12/03/2026
Allah muke roko da Ya Muna jagora
ANNABI NA JAGORANTAR MUTANE CIKIN SALLAR TAHAJJUDI:
1. Wahyin Hadithi ya tabbatar da cewa Annabi mai tsira da amincin Allah yana yi wa al’ummar musulmi maza da mata limancin sallar tahajjudi cikin wasu darairai a goman karshe na Ramadan a cikin masallacinsa; wannan shi yake tabbatar da cewa mustahabbibi ne maza da mata su je masallaci su yi tahajjudi a cikin jama’a; kamar yadda Imam Ibnu Khuzaimah yake cewa a cikin sahihinsa 3/339. Tabbas rashin zurfafa nazari ne yake sawa wani ya ce: yin sallar tahajjudi a ɗaiɗaiku a cikin gidaje a goman ƙarshen Ramadan shi ne ya fi kyau!!
2. Ga Hadithin da yake nassi ne ƙarara a kan cewa Annabi mai tsira da amincin Allah yana yi wa al’ummar musulmi maza da mata limancin sallar tahajjudi a cikin masallacinsa a cikin wasu darairan goman ƙarshe na Ramadan:
روى ابو داود: 1377, والترمذي: 806, والنسايي: 7706, وابن ماجه: 1327, واحمد:21447, واين خزيمة:2206, والبزار:4042, وعبد الرزاق:7706 بسند صحيح عن ابي ذر الغفاري رضي الله عنه قال: ((صمنا مع رسول الله صلى الله عليه واله وسلم رمضان فلم يقم بنا شييا من الشهر حتى بقي سبع، فقام بنا حتى ذهب ثلث الليل، فلما كانت السادسة لم يقم بنا، فلما كانت الخامسة قام بنا حتى ذهب شطر الليل فقلت: يا رسول الله لو نفلتنا قيام هذه الليلة؟ قال: فقال: ان الرجل اذا صلى مع الامام حتى ينصرف حسب له قيام ليلة. قال: فلما كانت الرابعة لم يقم، فلما كانت الثالثة جمع اهله ونساءه والناس، فقام بنا حتى خشينا ان يفوتنا الفلاح)).
3. Allah muke roƙon Ya taimake mu Ya cusa mana son yin riƙo da sunnonin Annabinmu cikin aƙida da ibada da kuma mu’amala. Ameen.