02/02/2026
Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh.
Da farko muna godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki, wanda Ya h**e mana zuciya da tausayi, Ya kuma umarce mu da taimakon marayu da marasa galihu. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Shugaban halitta Annabi Muhammad (SAW), wanda ya kasance mafi tausayi ga marayu, har ya ce: “Ni da mai kula da maraya muna tare a Aljanna kamar haka” sai ya nuna yatsunsa guda biyu.
Yan uwa maza da mata,
Maraya ba wai kawai yaro ne da ya rasa mahaifi ko mahaifiya ba; maraya yaro ne da ya rasa garkuwar rayuwa, ya rasa jagora, ya rasa wanda zai tsaya masa a lokacin bukata. Amma duk da haka, maraya yana da mafarki, yana da buri, yana da basira da hazaka kamar kowane yaro a cikin al’umma.
Babbar matsalar da marayu ke fuskanta a yau ita ce rashin damar samun ingantaccen ilimi. Yaro maraya na iya zama likita, malami, lauya ko shugaba, amma talauci da rashin tallafi na iya katse wannan tafiya tun daga tushe. Idan aka hana yaro ilimi, an hana shi makoma; idan aka taimaka masa da ilimi, an gina al’umma baki daya.
A nan ne rawar AA Qurami Orphans Support Organisation take bayyana. Wannan gidauniya ba wai tana ciyar da marayu kadai ba, tana tufatar da su ko kula da lafiyar su kawai ba; tana gina rayuwa ne ta hanyar ilimi. Tana biyan kudin makaranta, tana samar da kayan karatu, tana karfafa zuciyar marayu su ji suna da daraja kuma suna da makoma mai kyau...
Ya jama’a,
Duk littafin da aka saka a hannun maraya sadaka ce, duk kudin makarantar da aka biya masa ibada ce, duk murmushin da muka janyo masa lada ne a wurin Allah. Taimakon ilimin maraya ba ya lalacewa, domin ilimi gadon rayuwa ne da yake bin mutum har kabari.
Mu tuna cewa, wata rana mu ma za mu tsaya gaban Allah, za a tambaye mu: me muka yi da damar da aka ba mu? Shin mun taimaki marayu, ko mun juya baya? Shin mun gina rayuka, ko mun yi shiru muna kallo?
Saboda haka, muna kira ga masu hannu da shuni, ‘yan kasuwa, malamai, da duk mai zuciyar tausayi: ku tallafa wa AA Qurami Orphans Support Organisation. Ku bayar da duk abin da kuka iya kudi, lokaci, shawara ko addu’a, domin ceto makomar marayu ta hanyar ilimi.
A karshe, muna rokon Allah Ya saka wa duk wanda ya taimaka wa marayu da alheri, Ya yalwata masa arziki, Ya kare shi da iyalansa, Ya kuma haɗa mu tare da Annabi (SAW) a Aljannatul Firdaus.
Wassalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh.