ZALAU TV

ZALAU TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ZALAU TV, Nonprofit Organization, Dutsan Tanshi, Bauchi.

DA DUMI-DUMI: Bauchi Media Game Changers Network Ta Ƙaddamar da Shirin “Road to Bauchi State Government House”Ƙungiyar B...
30/06/2026

DA DUMI-DUMI: Bauchi Media Game Changers Network Ta Ƙaddamar da Shirin “Road to Bauchi State Government House”

Ƙungiyar Bauchi Media Game Changers Network ta sanar da ƙaddamar da wani shiri na musamman mai suna “Road to Bauchi State Government House”, wanda zai tattaro masu neman takarar Gwamnan Jihar Bauchi domin tattaunawa kai tsaye da al’umma.

Shirin, wanda zai gudana a matsayin tattaunawa ta mutum-da-mutum (One-on-One Interview Series), zai bai wa kowane ɗan takarar gwamna damar bayyana tafiyarsa ta siyasa, falsafar jagoranci, tarihin hidimomin da ya yi wa al’umma, nasarorin da ya samu, tsare-tsaren manufofinsa, da kuma hangen nesansa na makomar Jihar Bauchi.

A cewar masu shirya shirin, manufar wannan dandali ita ce bai wa kowane ɗan takara dama iri ɗaya ta bayyana kansa ga al’umma, tare da bai wa masu zaɓe cikakkun bayanan da za su taimaka musu wajen yanke shawara mai kyau kafin zaɓen 2027.

Hoton tallan shirin ya nuna cewa an gayyaci fitattun masu neman takarar gwamnan jihar daga jam’iyyu daban-daban, ciki har da:

* Barr. Mohammed Abdullahi Abubakar (APC)
* Hon. Yakubu Adamu, Ph.D. (APM)
* Sanata Shehu Buba Umar (PDP)
* Hon. Usman Adamu Sufi (PDP)
* Barr. Ibrahim Kashim (NNPP)
* Distinguished Senator Halliru Dauda Jika (ADC)

Masu shirya shirin sun bayyana cewa za a sanar da ranar fara gudanar da tattaunawar nan ba da jimawa ba.

Sanarwa:
Jamilu M. Inuwa
Ibrahim U Dagash.

DA ƊUMI-ƊUMI: Hukumar zaɓe na ƙasa INEC ta fitar da jadawalin jerin ƴan takarar Sanata da ƴan majalisun tarayya na jam'i...
30/06/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Hukumar zaɓe na ƙasa INEC ta fitar da jadawalin jerin ƴan takarar Sanata da ƴan majalisun tarayya na jam'iyyar APC a jihar Bauchi.

22/06/2026

YANZU-YANZU: Yadda DSS ke Hankaɗa Sowere zuwa gidan Yari, bayan kammala zaman kotun tarayya dake Abuja..

MOTA TA KWACE TA FADA KUSA DA GADAR GAMES VILLAGE A BAUCHI, DIREBA YA TSIRA.An samu wani hatsarin mota a yau a cikin gar...
17/06/2026

MOTA TA KWACE TA FADA KUSA DA GADAR GAMES VILLAGE A BAUCHI, DIREBA YA TSIRA.

An samu wani hatsarin mota a yau a cikin garin Bauchi bayan da wata mota ta kwace wa direbanta tare da fadawa kusa da gadar da ke dab da gidan Man Zaimah Petroleum a kan Titin Games Village.

Rahotanni sun nuna cewa motar ta rasa daidaito ne kafin ta fada wurin, lamarin da ya jawo hankalin mazauna yankin da masu wucewa.

Duk da hatsarin, an ce direban motar ya tsira daga lamarin, inda ya fito daga cikin motar ba tare da samun wani mummunan rauni ba.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a samu rahoton rasa rai ko wani mummunan rauni sak**akon hatsarin ba.

Masu gani da ido sun yabawa Allah bisa yadda direban ya tsallake hatsarin lafiya, tare da kira ga masu ababen hawa da su kasance masu taka-tsantsan yayin tuki.

Allah Ya Kare Hanyoyinmu Daga Hadurra.

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Ba-zata Cikin Dare Ga Al’umma da Jami’an Tsaro a Matazu da KewayeGwamnan Jihar Katsina, Mala...
17/06/2026

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Ba-zata Cikin Dare Ga Al’umma da Jami’an Tsaro a Matazu da Kewaye

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya gudanar da ziyarar ba-zata cikin dare zuwa garin Matazu da wasu kauyukan da ke kewaye da shi domin duba yadda ayyukan tabbatar da tsaro ke gudana a yankin.

