28/09/2025
Markazu Ahlis Sunnah Wal Jama'ah - Gombe - Nigeria:
*Markazu Ahlis Sunnah Wal Jama'ah - Gombe - Nigeria* Cibiyace ta musulunci (wato Islamic Centre) ta take gudanarwan ayyukan addini musamman karantarwa bisa tsarin Alqur'ani da Sunnah akan tafarkin Salafus Salih wanda tushenta na aqidah ne, aqidar Ahlus Sunnah Wal Jama'ah (Assalafiyyah).
Mun qirqiri wannam cibiyar ce don ciyar da aqidar Ahlus Sunnah Wal Jama'ah cigaba wanda muka kawo waensu ayyukan da muke gabatarwa kamar karantarwa da sauran abubuwa kamar:
1️⃣ Ofisoshi
Ofishin Imam ko Sheikh wato Director ko Chairman na duka markazin
Da Ofishin gudanarwa (Management office).
Da Ofishin kula da al’umma (Community services office).
Da Ofishin bada shawara (Counseling),wanda shine abu na farko da zamu fara kawowa insha Allah.
2️⃣ Masallaci (Wurin salla)
Domin gudanar da sallah 5 cikin yini da juma'a da sauran ibadu wanda ya had'a sallar maza da mata da wurin tsarki (wudu area) na maza da na mata, wanda shine abu na biyu da zamu kawo insha Allah a Wannanm Markazin.
3️⃣ Makaranta (Islamic School / Madrasa da kuma Makarantar Boko/Western/Secular Education )
Koyar da Qur'ani da tajweed.
Koyar da Hadisi, Fiqhu, Tauhidi, da sauran fannoni na addini da darussa na yara da manya mata da maza koyar da larabci gyaran akida da tarbiyya da sauransu Da kuma ilimin boko ko ilimin zamani, kuma wannam shine abu na uku da zamu kawo Insha Allah.
4️⃣ Library da Publication, Research & Da’awa Unit wato d'akin karatu da Wurin Gidauniyar Ilimi da nazarin harkokin Musulunci Don shirye-shiryen da’awa da yaduwar ilimi da fiitar da wallafe-wallafe da da buga littattafan na Qur’ani da Sunnah, da sauran ilimummuka na da da na zamani da s**a dace da Musulunci, kuma wannam shine abu na hud'u da zamu kawo Insha Allah sabida buqatuwarmu zuwa gareshi da muhimmancinshi kuma markazinmmu zatafi mayar da hankali akan wannam fiye da komai insha Allah
5️⃣ University (Jami'a) wacce ake koyar da manyan d'alibai (advanced Students) kuma ake bayarda shed a (certification) na diploma da degree da masters da Ph. D da ma Professor da sauran sheda na ilimummuka akan courses na addini kamarsu Aqidah da Hadisi da Qur’ani da Fiqhu da sauran ilimummuka na addini da na zamani, kuma wannam shine abu na biyar da zamu kawo Insha Allah.
6️⃣ Dakin koyar da sana’o’i (Skills Center) don koyar sana’o’in hannu da na zamani kamar su dinki, tukwane, fasahar kwamfuta, koyar da kasuwanci, da sauransu da ma koyar da ilimin rayuwa (life skills), kuma wannam shine burinnmmu na shida insha Allah.
7️⃣ Media Station and Unit (kafofin sadarwa kamar gidan radio ko talabijin watau TV) don qara yad'a dawaa da cigaban addini, birane da qauyuka/karkara da lunguna da saquna a fad'in duniya, kuma wannam yana ma daga cikin manya manyan burukanmmu.
8️⃣ Court/Chambers/Counseling Room (kotu da dakin shawarwari da sulhu
Shawarwari na aure da sauran abubuwa kamar shawarwarin matasa.
9️⃣ Hospital /Clinic/Health Unit/First Aid (Asibiti da gurin jinyan marasa lafia da Wurin Tsabtace Jiki da Ayyukan temakon lafiya na farko)
Hijama (cupping).
Taimakon lafiya ga mabukata.
🔟 Community Service Center (Wurin taimako)
Raba abinci ga mabukata.
Taimakon marayu da zawarawa tallafi ga masu matsala da shirye-shiryen lafiya da agaji.
Banking na zakka da tallafi da sauransu.
1️⃣1️⃣ Dakin Taro (Conference/Multipurpose Hall) domin gudanar da:
Karatu da darussa
Da Taron iyaye da malamai
Da Taron biki da walima da sauransu.
1️⃣2️⃣ Islamic Bank and Financial Institution (Banki da gurin gudanarwan kud'ad'e me tsarin Musulunci).
1️⃣3️⃣ Tsarin samar da tsaro da Kyautata Wuri da Hisbah wanda duka munada burin kawowa insha Allah.
1️⃣4️⃣ Hostel da guest rooms wato d'akunan d'alibai na nesa da d'akunan kar6an baqi.
