RuwanGodiya Development Society RDS

RuwanGodiya Development Society RDS Non-profit Organization

The Ruwangodiya Development Society proudly extends its heartfelt congratulations to our esteemed brother, Idris Imran, ...
31/03/2026

The Ruwangodiya Development Society proudly extends its heartfelt congratulations to our esteemed brother, Idris Imran, on the successful completion of his National Youth Service Corps (NYSC). 🇳🇬

Your dedication, discipline, and unwavering commitment to national service stand as a testament to your character and have brought pride and honor to our entire community. This remarkable achievement signifies not just the completion of a national duty, but the beginning of a future filled with promise and opportunity.

As you have served your country with distinction, we pray that your efforts are rewarded with lasting prosperity, meaningful success, and abundant blessings. May the Almighty continue to guide your path and grant you excellence in all your future endeavors.

Once again, congratulations on this outstanding accomplishment.

©️ RuwanGodiya Development Society RDS

SAƘON BARKA DA SALLAHAssalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuhu,Kungiyar Ruwangodiya Development Society na miƙa saƙ...
20/03/2026

SAƘON BARKA DA SALLAH

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuhu,

Kungiyar Ruwangodiya Development Society na miƙa saƙon barka da Sallah ga daukacin al’ummar Ruwangodiya da kewaye.

Muna taya ku murnar kammala ibadar azumin watan Ramadan, tare da fatan Allah (SWT) Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana kurakuranmu, Ya kuma sanya albarka da zaman lafiya a cikin al’ummarmu.

A wannan lokaci na farin ciki, muna me ƙarfafa juna da mu ci gaba da riƙo da kyawawan halaye da muka koya a watan Ramadan na tausayi, haƙuri, taimakon juna, da son zaman lafiya.

Allah Ya maimaita mana wannan rana cikin ƙoshin lafiya, arziki da yalwar zaman lafiya.

Barka da Sallah!

RuwanGodiya Development Society RDS

SAØON BARKA DA SHAN RUWA GAMI DASAKON FAÊAKARWA.Assalamu Alaikum Gare ku al'ummar Ruwangodiya da kewaye barkan Ku da sha...
25/02/2026

SAØON BARKA DA SHAN RUWA GAMI DASAKON FAÊAKARWA.

Assalamu Alaikum Gare ku al'ummar Ruwangodiya da kewaye barkan Ku da shan ruwa, Allah ya karɓi ibadun mu, ya sa wannan wata ya zama watan Ƴantuwar mu daga wuta.

Kungiyar Ruwangodiya Development Society (RDS) na me mika sakon tunatarwa ga daukacin al’ummar gundumar Ruwangodiya da sauran al'ummar Musulmai baki ɗaya a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

Ramadan wata ne na rahama, gafara da ‘yantarwa daga wuta. Wata ne da Allah (SWT) Ya saukar da Alƙur’ani domin shiryar da bayinsa. Saboda haka, mu ƙara ƙaimi wajen:

1 Tsarkake zukatanmu daga hassada, ƙiyayya da gulma.
2 Yawaita karatun Alƙur’ani da zikiri.
3 Taimakon marasa galihu da kula da juna.
4 Haƙuri da juna da kyautata mu’amala.
5 Neman gafarar Allah dare da rana.

Mu yi amfani da wannan dama wajen gyara kanmu, iyalanmu da al’ummarmu baki ɗaya. Ramadan wata ne na sauyi da komawa ga Ubangiji cikin tawali’u da tsoronSa.

Muna roƙon Allah (SWT) Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya kawo zaman lafiya da cigaba a Ruwangodiya da ƙasa baki ɗaya.

Ramadan Kareem 🌙

Taken mu: Haɗin kai ,Cigaba da Ƙaunar Al’umma.