Ziyarar ta biyo bayan wani zama da masu ruwa da tsaki a harkokin tsaro da Gwamnan ya yi tare da Kwamandan rundunar sojin da ke jagorantar Yakin, Major General W. B. Idris.

A yayin zagayen, Gwamna Radda ya fara isa garin Matazu kafin daga bisani ya zarce zuwa Sayaya, Mazoji, Fafawa, Nasarawan Kalgo da Tashar Icce.

Haka kuma, ya zagaya ta hanyar Sayaya da sauran kauyukan da ke makwabtaka da su.

Gwamnan ya kuma bi hanyar Mazoji zuwa Dutsinma kafin daga ƙarshe ya dawo Katsina.

- Katsina Post

KAI TSAYE DAGA NAN CIKIN GARIN BAUCHIRundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta fara ɗaukan tsauraran matakan hana zirga-zirga...
17/06/2026

KAI TSAYE DAGA NAN CIKIN GARIN BAUCHI

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta fara ɗaukan tsauraran matakan hana zirga-zirgar motocin da ba su da rajista da kuma waɗanda ke rufe ko amfani da lambobin mota na bogi a fadin jihar.

A matsayin wani bangare na aikin, an tura Kotunan Tafi-da-Gidanka (Mobile Courts) zuwa dukkanin shiyyoyin ‘yan sanda da kuma muhimman wurare a cikin birnin Bauchi domin gurfanar da masu laifi cikin gaggawa.

Rundunar ta bayyana cewa wannan mataki na da nufin ƙara tsaron hanyoyi da kuma rage aikata manyan laifuka k**ar satar mutane da fashi da makami da ake alaƙantawa da motocin da ba a iya gano su.

An kuma yi kira ga masu ababen hawa da su daidaita takardunsu da kuma tabbatar da cewa lambobin motocinsu a bayyane suke, domin duk wanda aka k**a zai fuskanci hukunci kai tsaye, k**a mota da kuma gurfanarwa a gaban kotu.

📷 Albarka Radio

Labari cikin hotuna!Yadda Rundunar sojan Najeriya ta Fansar yamma ta samu nasarar kubutar da mutanen nan guda huɗu da ak...
17/06/2026

Labari cikin hotuna!

Yadda Rundunar sojan Najeriya ta Fansar yamma ta samu nasarar kubutar da mutanen nan guda huɗu da aka nuna cikin faifan bidiyo tare da marigayi Janar Rabe Abubakar a ƙarƙashin wata bishiya ɗaure a wajen masu garkuwa da mutane.

Bayan kubutar dasu, an miƙa su ga likitoci domin su duba lafiyar su, kafin daga bisani a miƙa ga yan uwan su ko dangin su. Makusanta na wadannan mutane, sun bayyana cewa sama da wata biyu suna tsare hannun masu garkuwa da mutanen, a wata majiyar ma tace har kuɗin fansa an biya, amma basu sake suba.

Rundunar sojan Najeriya mai suna Fansar yamma na ci gaba da fatattakar yan ta'adda da s**a addabi yankin Matazu da Musawa, da wasu yankuna masu makwabta dasu, k**ar irin su Kankia, Charanci, da wani ɓangare na ƙaramar hukumar Kusada, dama wasu sassa na makwabciyar Jihar Katsina watau Jihar Kano.

Da ɗumi-ɗumi: Ƙungiyar (CAND) Ta Nemi A Binciki Sanata Abdulaziz Yari Kan Ɗanyen Zinare Na Naira Biliyan 4.4 Da Hukumar ...
17/06/2026

Da ɗumi-ɗumi: Ƙungiyar (CAND) Ta Nemi A Binciki Sanata Abdulaziz Yari Kan Ɗanyen Zinare Na Naira Biliyan 4.4 Da Hukumar EFCC Ta K**a Ana Ƙoƙarin Fita Da Shi Ƙasar Waje A Jihar Kano

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa, (EFCC) ta tsananta bincike kan wani ɗanyen zinare da ta k**a a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, mai nauyin kilogiram 22.2, wanda darajarsa ta kai kusan Naira Biliyan 4.4, da ake zargin ana yunƙurin safarar sa zuwa ƙasar waje ba bisa ƙa'ida ba.

