30/07/2026
TARON TATTAUNAWA DA WAKILAN JAM'IYYAR ADC NA HADEJIA ZONE
A yau ne aka gudanar da taron tattaunawa domin bunƙasa tafiyar Jam'iyyar ADC tare da wakilan ƙananan hukumomin Hadejia Zone a garin Hadejia.
Taron ya samu halartar manyan jagororin jam'iyyar ADC na Hadejia Zone, ciki har da:
- Tsohon ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Birniwa/Guri/Kiri-Kasamma, tsohon Sanata, kuma Jagoran Jam'iyyar ADC na Hadejia Zone, Hon. Abdul'aziz Usman Turabu.
- Tsohon Shugaban Ƙaramar Hukumar Hadejia, Alhaji Ibrahim Muhammad Jaga.
- Tsohon ɗan Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Hon. Adamu Hassan Abunabo.
- Hon. Usaini Rally Hadejia, tare da sauran manyan jiga-jigan jam'iyyar.
Haka kuma, taron ya samu halartar 'yan takarar Majalisar Wakilai na Jam'iyyar ADC:
- Hon. Salisu Muhammad Birniwa, ɗan takarar Birniwa/Guri/Kiri-Kasamma.
- Wakilin Hon. Zakari Kafin Hausa, ɗan takarar Hadejia/Auyo/Kafin Hausa.
Sannan an samu halartar 'yan takarar Majalisar Dokokin Jihar Jigawa da wakilansu, waɗanda s**a haɗa da:
- Wakilin Hon. Umar Baffa Birniwa, ɗan takarar Birniwa.
- Hon. Isah Billami, ɗan takarar Hadejia.
- Hon. Kais Abdallah, ɗan takarar Mallam Madori.
- Hon. Suraja Lawan Jiyan, ɗan takarar Kiri-Kasamma.
- Ɗan takarar Bulangu.
- Ɗan takarar Auyo.
- Wakilin ɗan takarar Kaugama.
A yayin taron, an tattauna muhimman batutuwa kan yadda za a ƙara ƙarfafa haɗin kai, fahimtar juna, da haɗa ƙarfi domin tabbatar da nasarar Jam'iyyar ADC a zaɓuɓɓuka masu zuwa, In shā Allah.
Allah Ya ba mu nasara.
Allah Ya tabbatar mana da alkhairi.
Allah Ya yi mana jagora. Amin.
#2027