©️ RuwanGodiya Development Society RDS

24/02/2026

BARKA DA SHAN RUWA

Kungiyar Ruwangodiya Development Society (RDS) na miƙa saƙon barka da shan ruwa ga daukacin al’ummar Ruwangodiya, tare da yi wa Musulmai baki ɗaya fatan alheri da karɓuwar ibadu.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi azuminmu, Ya yafe mana kura-kuranmu, Ya kuma ba mu ikon ci gaba da ayyukan alheri bayan watan Ramadan. Allah Ya sanya wannan lokaci ya zama sanadin haɗin kai, zaman lafiya, da cigaban al’ummarmu.

Barka da shan ruwa. Allah Ya sada mu da alkhairi. 🤲

BARKA DA SHAN RUWAKungiyar Ruwangodiya Development Society (RDS) na miƙa saƙon barka da shan ruwa ga daukacin al’ummar R...
24/02/2026

BARKA DA SHAN RUWA

Kungiyar Ruwangodiya Development Society (RDS) na miƙa saƙon barka da shan ruwa ga daukacin al’ummar Ruwangodiya, tare da yi wa Musulmai baki ɗaya fatan alheri da karɓuwar ibadu.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi azuminmu, Ya yafe mana kura-kuranmu, Ya kuma ba mu ikon ci gaba da ayyukan alheri bayan watan Ramadan. Allah Ya sanya wannan lokaci ya zama sanadin haɗin kai, zaman lafiya, da cigaban al’ummarmu.

Barka da shan ruwa. Allah Ya sada mu da alkhairi. 🤲

SAƘON TUNATARWA KAN HALIN DA MAKARANTAR GARIN KWAKWARE KE CIKI ZUWA GA SHUGABAN ƘARAMAR HUKUMAR FASKARI.Bayan sallama da...
19/02/2026

SAƘON TUNATARWA KAN HALIN DA MAKARANTAR GARIN KWAKWARE KE CIKI ZUWA GA SHUGABAN ƘARAMAR HUKUMAR FASKARI.

Bayan sallama da fatan Alkhairi ga dukkan shugabannin mu na ƙaramar hukumar mu ta Faskari, da ma jihar Katsina baki ɗaya,
Ruwangodiya Development Society tana mai mika sakon gaggawa na tunatarwa ga hukumomin da ke kula da harkar ilimi na ƙaramar hukumar mu ta Faskari da Jahar Katsina baki daya dangane da mawuyacin halin da Makarantar garin Kwakware ke ciki a gundumar Ruwangodiya.

Wannan sako an rubuta shi ne biyo bayan ziyarar da kungiyarmu ta Ruwangodiya Development Society ta kai wa Shugaban ƙaramar hukumar Faskari, Hon. Sirajo Aliyu Daudawa, a lokacin baya, inda muka tattauna dashi akan matsalolin wannan makaranta waɗanda s**a hada da rashin matsugunni na dindindin musamman samar da gini na zamani da ya dace da yanayin koyo da koyarwa da kuma daukar malamai da ake matukar bukata domin tafiyar da makarantar yadda ya kamata.

An kafa makarantar ne shekaru biyar (4) da s**a gabata domin samar wa yara ilimi a yankin. Sai dai abin takaici, har yanzu makarantar ba ta da fili ballantana gini na dindindin. Dalibai na karatu ne a wani wuri na wucin gadi da makarantun Islamiyyu na gari s**a bayar, wanda su kan su wannan makarantu suna buƙatar gyara da kulawa ta musamman saboda a halin da take ciki yanzu yanayin ta bai dace ba kuma ba ya samar da ingantaccen yanayi na koyarwa da koyo. Ba kayan aiki na wajibi a makarantar.

Haka kuma, makarantar ba ta da malamai na dindindin ko na wucin gadi da gwamnati ta ɗauka. Ayyukan koyarwa gaba daya suna hannun malamai waɗan da su ke yin wannan koyarwa fisabilillah, waɗan nan matasa suke sadaukar da lokacinsu da karfinsu domin cigaban al’ummar su. Duk da cewa kokarinsu abin yabawa ne, amma ba za a iya dogaro da aikin malaman sa kai kaɗai ba wajen tabbatar da makomar ilimin yaranmu da Yankin mu ba saboda yau da gobe da wani lokacin koda suna son taimakawar ba dama saboda ƙila sun fita neman Abin rufawa kan su asiri.

