15/08/2026
’Yan Sanda Sun K**a Wani Mutum Kan Zargin Binne Al-Qur’ani da Abubuwan Tsafi a Zuru
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta k**a wani mutum mai suna Abubakar Musa, mai shekaru 29, mazaunin ƙauyen Rafin Mose da ke ƙaramar hukumar Zuru, bisa zargin haɗa baki, tozarta littafin addini, amfani da tsafi da sihiri, da kuma tayar da zaune tsaye.
Kakakin rundunar, SP Bashir Usman, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 9 ga Agustan 2026, da misalin ƙarfe 7:00 na yamma, a yankin Zango da ke Zuru.
A cewar rundunar, binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ya haɗa baki da wasu mutane biyu, Rabi’u Tela, mijin Zarau Hassan, da Hamza Zango, waɗanda s**a tsere, inda ake zargin sun haƙa rami a cikin ɗakin Zarau Hassan tare da binne Al-Qur’ani da wasu abubuwa.
’Yan sandan sun ce daga cikin abubuwan da aka binne tare da Al-Qur’ani akwai maniyyi, goro fari da ja, kayan ciki, matattun dabbobi da wasu abubuwan da ake zargin na tsafi ne.
Rundunar ta ce ana zargin an aikata hakan ne da nufin sanya Zarau Hassan ta kasance mai biyayya ga mijinta, Rabi’u Tela, abin da ta ce ka iya haifar da rikici da tada hankalin al’ummar Musulmi.
A halin yanzu, Abubakar Musa yana tsare a hannun ’yan sanda, yayin da ake ci gaba da kokarin cafke Rabi’u Tela da Hamza Zango.
Rundunar ta bayyana cewa za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kebbi, CP Umar M. Hadejia, ya yi Allah-wadai da lamarin, tare da jaddada cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda aka samu da laifin da ka iya barazana ga zaman lafiya da haɗin kan al’umma.