Rahoton shafin (Billionaires.Africa) da aka wallafa a ranar 15 ga Yuni, 2026, ya ce jami'an EFCC na shiyyar Kano sun k**a wani jami'in tsaro na Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA), Anas Baffa, bisa zargin ɓoye ɗanyen zinaren a cikin wandonsa domin tsallake binciken tsaro a filin jirgin kafin a miƙa shi ga wasu fasinjojin da ke shirin tafiya ƙasar waje.

Rahoton ya kuma ce wata ƙungiyar fararen hula mai suna Coalition for Accountability and National Development (CAND) ta yi kira ga hukumomin tsaro su zurfafa bincike kan safarar zinare da haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba, tana mai zargin cewa ya k**ata a binciki wasu manyan mutane kan lamarin, ciki har da Sanata Abdulaziz Yari, tsohon gwamnan Jihar Zamfara.

A cewar daraktan ƙungiyar, Ibrahim Musa, irin waɗannan ayyuka na jawo asarar kuɗaɗen shiga ga gwamnati tare da ƙara rura wutar matsalolin tsaro a wasu sassan ƙasar.

Sai dai, har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, EFCC ba ta ambaci sunan Sanata Abdulaziz Yari a matsayin wanda ake zargi a hukumance ba dangane da binciken, kuma babu wata sanarwa daga hukumar da ta tabbatar da zarge-zargen da ƙungiyar CAND ɗin ta yi.

A gefe guda kuma, a wani bidiyo da ya wallafa a shafin Tiktok, wani mai sharhi kan al'amuran yau da kullum, Junaidu Aminu, ya bayyana cewa ana gudanar da bincike kan wani jirgin kamfanin Ethiopian Airlines a Filin Jirgin Sama na Kano.

Ya yi zargin cewa an gano wasu akwatuna guda 15 da aka ɓoye bayanan abubuwan da ke cikinsu, waɗanda ake zargin suna ɗauke da kayayyaki masu haɗari.

Junaidu, ya kuma yi iƙirarin cewa haƙar ma'adanai ta ɓarauniyar hanya na da alaƙa da matsalolin tsaro k**ar garkuwa da mutane da ayyukan ƴan fashin daji a Arewa, musamman a Jihar Zamfara, yana mai cewa wannan kamun alama ce ta ƙoƙarin hukumomi na daƙile irin waɗannan ayyuka.

Wannan lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da wata ƙungiyar fafutuka mai suna "Mai Kare Talakawa" da ke Sokoto ita ma ke tambayar tushen arziƙin Sanata Abdulaziz Yari.

A cewar rahoton Billionaires.Africa, ƙungiyar ta nuna damuwa kan yadda kamfanin Yari, MA'AM Energy Limited, ya sayi kaso mafi rinjaye, kusan kashi 95 cikin ɗari na kamfanin Geregu Power Plc daga hannun attajiri Femi Otedola a watan Disambar 2025, a wata yarjejeniya da aka ƙiyasta cewa darajarta ta kai Naira Tiriliyan 1.08.

Sai dai, babu wata hukuma da ta tabbatar da cewa akwai alaƙa tsakanin wannan harkar kasuwanci da binciken safarar zinaren da EFCC ke gudanarwa. Haka kuma, Sanata Abdulaziz Yari bai fito ya yi martani kai tsaye ga zarge-zargen da wasu ƙungiyoyi da masu sharhi s**a yi ba.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta gina sabbin gidaje ga manyan alƙalan Babbar Kotun Tarayya, a wani mataki na inganta walwa...
17/06/2026

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta gina sabbin gidaje ga manyan alƙalan Babbar Kotun Tarayya, a wani mataki na inganta walwala da yanayin aikinsu. An ƙaddamar da gidaje guda 10 a sabon rukunin gidajen alƙalai da ke Gundumar Katampe, inda gwamnati ta bayyana cewa hakan zai ƙara ƙarfafa ɓangaren shari’a da kuma tubalin dimokuraɗiyyar ƙasa.

HOTUNA: Rikici ya barke tsakanin mambobin ƙungiyoyin direbobi na NURTW da RTEAN kan ikon mallakar tashar mota da ta ’yan...
17/06/2026

HOTUNA: Rikici ya barke tsakanin mambobin ƙungiyoyin direbobi na NURTW da RTEAN kan ikon mallakar tashar mota da ta ’yan tifa da ke kusa da shatale-talen Awala a cikin garin Bauchi, lamarin da ya yi sanadiyyar asarar dukiyoyi masu yawa.

📷 Albarka Radio

Address

Dutsan Tanshi
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZALAU TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share