Saboda haka muna sake kira ga:

1.Shugaban ƙaramar hukumar Faskari, Hon. Sirajo Aliyu Daudawa

2.Dan majalisar jaha na Katsina mai wakiltar Faskari, Hon. Sama'ila Mu'azu Bawa

3.Dan majalisar tarayya mai wakiltar Faskari/Kankara/Sabuwa a majalisar wakilai ta Najeriya, Hon. Shehu Dalhatu Tafoki

4.Sanata mai wakiltar Yankin Funtua a majalisar Dattawa, Sanata Muntari Dandutse

5.Kwamishinan Muhalli na Jihar Katsina, Hamza Sulaiman Sadaukin Kasar Hausa, kasancewarsa dan asalin karamar hukumar Faskari.

6. Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin maigirma Gwamna Umar Dikko Raɗɗa.

Mu na kira ga waɗan nan hukumomi da su cika alkawarin da su ka dauka na inganta rayuwar al'ummar su gami da duba wannan lamari na makarantar Garin kwakware B cikin gaggawa domin tabbatar da cewa makarantar ta samu matsugunni na dindindin, gine-gine masu inganci, da malamai na dindindin (mu na fatan in za a ɗauka a Duba waɗan nan malamai na sa kai da s**a sadaukar da lokacin su dan tabbatuwar makarantar).

Sanin kowa ne Ilimi shi ne ginshikin cigaban kowace al’umma. Makarantar Kwakware B ita ce tubalin ilimi sauran garuruwa na kusa da su. kuma yin watsi da ita wannan makaranta yana nufin barazana ga makomar gaba ɗaya ta yaran yankin. Al’ummar Kwakware na da cikakken Ƴanci kamar kowanne yanki na ƙaramar hukumar Faskari dan haka mu na kira Cikin girmamawa da a yi la’akari da su a shirye-shiryen cigaba, musamman a bangaren ilimi.

Muna fatan shugabanni za su dauki wannan kira da muhimmanci tare da gaggauta daukar mataki na tabbatuwar wannan makaranta.
Sannan mu na tunatar da shugabanni cewa in aka kasa inganta rayuwar al'ummar mu to mu na nan riƙe da katunan zaɓen mu.

Allah ya taimaki al'ummar gundumar Ruwangodiya, ƙaramar hukumar Faskari, jahar Katsina da ma Najeriya baki Ɗaya.

©️ Ruwangodiya Development Society (RDS)

🌙✨ RAMADAN MUBARAK ✨🌙Ruwangodiya Development Society (RDS) warmly extends its heartfelt Ramadan greetings to all the goo...
17/02/2026

🌙✨ RAMADAN MUBARAK ✨🌙

Ruwangodiya Development Society (RDS) warmly extends its heartfelt Ramadan greetings to all the good people of Ruwangodiya Ward and the entire Muslim Ummah.

May this blessed month of Ramadan bring peace to our homes, unity to our community, and prosperity to our land. May Allah (SWT) accept our fasting, prayers, sacrifices, and good deeds.

Let this sacred month strengthen our spirit of love, patience, charity, and togetherness as we continue working for the growth and development of our ward.

🌙 May Allah grant us forgiveness, mercy, and countless blessings.May He protect our families and our community.

Ramadan Kareem!
Ruwangodiya Development Society (RDS)

On behalf of the entire members of Ruwangodiya Development Society (RDS), we heartily congratulate the Kwai Community De...
31/01/2026

On behalf of the entire members of Ruwangodiya Development Society (RDS), we heartily congratulate the Kwai Community Development Association (KCDA) and the good people of Kwai on the successful approval of your request for the establishment of Pilot Junior Secondary School, Kwai, as approved by the Local Government Education Secretary.

This remarkable achievement is a clear testament to your commitment to educational development and community progress. Education remains the foundation of sustainable growth, and this milestone will undoubtedly shape a brighter future for the children and youth of Kwai community.

