Masu shirya auren sunnah msas bauchi state chapter

Masu shirya auren sunnah msas bauchi state chapter Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Masu shirya auren sunnah msas bauchi state chapter, Nonprofit Organization, SABIL Plaza AKAN BABBAN HANYAR MAIDUGURI , BAUCHI, Bauchi.

INGANTACCIYAR HANYA DOMIN
BADA GUDUMAWAR SHAWARWARI
•WA MANEMA AURE
•SHIRYA AUREN BISA SUNNAH
• TATTAUNAWA AKAN SHAWO KAN MATSALOLIN DA YAKE ADDABAR ZAMANTAKEWAR AURE
CIKIN AMANA SIRRI DA KUMA GASKIYA

09/05/2026

MATSALOLIN KISHIYOYI DA YADDA ZA'A WARWARE SU

Kishi wata dabi'a ce da Allah ya halicci mata da shi, Nana A'isha tana cewa : "Ban taba yin wani kishi ba, irin kishin da na yiwa Khadijah, kuma ban taba ganinta ba, saboda yadda naji Annabi s.a.w yana ambaton ta" Bukhari 1388

Kishi mai tsafta, shi ne : kishiya ta yi rige-rige da kishiyarta, wajen kyautatawa mijinsu, saidai abin tambaya anan shine : menene yake kawo matsaloli tsakanin kishiya da kishiya, kuma ta yaya za'a iya warware su :

1.Jahilci : ta yadda mata da yawa s**a jahilci, hikimomin da s**a sa Allah ya yi umarni a kara aure, kamar : rage yawan zawarawa da 'yammata, da kuma yawaita zurriyar Annabi s.a.w.

2. Mummunan zato, yawanci uwar gida tana tarbar amarya da mummunan zaton cewa za ta rainata, haka ita ma amarya ta kan zo da mummunan zaton cewa ba za suyi zaman lafiya ba da uwar gida, wannan sai ya sa daga zarar sun hadu babu wuya sun yi rigima.
Amma idan da ace kowacce za ta tarbi kowacce da kyakykyawan zato, har ta ga kamun ludayinta da ba'a samu matsala ba.

3. Rashin adalci daga wajen namiji, yawanci maza su kan karkata zuwa amarya, wannan sai ya haddasa fitina, saboda uwar gida za ta ce ba ta yarda ba.
Saidai abin da ya kamata mata su fahimta shi ne : babu yadda za'a yi namiji ya hada mata biyu face sai ya fi son daya, Annabi s.a.w. ya zauna da mata tara kuma ya fi son Nana A'isha, har ma mutane sun fahimci haka, wannan ya sa idan za su yi masa kyauta, s**an kirdadi ranakun da yake dakinta, don sun san kyautarsu za ta fi karbuwa a ranar, don haka idan kika ga mijinki ya fi son kishiyarki, ki yi masa uzuri kar ki tada fitina, saidai abin da sharia ta hana shi ne : rashin adalcin ya fito a hidimomin yau da kullum.

4. Munafukai, masu cece-kuce, idan da ace kishiyoyi zasu daina daukar gutsuri-tsoma, ta yadda idan s**a ji magana za su tabbatar da ita kafin su yi hakunci ga kishiyarsu da hakan ya rage kawo matsaloli.
IDAN HAR WADANNAN MATSALOLIN ZA SU WARWARE, INA GANIN ZA'A SAMU KISHI MAI TSAFTA, MENENE RA'AYINKU?

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

09/05/2026

IDAN BUDURWARKA TANA DA HALAYEN NAN GUDA UKU (3) MASU HAƊARI, KA YI GAGGAWAR RABUWA DA ITA.

Akwai wasu halaye masu haɗarin gaske ga rayuwar namiji, waɗanda matasa suke yawan yin watsi da su saboda ruɗin soyayya ko kyan fuska. Aure fa ba filin wasa ba ne, kuma ba a gina shi a kan kyawun sura kawai. Macen da zaka aura ita ce za ta zama uwar yayanka, asirin gidanka, kuma mai tsara makomarka a ɓoye.

