankali," in ji Fagge.
Ya kara da cewa basu san me ya same.shi har ta kai ga ya samu larurar ƙwaƙwalwa na, sai dai kuma Fagge ya kara da cewa tuni su ka haɗa kuɗi a junansu su ka kai shi asibiti.
"Yanzu haka aiki za a yi masa a asibitin tunda gaban nasa bai karasa gutsirewa ba."
Ya kuma koka da cewa tun farkon fara ciwon nasa s**a sanar da ofishin jakadancin Nijeriya na Libya amma basu dauki wani mataki ba.
Ya kara da cewa yanzu dai matashin ya na asibiti ya na samun kulawar likitoci, inda ya ce sun sanar da ofishin jakadancin Nijeriya don dawo da shi gida Kano.
" Idan kuma hakan bai samu ba, za mu hada kudi-kudi mu dauki nauyin dawowar da a jirgi zuwa gida don a yi masa magani na ciwon ƙwaƙwalwar ta da," in ji Fagge.
~ Daily Nigerian