We particularly commend the youths of Kwai for their resilience, unity, and unwavering determination in standing firm for the development of their society. Your dedication and collective effort demonstrate that when youths rise with purpose, meaningful change is inevitable.

Ruwangodiya Development Society (RDS) celebrates this victory with you and prays that this new institution will grow in strength, excellence, and positive impact for generations to come.

Once again, congratulations on this laudable achievement.

©️ RuwanGodiya Development Society RDS

From everyone at Ruwangodiya Development Society RDS, we extend our New Year wishes, hoping this year fills our life wit...
01/01/2026

From everyone at Ruwangodiya Development Society RDS, we extend our New Year wishes, hoping this year fills our life with unending joy and happiness

Saƙon Taya murna ga Hazikan Ɗaliban Mu(Shukuranu Ɗayyabu, Ruƙayya Bara'u da Haruna Inuwa)A mamadin dukkan al'ummar Ruwan...
27/11/2025

Saƙon Taya murna ga Hazikan Ɗaliban Mu(Shukuranu Ɗayyabu, Ruƙayya Bara'u da Haruna Inuwa)

A mamadin dukkan al'ummar Ruwangodiya, kungiyar cigaban Ruwangodiya (RDS) na miƙa saƙon taya murna da jinjina ga Hazikan Ɗaliban Mu da su ka kammala karatun su a bangaren kiwon lafiya.

Haƙiƙa wannan mataki da ku ka taka mataki ne na farin ciki da alfahari gare mu baki ɗaya, Domin wannan ilimi wata fitila ce da ke haska makomar Garin mu da kewaye. Samun matasa ma su jajircewa da ƙwazo wajen neman ilimi shi ne yake nuna makomar kowacce al'umma. Dan haka Shukuranu, Haruna da Ruƙayya a yau mu na matukar farin ciki da ku sannan mu na jaddada murnar mu gare ku baki ɗaya, ku cigaba da jajircewa wajen karfafa kan ku wajen cigaba da zama jakadu na gari ga mutanen RUWANGODIYA.

Babban Abin farin cikin shine samun Ƴar uwa Ruƙayya a cikin waɗan nan zaratan ɗalibai, samun mace a fannin ilimi musamman na lafiya ba ƙaramin Abin murna da alfahari ba ne mu na fatan Ruƙayya ta zama madubi ga sauran ƴaƴa mata da su ke da burin yin ilmi mai zurfi anan gaba.

Mu na jinjina ga iyaye da yan uwan waɗan nan ɗalibai bisa ga jajircewar su da taimakon su akan karatun waɗan nan Matasa, haƙiƙa mu na godiya gare ku bisa wannan sadaukarwa mun gode da wannan kyautatawa ga al'ummar Ruwangodiya. A wannan gaɓar nake kira da roƙo ga sauran iyaye da su daure su rinƙa tallafawa ƴaƴa musamman mata wajen samun ilimi, mace mai ilimi jigo ce a cikin al'umma.

Kira da jan hankali zuwa ga sauran matasa masu tasowa: wannan ƙungiya ta mu tana ƙara kira ga matasan mu masu tasowa da su yi koyi da waɗan nan jajirtattun matasa wajen zage damtse wajen cigaba da Neman Ilimi na Addini da na zamani, ina so su sani makomar garin mu ta dogara ne kacokan ga Irin fikira da ƙwazon da matasan garin RUWANGODIYA za su yi wajen neman ilimi, Dan haka mu ke roƙon su da su ƙara bada himma a ɓangaren karatun su.

Shukuranu Ɗayyabu, Ruƙayya Bara'u da Haruna Inuwa Kungiyar mu na ƙara taya ku murna, Allah ya kawo babban Rabo.

Kungiyar Cigaban Ruwangodiya( RuwanGodiya Development Society RDS ).