Idan har kana tare da yarinyar da kake lissafin aure kuma ka ga ta cika waɗannan halayen guda uku (3), ina baka shawarar ka tattara kayanka ka gudu tun kafin ta jefa ka a halaka:

1. Rashin Girmama Ka Da Yawan Mayar Da Magana:
Babban abin da namiji yake buƙata a wajen mace shine Biyayya da Girmamawa. Idan har a lokacin da kuke zance budurwarka tana yi maka rashin kunya, tana mayar maka da magana daki-daki, ko tana yi maka tsawa a gaban mutane ko a waya, to tabbas zaka auri kishiyarka ne ba mata ba. Macen da bata girmama ka a waje, wallahi zata yi maka hawan-ƙawara idan ta shiga gidanka. Natsuwar namiji yana samuwa ne idan matarsa tana kallonsa da daraja.

2. Son Abin Duniya Fiye Da Kima:
Macen da kullum gori take yi maka akan baka yi mata abin da saurayin kawarta ya yi mata ba, tana da matuƙar haɗari. Yarinyar da bata san ciwon gumin da kake yi ba, kuma bata tausayawa ƙaramin jarinka, idan ka aure ta zata sa ka hawan jini. Saboda burinta na son rayuwar Soshiyal Midiya da gasa, zata iya tura ka cin amana, karɓar cin hanci, ko bashi domin kawai ta burge duniya. Ka auri wacce zata taya ka rufin asiri a matakinka na yanzu.

3. Rashin sirri Da Yawan Kawaye Marasa Tarbiyya:
Ka ji tsoron macen da bata da sirri, Idan duk wata 'yar matsala da kuka samu sai ta kwashe ta kai wa ƙawayenta don su bata shawara, gidanka ya rushe. Haka kuma macen da bata iya zama sai ta ɗora duk wani motsinta a intanet tana neman Likes & Comments daga mazan waje, bata shirya gina miji ba. Ƙawaye marasa tarbiyya sune suke wargaza gidan aminiyarsu a ɓoye ta hanyar ba ta miyagun shawarwari.

Maza, mu buɗe idonmu da kyau, Auren mace don kawai tana da kyau alhalin bata da tarbiyya, tamkar sayen mota mai tsada ce wacce babu inji a cikinta; fita daban, ciki daban.

Ka zaɓi macen da zata zama aljannar gidanka, ba wacce zata zama karshen natsuwarka ba.

Allah ya haɗa mu da matan kirki na asali waɗanda s**a san darajar namiji.
UMAR ALIYU DAHIRU ✍️

08/05/2026

FA’IDODI GUDA TAKWAS GA WANDA YA SAMU SALLAR ASUBA CIKIN JAM’I

1- FA’IDA TA DAYA.

“Samun Ladar Tsayuwar dare da ibada, idan kayi sallar assuba da isha’i a jam’i.
Annabi s.a.w yana cewa:
(Wanda yayi sallar isha’i a jam’i kamar ya
raya rabin dare da ibada,wanda ya kuma
ya kara da Sallar assuba a jam’i kamar ya
raya darene gaba daya). Tirmizy ya ruwaito shi.

2- FA’IDA TA BIYU.

“Samun kariya da alkawalin Allah”.
Annabi s.a.w yana cewa: "Wanda yayi sallar assuba acikin jam’i yana cikin alkawali da kulawar Allah".

3- FA’IDA TA UKU
“Shiga gidan aljanna” Annabi s.a.w yana cewa:
(Duk wanda ya sallaci sanyin nan guda biyu”Wato Sallar la’asar da assuba” zai shiga Aljanna).

4- FA’IDA TA HUDU
“Samun kubuta daga munafinci”.
Annabi s.a.w yana cewa: (Sallah mafi nauyi ga munafiki itace SallarAsuba da Isha’i, Kuma da yasan alkhairin dake cikinta da ya halascesu koda da rarrafe ne.

5- FA’IDA TA BIYAR.
“Samun ladar aikin hajji da Umara
cikakkiya ga wanda ya sallaci Sallar asuba
a jam’i sannan ya zauna yana rokan Allah
har rana ta fito”. Annabi s.a.w yana cewa:

{ ﻣﻦ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻐﺪﺍﺓ ﻓﻲ ﺟﻤﺎﻋﺔ ﺛﻢ ﻗﻌﺪ ﻳﺬﻛﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﺣﺘﻰ ﺗﻄﻠﻊ ﺍﻟﺸﻤﺲ ﺛﻢ ﺻﻠﻰ ﺭﻛﻌﺘﻴﻦ ﻛﺎﻧﺖ ﻟﻪ ﻛﺄﺟﺮ ﺣﺠﺔ ﻭﻋﻤﺮﺓ }…

6- FA’IDA TA SHIDA.