Muna waennam ayyukanne don neman sakamako me kyau me yawa da rabauta agurin Allah Ubangiji Maɗaukaki domin gina Markaz ko temakawa cigaban addini ko taimakawa wajen ƙarfafa ayyukan addini yana daga cikin ayyukan da ke da dimbin lada a duniya da lahira. Sabida
1. قال رسول الله صلى الله عليه وسلم "من سن في الإسلام سنة حسنة فله أجرها وأجر من عمل بها بعده، من غير أن ينقص من أجورهم شيء... “Duk wanda ya ƙirƙiro kyakkyawan (aiki) a Musulunci, yana da ladarsa, da kuma lada na duk wanda ya bi sawunsa har abada, ba tare da an rage ladar kowa ba.”
Muslim, Hadisi na 1017)
2. قال رسول الله ﷺ:
"من دلَّ على خيرٍ فله مثلُ أجرِ فاعلِه."
[رواه مسلم – الحديث رقم 1893]
“Wanda ya jagoranci wani alheri (ya nuna hanya ko ya kira wani zuwa alheri), yana da lada kamar na wanda ya aikata shi.”
3. قال رسول الله ﷺ:
"إذا مات الإنسان انقطع عمله إلا من ثلاثة: صدقة جارية، أو علم يُنتفع به، أو ولد صالح يدعو له."
[رواه مسلم – الحديث رقم 1631]
Manzon Allah ﷺ ya ce:
"Idan mutum ya mutu, dukkan ayyukansa sun yanke sai daga abubuwa uku:
Sadaqa me gudana,
Ko ilimi da ake amfani da shi,
Ko yaro nagari da ke yi masa addu’a."
4. قال رسول اللهﷺ: والله في عون العبد ما كان العبد في عون أخيه
Allah ya cikin temakon bawa matukqar bawa yana cikin temakon d'an uwanshi
(Bukhary da Muslim)
مَنْ كَانَ فِي حَاجَةِ أَخِيهِ، كَانَ اللَّهُ فِي حَاجَتِهِ، وَمَنْ فَرَّجَ عَنْ مُسْلِمٍ كُرْبَةً، فَرَّجَ اللَّهُ عَنْهُ كُرْبَةً مِنْ كُرَبِ يَوْمِ الْقِيَامَةِ، وَمَنْ سَتَرَ مُسْلِمًا، سَتَرَهُ اللَّهُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ
Duk wanda yake cikin biyan buƙatar ɗan'uwansa, Allah zai kasance cikin biyan buƙatarsa. Duk wanda ya rage wa musulmi wata damuwa, Allah zai rage masa damuwa daga damuwar ranar Kiyama. Duk wanda ya rufe (asirin) musulmi, Allah zai rufe asirinsa a ranar Kiyama
Bukhari da Muslim
أَحَبُّ النَّاسِ إِلَى اللَّهِ أَنْفَعُهُمْ لِلنَّاسِ
Mafi soyuwa a wajen Allah daga cikin mutane shi ne wanda yafi amfani ga mutane.
Sahih al-Bukhari (Hadisi na 6026) da Sahih Muslim
إِنَّ الصَّدَقَةَ لَتُطْفِئُ غَضَبَ الرَّبِّ
Lallai sadaka tana kashe fushin Ubangiji.
Sunan Ibn Mājah (Hadisi na 2431) – Hasan
أَحَبُّ الأَعْمَالِ إِلَى اللَّهِ سُرُورٌ تُدْخِلُهُ عَلَى مُسْلِمٍ، أَوْ تَكْشِفُ عَنْهُ كُرْبَةً، أَوْ تَقْضِي عَنْهُ دَيْنًا، أَوْ تَطْرُدُ عَنْهُ جُوعًا.
Mafi soyuwa daga ayyuka a wajen Allah shi ne farin ciki da ka sa wa musulmi, ko ka rage masa wata damuwa, ko ka biya masa bashi, ko ka kore masa yunwa.
Muslim
مَثَلُ الَّذِينَ يُنْفِقُونَ أَمْوَالَهُمْ فِي سَبِيلِ اللَّهِ كَمَثَلِ حَبَّةٍ أَنبَتَتْ سَبْعَ سَنَابِلَ فِي كُلِّ سُنبُلَةٍ مِّائَةُ حَبَّةٍ ۗ وَاللَّهُ يُضَاعِفُ لِمَن يَشَاءُ ۗ وَاللَّهُ وَاسِعٌ عَلِيمٌ
Misalin waɗanda suke ciyar da dukiyarsu a kan hanyar Allah, kamar irin hatsi da ya tsiro da kawuna bakwai, a kowace kawanar akwai ɗari. Allah yana ninka (lambar lada) ga wanda Yake so, kuma Allah Mai yalwa ne, Masani."
Suratul Baqarah, Aya ta 261.
Sabida haka duk wanda yasamu damar ire iren waencan ayyuka kada yayi wasa da damar, ko a wane hali kake ciki tabbas kana damar aikata haka ko sashen wani abu daga ciki ko temakon masu aiwatarwa ta hanyar qarfinka ko dukiyarka ko shawarinka ko kulawarka ko iliminka don yin tarayya acikin ladan.
Allah Ya sa mu kasance cikin masu taimakawa addini da ilimi da ibada. Ameen