19/02/2026
SAĆON TUNATARWA KAN HALIN DA MAKARANTAR GARIN KWAKWARE KE CIKI ZUWA GA SHUGABAN ĆARAMAR HUKUMAR FASKARI.
Bayan sallama da fatan Alkhairi ga dukkan shugabannin mu na Ćaramar hukumar mu ta Faskari, da ma jihar Katsina baki Éaya,
Ruwangodiya Development Society tana mai mika sakon gaggawa na tunatarwa ga hukumomin da ke kula da harkar ilimi na Ćaramar hukumar mu ta Faskari da Jahar Katsina baki daya dangane da mawuyacin halin da Makarantar garin Kwakware ke ciki a gundumar Ruwangodiya.
Wannan sako an rubuta shi ne biyo bayan ziyarar da kungiyarmu ta Ruwangodiya Development Society ta kai wa Shugaban Ćaramar hukumar Faskari, Hon. Sirajo Aliyu Daudawa, a lokacin baya, inda muka tattauna dashi akan matsalolin wannan makaranta waÉanda s**a hada da rashin matsugunni na dindindin musamman samar da gini na zamani da ya dace da yanayin koyo da koyarwa da kuma daukar malamai da ake matukar bukata domin tafiyar da makarantar yadda ya kamata.
An kafa makarantar ne shekaru biyar (4) da s**a gabata domin samar wa yara ilimi a yankin. Sai dai abin takaici, har yanzu makarantar ba ta da fili ballantana gini na dindindin. Dalibai na karatu ne a wani wuri na wucin gadi da makarantun Islamiyyu na gari s**a bayar, wanda su kan su wannan makarantu suna buĆatar gyara da kulawa ta musamman saboda a halin da take ciki yanzu yanayin ta bai dace ba kuma ba ya samar da ingantaccen yanayi na koyarwa da koyo. Ba kayan aiki na wajibi a makarantar.
Haka kuma, makarantar ba ta da malamai na dindindin ko na wucin gadi da gwamnati ta Éauka. Ayyukan koyarwa gaba daya suna hannun malamai waÉan da su ke yin wannan koyarwa fisabilillah, waÉan nan matasa suke sadaukar da lokacinsu da karfinsu domin cigaban alâummar su. Duk da cewa kokarinsu abin yabawa ne, amma ba za a iya dogaro da aikin malaman sa kai kaÉai ba wajen tabbatar da makomar ilimin yaranmu da Yankin mu ba saboda yau da gobe da wani lokacin koda suna son taimakawar ba dama saboda Ćila sun fita neman Abin rufawa kan su asiri.
Saboda haka muna sake kira ga:
1.Shugaban Ćaramar hukumar Faskari, Hon. Sirajo Aliyu Daudawa
2.Dan majalisar jaha na Katsina mai wakiltar Faskari, Hon. Sama'ila Mu'azu Bawa
3.Dan majalisar tarayya mai wakiltar Faskari/Kankara/Sabuwa a majalisar wakilai ta Najeriya, Hon. Shehu Dalhatu Tafoki
4.Sanata mai wakiltar Yankin Funtua a majalisar Dattawa, Sanata Muntari Dandutse
5.Kwamishinan Muhalli na Jihar Katsina, Hamza Sulaiman Sadaukin Kasar Hausa, kasancewarsa dan asalin karamar hukumar Faskari.
6. Gwamnatin Jihar Katsina ĆarĆashin maigirma Gwamna Umar Dikko RaÉÉa.
Mu na kira ga waÉan nan hukumomi da su cika alkawarin da su ka dauka na inganta rayuwar al'ummar su gami da duba wannan lamari na makarantar Garin kwakware B cikin gaggawa domin tabbatar da cewa makarantar ta samu matsugunni na dindindin, gine-gine masu inganci, da malamai na dindindin (mu na fatan in za a Éauka a Duba waÉan nan malamai na sa kai da s**a sadaukar da lokacin su dan tabbatuwar makarantar).
Sanin kowa ne Ilimi shi ne ginshikin cigaban kowace alâumma. Makarantar Kwakware B ita ce tubalin ilimi sauran garuruwa na kusa da su. kuma yin watsi da ita wannan makaranta yana nufin barazana ga makomar gaba Éaya ta yaran yankin. Alâummar Kwakware na da cikakken Ćłanci kamar kowanne yanki na Ćaramar hukumar Faskari dan haka mu na kira Cikin girmamawa da a yi laâakari da su a shirye-shiryen cigaba, musamman a bangaren ilimi.
Muna fatan shugabanni za su dauki wannan kira da muhimmanci tare da gaggauta daukar mataki na tabbatuwar wannan makaranta.
Sannan mu na tunatar da shugabanni cewa in aka kasa inganta rayuwar al'ummar mu to mu na nan riĆe da katunan zaÉen mu.
Allah ya taimaki al'ummar gundumar Ruwangodiya, Ćaramar hukumar Faskari, jahar Katsina da ma Najeriya baki Ćaya.
ÂŠď¸ Ruwangodiya Development Society (RDS)