“Samun adduar mala’iku da kuma rubutaka cikin wadanda suke halartar sallar assuba a jam’i,Sannan zasu rubuta maka ita amatsayin aikinka na farko awannan yini,Sannan dayan mala’ikan zai rubuta maka ita a matsayin aikinka na karshe a daren da ya gabata”….
Annabi s.a.w yana cewa:

{ ﻳﺘﻌﺎﻗﺒﻮﻥ ﻓﻴﻜﻢ ﻣﻼﺋﻜﺔ ﺑﺎﻟﻠﻴﻞ ﻭﻣﻼﺋﻜﺔ ﺑﺎﻟﻨﻬﺎﺭ ، ﻭﻳﺠﺘﻤﻌﻮﻥ ﻓﻲ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺠﺮ ﻭﺻﻼﺓ ﺍﻟﻌﺼﺮ ،ﺛﻢ ﻳﻌﺮﺝ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺑﺎﺗﻮﺍ ﻓﺒﻜﻢ ﻓﻴﺴﺄﻟﻬﻢ ﺭﺑﻬﻢ ﻭﻫﻮ ﺃﻋﻠﻢ ﺑﻬﻢ : ﻛﻴﻒ ﺗﺮﻛﺘﻢ ﻋﺒﺎﺩﻱ ؟ ﻓﻴﻘﻮﻟﻮﻥ :ﺗﺮﻛﻨﺎﻫﻢ ﻭﻫﻢ ﻳﺼﻠﻮﻥ ﻭﺃﺗﻴﻨﺎﻫﻢ ﻭﻫﻢ ﻳﺼﻠﻮﻥ }

7- FA’IDA TA BAKWAI
“Samun haske cikakke a ranar alkiyama”
Annabi s.a.w yana cewa:
:{ ﺑﺸﺮ ﺍﻟﻤﺸﺎﺋﻴﻦ ﻓﻲ ﺍﻟﻈﻠﻢ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﻤﺴﺎﺟﺪ ﺑﺎﻟﻨﻮﺭ ﺍﻟﺘﺎﻡ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻘﻴﺎﻣﺔ }

8- FA’IDA TA TAKWAS.
“Dacewa da falalar raka’a tanilfajir, wadda
Annabi s.a.w yake cewa tafi duniya da
abinda yake cikinta alkhairi”. Annabi s.a.w yana cewa:
:{ ﺭﻛﻌﺘﺎ ﺍﻟﻔﺠﺮ ﺧﻴﺮ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ ﻭﻣﺎ فيها

06/05/2026

Yar uwata ki fahimci abinda zan gaya miki.

1.ki girmama mijin ki

2. Ki girmama iyayen mijin ki da yan uwan sa.

3. Ki zama mace mai
kunya da kamun kai.

4.ki zama mace mai nutsuwa da rikon Amana.

5.ki kula da Addinin ki,nemi sani sosai akan ibadar ki musamman bangaren tsarki.

6.ki nisanci duk wata kawar da bata arziki ba,domin wasu kawayen zasu iya bata miki rayuwa,wasu har auren ki ma zasu iya miki sanadin mutuwar auran ki.

7.ki zama matar rufin asirin mijin ki.bawai ki zama matar tonawa mijin ki asiri a duniya ba.

8. Kar ki yi wasa da iyayen ki ta wajan masu biyayya da kyautata wa a gare su,har da yan uwan ki ma.

9.lallai ya zama kina kulawa da tarbiyyar. 'ya'yan ki.

10.ki zama mace mai taimakon mijin ta koda bata hanyar kudi ba, kwantar masa da hankali.

11.ki zauna da kishiyar/kishiyoyin ki lafiya,har da yaran su.

12.ki dauki zaman auren ki a matsayin ibada Wanda Aljanna k**e nema.

13.ki yawaita yiwa yaranki addu'a, sannan ki koya masu yadda zasu nayiwa mahaifin su dake addu'a.

14. Ki zama mace mai taimako da abinda Allah ya h**e miki.

15.ya zama kina shigar kamala idan zaki fita.

Dafatan zaku fahimci abinda na fada maku.

