08/03/2026
FASSARAR WASIƘAR AMINU HALLIRU ZAUWA HARSHEN HAUSA:
BUƊELADIYAR WASIƘA ZUWA GA HON. MEMBA (Hon. Abdulkarim Kero)
Mai Girma, Ranka Ya Dade,
Na rubuta wannan wasiƙa ne a madadin dimbin matasa da mazauna Mazabar Kaduna ta Kudu, waɗanda ke nuna damuwa da takaici game da irin wakilcin da kuke yi musu a halin yanzu a Majalisar Tarayya.
A yau, wakilan jama’a a Majalisar Wakilai ta Tarayyar Najeriya suna ƙoƙari matuƙa wajen tallafa wa al’ummomin da suke wakilta ta hanyar samar musu da damammaki masu ma’ana. Wasu na nemo guraben aikin gwamnati a matakin tarayya, suna taimaka wa matasa samun aiki a hukumomin gwamnati, suna jawo shirye-shiryen horo, tallafin karatu, da shirye-shiryen ƙarfafa rayuwar jama’a.
Sai dai abin takaici, halin da ake ciki a Kaduna ta Kudu, ya sha ban-ban da irin na wasu yankun.
Yayin da takwarorinku a sassa daban-daban na ƙasar nan ke taimaka wa al’ummominsu wajen samun aikin gwamnati da damammakin aiki masu ɗorewa, wasu daga cikin matasan Kaduna ta Kudu ana ba su ƙananan kuɗaɗe na naira dubu biyar (₦5,000) kacal a wasu lokuta. Da dukkan girmamawa, wannan ba ƙarfafawa ba ne; hanya ce da ke jefa mutane cikin dogaro da taimakon wucin gadi.
Matasanmu sun yi karatu, suna da ƙwarewa, kuma suna da sha’awar yin aiki. Abin da suke buƙata shi ne wakilci wanda zai yi fafutuka domin a haɗa su cikin damammakin da gwamnatin tarayya ke bayarwa, ba wai rabon ƙananan kuɗaɗe da ba su ma iya biyan bukatun yau da kullum ba.
Al’ummar Kaduna ta Kudu ba su zaɓi a ba su tarkace ba. Sun zaɓi a wakilce su, a kare muradunsu, kuma a kawo ci gaba gare su. Sun zaɓi wanda zai buɗe musu ƙofofin damammakin da ke akwai a matakin gwamnatin Tarayya.
Muna sa ran wakilinmu zai yi gwagwarmaya domin samar wa ‘ya’yan mazabar guraben aiki a ma’aikatun tarayya, hukumomi, da sauran cibiyoyin gwamnati. Muna son ƙarfafawa ta hanyar kasuwanci, koyon sana’o’i, da bunƙasa ilimi, domin waɗannan su ne ababen da ke kawo ingantacciyar ƙarfafawa.
Gaskiya ne, raba ₦5,000 ga matasa masu fama da wahalhalu na iya zama kamar karamci, amma ba zai iya magance matsalolin rashin aikin yi, talauci, da jin an ware matasa a wannan mazaba ba.
Mai girma Hon. Memba, shugabanci a yau ba wai game da busa ƙaho ko sanya hula ba ne. Shugabanci yana nufin samun hangen nesa, ƙarfafa gwiwar jama’a, da yin fafutuka domin ci gaban mutanen da kake wakilta.
Kaduna ta Kudu ta cancanci fiye da haka. Matasanmu suna buƙatar damammaki, ba rabon ƙaramin taimako na wucin gadi ba. Don haka wannan wasiƙa kira ne na a sauya salon da zai fifita ƙarfafawa mai ɗorewa, damammaki na gaskiya, da ingantaccen wakilci ga al’ummar da s**a ba ku amanar wakilcin su.
Tarihi zai yi muku hukunci ba bisa yawan kuɗin da kuka raba ba, sai dai bisa damammakin da kuka samar wa al’ummarku.
Matasan Kaduna ta Kudu na kallonku, kuma suna fatan za a ji muryarsu.
Rubutawa: Aminu HALLIRU
Fassara: ELTAF News TV
08:03:2026