13/04/2026
*KODA KAI NE MAFI HAZAKA, IDAN KANA WURI MARA KYAU BAZA A SAN DARAJARKA BA*
Mutane da yawa suna zargin kansu da rashin sa'a ko rashin iya fafutuka, ba tare da sun lura cewa asalin matsalar ba daga su take ba. Koda kai ne kafi kowa kaifin basira a duniya, idan ka dasa kanka a cikin mutanen da basu san kimarka ba, wallahi a banza zaka tsufa.
Ga abubuwa guda biyar da zasu tabbatar maka cewa kana cikin mutanen da ya kamata ka gaggauta canzawa domin tsiratar da makomarka:
1. Suna Kashe Maka Kwarin Gwiwa: Idan duk lokacin da ka kawo sabon tsarin neman kudi ko wata shawarar ci gaba, sai su kawo maka dalilan da zasu nuna maka cewa abin ba zai yiwu ba. Suna amfani da tsoron dake zukatansu wajen dake maka gwiwa. Dole ka canza su kafin su mayar da kai raggo.
2. Basu Girmama Jajircewarka: Kana fita tun asuba kana zage damtse neman halas dinka, amma a wajensu abin dariya ne saboda aikin karfi ne ko sana'a ce karama. Mutumin da bai san zafin neman na kansa ba, ba zai taba girmama kwazon da kake yi ba, sai dai ya kawo maka cikas.
3. Babu Wani Ci Gaba : Ka duba shekaru biyu ko uku baya, idan har babu wani sabon ilimi, dabarar kasuwanci, ko rufin asiri da ka samu a dalilin zamanka a wannan wurin ko a cikin wadannan mutanen, to lallai kasar da ka shuka irin ka bata da taki. Fita ka nemi inda ake maganar ci gaba.
4. Suna Amfani Da Kai Ne Kawai: Darajarka tana fitowa ne a wajensu kawai idan suna da wata matsala da kake da mafitarta. Da zaran ka warware musu damuwarsu ko bukatarsu ta biya, sai su watsar da kai a gefe. Wannan ba nuna kima ba ne, zalunci ne da amfani da basirar mutum a banza.
5. Kana Rasa Natsuwar Zuciyarka: Duk wurin da zaka zauna kaji kullum kana cikin fargaba, bacin rai, ko zargin kanka cewa baka da amfani, wallahi wannan wurin ba naka ba ne. Natsuwa ita ce asalin mizanin samun kudi, a duk inda babu ita, babu arziki ko ka yi fafutuka har sai ka mutu.
Idan har zaka dauki matakin canza wurin zama ko abokan mu'amala zuwa inda ake yaba maka, zaka yi mamakin yadda kofofin nasara zasu bude maka cikin kankanin lokaci. Ka daina yi wa makafi bayanin kyan launi.
Allah ya raba mu da mutanen da zasu rage mana daraja.
Maiunguwa Ibrahim Z***r Al-kampaly Kampala