Khadija Auwal ✍️
Copy From
🧕🏽Nisa,us Sunnah🧕🏽






06/05/2026

*NASIHA TA MUSAMMAN*

Ka rayu da tsoron Allah ko da babu wanda yake ganin ka, domin ka sani Allah koyaushe yana kallonka.

Ka kasance mai gaskiya a dukkan al’amuranka, domin gaskiya tana jagorantar zuwa alheri, alheri kuma yana kaiwa Aljannah.

Ka rike iyayenka da mutunci da tausayi, domin jin dadinsu shi ne tushen albarkarka.

Ka guji hassada da kiyayya, domin su ne asalin mafi yawan sharri.

Ka dinga tuna mutuwa, domin hakan yana rage tsananin son duniya a zuciya.

Ka rike addu’a da godiya ga Allah a kowanne hali, domin komai yana tafiya ne da kudirinsa.

Rayuwa hanya ce mai gajarta — ka cika ta da ayyukan alheri kafin lokacin komawa ya zo.

Allah Ya ba mu ikon aikata abin da Yake so, Ya kuma kare mu daga abin da zai jawo mana laifi a gabansa. Ameen

05/05/2026

LAIFUKA (20) DAKE HANA MACE SHIGA ALJANNAH INDAI BATA TUBA BA

1) Duk Matar da take da aure tayi zina.

2) Duk Matar da ta Mallaki Mijinta ta hanyar asiri ko ta hanyar tsafi

3) Duk Matar data Hana kishiyarta ta zauna da Mijinta lafiya

4) Duk matar da ta raba mijinta da 'ya'yansa,ko ta Hanyar Asiri ko Yaudara

5) Duk matar data raba mijinta da Yan uwansa ta hanyar asiri ko yaudara

6) Duk matar da tayi asiri akan saukarwa kishiyarta jinin haila duk ranar kwananta sai haila tazo mata

7) Duk matar da tasa aka daure mahaifar kishiyarta,don kar ta haihu

8) Duk matar data dauko ciki a waje ta bawa mijinta,kuma ta tabbata ba nasa bane

9) Duk matar da tayi daurin baka ga mijinta don yayi mata kishiya

Ma'anar baka shine: Duk ranar da zai kwana a dakin kishiyarta sai ya zamanto bana miji ba

Amma idan ya dawo dakin matsafiyar sai ya dawo namiji

10) Duk matar data nemi mijinta ya saketa,alhali baya cutar da ita.Kuma ba yadda ya iya

11) Duk matar da bata godewa mijinta bisa ga irin abubuwan da yake mata na Alkhairi

12) Duk matar da take cutar da mijinta da bakinta

13) Duk matar da batayin wankan janaba, bayan ta sadu da mijinta,ko batayin wankan haila ko biki

14) Duk matar da take tona asirin mijinta a cikin kawayenta

15) Duk matar da take annamimanci

16) Duk matar da take sa kayan da yake nuna tsiraicinta

Irin wanda musulunci yake fada akan irin shigar yahudawa da nasara

17) Duk matar data kara gashi akan nata

18) Duk matar da tilastawa mijinta yayi mata wani abu wanda ba zai iya yi ba

19) Duk matar data dauki dan wani ta bashi Mama (Nono) bada izinin Mijinta ba

20) Duk matar da zata cewa Mijinta tunda muke dakai meka taba yi mini.

Dukkan wadannan Laifuka guda 20, ko wani guda daya a ciki

Idan Mata ta mutu tanayi bazata shiga Aljannah ba

Koda zata shiga sai an Babbaka ta

ALLAH YASA MUDACE AMIN ✍️

05/05/2026

NASIHA GA IYAYE MAZA DA MATA AKAN AURE
*************************************

BURIN MACE KO NAMIJI GAMEDA ABOKIN RAYUWAR AURE

Kowace macen da ta kai minzalin aure, ƙololuwar burin ta a rayuwa shine taga ta auri mutumin kirki wanda yake kwatanta koyi da tafiya bisa tafarkin Manzon Tsira SAW., Wanda take sa ran zai kwatanta yi mata adalci da kyautata muamala gareta a yayin su ka yi aure.

To amma son hakan a zuci ko kuma faɗar sa da baki kaɗai ba zai isa ba wajen samun cikar wancan burin nata matsawar dai ba ta haɗa da aiki tuƙuru bisa juriya da jajircewa ba.