CONGRATULATORY MESSAGE TO OUR EXEMPLARY SCHOLARS(Shukuranu Dayyabu, Rukayya Bara’u, and Haruna Inuwa)On behalf of the en...
27/11/2025

CONGRATULATORY MESSAGE TO OUR EXEMPLARY SCHOLARS
(Shukuranu Dayyabu, Rukayya Bara’u, and Haruna Inuwa)

On behalf of the entire community of Ruwangodiya, the Ruwangodiya Development Society (RDS) extends its warmest congratulations and profound admiration to our outstanding students who have successfully completed their studies in the field of health sciences.

This remarkable achievement is a source of immense pride and joy for us all. The knowledge you have attained stands as a beacon of hope, illuminating the path toward a brighter and more prosperous future for our community and its environs. The progress of any society rests on the commitment and intellectual strength of its youth; your dedication exemplifies this truth with admirable clarity.
Shukuranu, Haruna, and Rukayya, today we celebrate not only your accomplishments but also the promise you hold for the advancement of Ruwangodiya. We commend your perseverance and encourage you to continue embodying the values of discipline, excellence, and service as worthy ambassadors of our community.

We are especially proud to have our daughter, Rukayya, among these distinguished graduates. The success of a woman in the pursuit of knowledge particularly in the critical field of health is a significant achievement and a source of deep pride. We pray that Rukayya becomes an inspiring model for young girls who aspire to attain higher education in the years ahead.

Our heartfelt appreciation also goes to the parents and families of these graduates. Your unwavering support, sacrifice, and encouragement have played an essential role in shaping this success. We sincerely thank you for your contribution to the intellectual and social growth of Ruwangodiya.
At this moment, we call on all parents to continue supporting their children especially daughters in their educational journeys. An educated woman is a cornerstone of any thriving society.

A Call to Our Rising Generation:
We urge all upcoming youths to emulate the diligence and determination shown by these exceptional graduates. Your future and indeed the future of Ruwangodiya depends on your willingness to pursue both religious and modern education with seriousness and ambition. We encourage you to strengthen your resolve, deepen your commitment, and strive toward excellence.

Once again, we extend our heartfelt congratulations to
Shukuranu Dayyabu, Rukayya Bara’u, and Haruna Inuwa.
May this milestone be the beginning of even greater achievements.

RuwanGodiya Development Society RDS

Sakon Taya Murna daga Ƙungiyar Ruwangodiya Development Society.Ƙungiyar Cigaban Ruwangodiya (Ruwangodiya Development Soc...
09/11/2025

Sakon Taya Murna daga Ƙungiyar Ruwangodiya Development Society.

Ƙungiyar Cigaban Ruwangodiya (Ruwangodiya Development Society) na mika saƙon taya murna tare da nuna farin ciki zuwa ga dukkan ɗalibai maza da mata da s**a kammala saukar Alƙur’ani Mai Girma a yau a garinmu, abin ƙaunar mu,Ruwangodiya.

Wannan babbar nasara ba wai abu ne na alfahari gare ku kaɗai ba, tana zama abun girmamawa ga iyayenku, malamanku, da al’ummar Ruwangodiya gaba ɗaya. Himma, jajircewa da ɗa’a da kuka nuna wajen neman ilimin Alƙur’ani hujja ce ta karfin gwiwar da garin Ruwangodiya ya dade yana alfahari da shi, gari mai ɗumbin tarihi a cikin addini, ilimi, da kyawawan ɗabi’u.

Muna roƙon Allah Maɗaukaki (SWT) Ya saka muku da alheri, Ya faɗaɗa fahimtar ku ga kalmominSa(Kur'ani), kuma Ya sanya Alƙur’ani ya zama haske da zai zama jagora a rayuwarku. Haka kuma muna roƙonSa Ya ƙara wa sauran ɗalibai himma da ƙwazo su yi koyi da ku wajen neman ilimi na addini da na zamani.

Muna ƙara taya ku murna daga dukkan mu da ke Ƙungiyar Ruwangodiya Development Society nasararku abar alfaharinku ce, nasarar ku Abar alfaharinmu ce gaba ɗaya.

RuwanGodiya Development Society RDS

Address

Kofar Fada Street, RuwanGodiya
Faskari

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when RuwanGodiya Development Society RDS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share