A matsayin ki ta mace, koda ace kin yi sa'a Allah ya azurta ki da irin wancan abokin zaman da k**e buƙata, to fa sai kin yi aiki tuƙuru kafin ki iya tatsowa da canjawa ko ɗora wannan miji naki bisa turbar da wannan auren naku zai bunƙasa har ya kai ga nasarar da k**e buƙata.

Kisa aran ki cewa ba zaki taɓa samun abinda k**e so daga wajen mai gidan ki ba har sai kin zauna kinyi sabon karatu mai zurfi akan sa yadda zaki masa fahimta irin ta ciki da waje, kuma irin wannan karatu ya sha bambam da duk wanda kika yi masa a baya kafin ku yi aure, domin duk yadda k**e tsammanin kin shaƙu dashi saboda kusanci na soyayya data gabata kafin aure, to daga sanda aka ɗaura aka shigo gida, to fa karatu ya dawo sabo, ki ƙaddara cewa a baya baki san shi ba yanzu ne zaki san ainifin waye shi.

Da zarar kin fahimci irin kalar mai gidan naki, ba tare da wata-wata ba sai ki ɗaura ɗammarar yin aiki na fuskantar ƙalubalen da ke gabanki manya da ƙanana.

Misali:

Akwai buƙatar ki zamo mai nuna wa mai gidan ki kulawa cikkakka, mai ƙara masa ƙwarin guiwa, mai taimakon sa bisa sauke nauyin da ke kan sa, mai riƙe asirin sa, kana mai miƙa masa yarda da amincin ki.

Akwai buƙatar ki zamo mai yawan murmushi (haƙiƙa shi babban makami ne dake cin zukatan mazaje da yaƙi), mai yin ba'a (wasa) da dariya, mai shagwaɓa, wani lokacin kuma ki zamo kece mai lallashi/rarrashi,.

Akwai buƙatar ki zamo mai nuna masa cewa da gaske fa kina SON shi (irin huɗubar nan da akewa yaran mata cewa ba'a nunawa miji soyayya ko sakin jiki dashi saboda ba ɗan goyo ba ne, huɗuba ce ta shaiɗan ki nisance ta), ki zamo tushen samuwar nutsuwa, farin ciki da kimtsuwar sa, ki nuna masa cewa baki da wani abu a duniya daya kai muhimmancin sa agareki; ya fi miki tarin dukiya da duk wani ƙyale-ƙyalen duniyar nan.

Ki zamo masa MACE a aikace ba a suna ba ta hanyar amfani da baiwar da Ubangiji yai miki na halitta don samarwa mijin nutsuwa wanda kuma shine ya bambamta ki da namiji (Akwai matan da sunan mata kawai suke amsawa amma duk muamalar su irin ta maza ne, irin waɗannan matan ba yadda za'ayi su iya nasarar kame zukatan mazajen su, saboda shi namiji da mace yake buƙatar zaman aure ba macen-namiji ba).

Ki zamo mai lura da ƙarfafar tunanin sa da motsin ruhin sa ta kowane irin yanayi na ɓacin rai ko annashuwa, ki zamo mai haƙuri da juriya wajen ɗaukar ɗawainiyar sa, mai ƙarfafa shi cikin gyaran alaƙar sa da Ubangijin sa, ki taimake sa wajen riskar ƙololuwar matsayi na zamowa cikin sahun cikakkun bayin Allah masu biyayya.

IN MUKA KOMA ƊAYA GEFEN KUMA:

Suma maza kowannen su burin sa shine ya auri mace wacce take kan tafarkin koyi da Sayyidah Khadija (r.t.a) wanda kowa yasan irin kulawar da ta bawa Manzo SAW. ne hakan ya bata babban matsayin da bama ita ba hatta ƙawayen ta Manzon Allah SAW yana girmama su da wani irin girma na musamman.

To amma shima namiji kamar irin waɗancan abubuwa da aka ce mace sai ta kiyaye kafin ta kai ga riskar cikar burin ta, shima basu faɗi akan sa ba.

Da farko a matsayin ka na namiji da ke son rayuwar auren sa da matar sa ta yi nasara, to akwai buƙatar ka fara cikawa ko sauke duk haƙƙin da ke wuyan ka da Allah ya ɗora maka na haƙƙin wannan auren (ba zai taɓa yuwuwa ba ka samu nasara a rayuwar auren ka ba alhali haƙƙin da ke kanka kana wasa dashi, hakan shi zai buɗe ƙofar ɓaraka da zata ɓata alaƙar ka da matar ka domin kamar yadda taga baka bata nata haƙƙin ba, kai ma fa kar kayi tsammanin samun naka daga gareta).

Akwai buƙatar bada ingantaccen lokacin ka ga iyalin ka acikin gidan ka, ba wai ka ɗauki iyalin ka cewa basu da lokacin ka da ka ware domin su ba, hakan na nuna basu da wani muhimmanci agare ka, abinda hakan zai haifar maka shine kaima sai su ɗauke ka kamar irin yadda ka ɗauke su ba ka da muhimmanci.

Akwai buƙatar ka zamo babban aboki gareta, ka nuna mata tsantsar SO da ƘAUNA da kulawa, ka girmama ta da irin girmamawan da har sai ta ji cewa bata kai a bata irin wannan girman ba, ka riƙa tunanin ta aran ka, ka zamo mai jin kewar ta a sanda bakwa tare (ka ɗaga waya ka kirata kace kawai ka kira ne don kaji muryar ta saboda kana missing ɗin ta), ka riƙa yin hira da ita, kana mai bata labari mai daɗi, burgewa da ƙayatarwa, ka yi wasa da dariya da ita, kuma ka daraja ta.

Akwai bukatar ka riƙa yaba mata a duk sanda ta kƴautata maka ko tayi wani abu na burgewa domin kai, idan ta durƙushe ka ɗaga ta ka tallafe ta, ka zamo mai yafiya da kauda kai bisa kuskuren ta da ajizancin ta.

Akwai buƙatar ka nuna mata cewa ita ce mutum mafi kusanci da muhimmanci agare ka a duniyar nan musamman da daddare kar ka barta ka tafi can cikin abokai kana hira sai can tsakar dare ka dawo daidai lokacin har tayi barci.

A duk sanda zaka yi ibada don samun kusanci da Ubangiji, ka umarce ta itama ku yi tare, idan kun kammala ku yiwa junan ku da zamantakewar ku addua.

A yayin da ma'aurata s**a iya kiyaye wannan, zamantakewar auren su zai kai ga duk irin nasarar da suke buƙata in sha Allahu.

Alhamdulillah!
Anan na kawo ƙarshen wannan jerin rubutu nawa mai taken NASIHA GA IYAYE MAZA/MATA AKAN AURE.
Ina fatan Allah ya sa waɗanda aka yi domin su, su yi aiki da abinda s**a karanta, ya sanya ya zamo sanadiyyar gyaruwar gidajen auren mu.
Allah ya karɓi abinda yake daidai a ciki, kusakuren ciki kuma ya yafe.
Ina godiya ga ɗaukacin waɗanda s**a bada lokacin su mai tsada s**a bibiyi abinda aka rubuta Ubangiji ya saka musu da alherin sa bisa goyon baya da ƙwarin guiwar da s**a bayar.

Ɗanuwan ku a musulunci Bn-Ahmad Imaam

Nagode.

03/05/2026

Maza basa son mace marar Tarbiyya
Maza basa son macen da bata da kamun kai.
Maza basa son mace marar aji.
Maza basa son ballagazar mace.
Maza basa son mace mai gulma da munafurci
Maza basa son mace mai yawan yawo.
Maza basa son mace mai kwadayi da roko.
Maza basa son mace marar kunya
Maza basa son mace kazama
Maza basa son mace marar kirki.
Maza basa son mace jahila
Maza basa son mace marar sirri
Maza basa son mace mai Gori
Maza basa son mace mai gadara

Saboda haka ki kula,ki kiyaye kin ji yar uwata

22/04/2026

WASU DAGA CIKIN DALILAN DAKE SA AURE SAURIN MUTUWA

A halin yanzu da dama aure na saurin mutuwa sosai,wani da anyi ko shekara bara'a cika ba sai auran ya mutu,wani kuma cikin watanni auran ke mutuwa,kuma hakan nada nasaba daga cikin wasu dalilai.

1.KARYA
yana matukar taka rawar gani gun tarwatsa rayuwar aure,idan miji yayi wa budurwa karyan abubuwa da dama,tun tana waje yagama mata karya,idan ta aure shi taga babu hakan,shikenan kuma aure yafara rawa son bazata zauna ba,saboda don auran karya aka gina daga karshe sai kuma rabuwa saboda daman don karya akayi auran.

2 IDAN AN SAN JUNA A WAJE
matukar ansan juna tun awaje,wannan baisa aure jimawa ,saboda zargin juna dake tsakanin su,macen bazata yarda dashi ba saboda lokacin dazai fita zatana tunanin cewa zai je iskanci ne gun mace kamar yadda s**ayi a waje,haka shima mijin zai dinga zargin matarsa duk lokacin da zata fita,saboda tun a waje sun rusa tubalin kyakkyawan alakar dake tsakanin su,daga karshe idan an gagara hakuri sai kuma rabuwa.

3.AURAN SHA'AWA
idan anyi aure don sha'awa daga lokacin da kowa ya gamsu da juna,sha'awa ta gushe a tsakanin su shikenan kuma babu wani so saboda daman don sha'awa akayi auran bawai don kaunar juna ba,hakan kuma nasawa a rabu da juna.

4.TSANANIN KISHI MAI SA ZARGI
Da akwai wasu masu mungun kishin da bai dace ba,wanda hakan ke sa zargi a tsakanin mijin ga matarsa,kishin yakan zama na hauka har ya wuce shari'a yadda ta amta,daga karshe hakan nasa wa mijin har ya iya zargin matarsa yarabu da ita don mungun kishin nasa.

5.RASHIN HAKURI
Idan har ma'aurata sun kasance basu da hakuri akan junan su,abu kadan yasa bazasu iya danne zuciyarsu ba hakan na iya ruguza zamantakewar rayuwar auran nasu.

6.KAZANTA
gaskiya kazanta yana taka rawar gani shima narashin kula dake tsakanin ma'aurata walau mace ko namiji duk wanda yakasance kazami a tsakanin su.

7.AURE DON KUDI
idan mace ta yi aure don kudi ,saboda kudin namiji take so idan ta aure shi saboda kudi,tana mishi soyayya don kudi ne...

21/04/2026

*YAR UWA WACCE TAKE GIDAN AURE DA WACCE ZATAYI AURE DAKE NAKE*

Mijinki shugabanki ne

Mijinki jagoranki ne

Mijinki abin sonki ne

Mijinki masoyinki ne

Mijinki abin qaunarki ne

Mijinki farincikin ki ne

Mijinki nutsuwarki ne

Ya zabeki ya aureki saboda yana sonki yana qaunarki

Ya zabeki cikin dubban mata saboda ke kadai zuciyarsa take bukata kuma ta samu nutsuwa dake

Ya zabeki sabida ya yadda da tarbiyyarki dattaku da mutuncin gidanku

Ya zabeki sabida ya cigaba da zama farincikin ki jagoran rayuwanki

Saboda haka ki kasance abin alfahari gareshi

Ki masa biyayya ki kula dashi da duk abinda ya shafesa

Ki kasance masa masoyiya qanwarsa aminiyarsa ki haskaka rayuwarsa da kyakkyawan dabi'unki

Idan iyayensa suna raye ki tayashi yi musu biyayya kisa suji tabbass ke diyarsu ce ba suruka ba

Ko da wasa karki bari fushi ya shiga tsakaninku

fushin da zaki kada ya wuce na dan second domin ba'aso ma'aurata suna nesanta da junan da har zasu cutar da junansu

Ko ya daga murya ko yana cikin fushi ki rarrasheshi cikin taushin kalma

Kukan mace yana karya zuciyar namiji ki hada dashi zakiga shi zai dawo yana rarrashinki

Kada ki bari shedan yashiga tsakaninku kuyi hakuri ku kaunaci juna ku taimaki junanku har abada

ALLAH ya dawwamar da farinciki ni'ima aminci da zaman lafiya a rayuwarmu🤲🤲🤲

Shawara ce da jan hankali zuwa gareki

Zanzo kan yan uwana Maza

Address

SABIL Plaza AKAN BABBAN HANYAR MAIDUGURI , BAUCHI
Bauchi

Opening Hours

Monday 08:00 - 18:00
Tuesday 08:00 - 18:00
Wednesday 08:00 - 18:00
Thursday 08:00 - 18:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 08:00 - 18:00
Sunday 08:00 - 18:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Masu shirya auren sunnah msas bauchi state chapter posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share