13/06/2026
Kungiyar “Arewa Media Writers” Na Alhini Kan Rasuwar Janar Rabe Abubakar A Hannun Yan Kidnapping, Ta Kuma Yi Allah-Wadai Da Cigaba Da Tabarbarewar Tsaro
…Ƙungiyar ta ce mutuwar babban jami’in soja a hannun ’yan ta’adda babbar alama ce ta yadda matsalar tsaro ke ƙara tsananta, tare da kira ga gwamnati da ta ɗauki matakan gaggawa maimakon mayar da hankali kan abubuwan da ba su da muhimmanci.
Daga Ƙungiyar “Arewa Media Writers”
Ƙungiyar “Arewa Media Writers” ƙarƙashin jagorancin shugaban kungiyar na kasa Comr. Haidar H Hashim Kano, ta bayyana matuƙar alhini da damuwa kan rasuwar Janar Rabe Abubakar, wanda aka ruwaito ya rasa ransa a hannun yan ta’adda bayan gaza kubutar da shi da gwamnati ta yi.
Ƙungiyar ta bayyana cewa wannan mummunan lamari ya sake bayyana irin girman ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta, inda har manyan jami’an tsaro ke rasa rayukansu duk da shekaru 35 da s**a kwashe suna yiwa kasarsu hidima.
A cewar ƙungiyar, hakan ya kamata ya zama abin da gwamnati da al’umma za su fi mayar da hankali a kai fiye da shagaltuwa da batutuwa marasa tasiri ga rayuwar jama’a.
“Arewa Media Writers” ta bayyana cewa ci gaba da irin waɗannan hare-hare na nuna akwai manyan gibi a tsarin tsaro da ke buƙatar a magance su cikin gaggawa.
Ƙungiyar ta yi nuni da cewa idan ba a ɗauki matakan da s**a dace ba, hakan na iya ƙara jefa al’umma cikin fargaba tare da barazana ga zaman lafiya da ci gaban ƙasa.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su sake nazari kan dabarun da ake amfani da su wajen yaƙi da ta’addanci, tare da samar da isassun kayan aiki, bayanan sirri da tallafin da jami’an tsaro ke buƙata domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
A cewar ƙungiyar, kare rayukan ’yan ƙasa da tabbatar da tsaro shi ne muhimmin nauyin da ya rataya a wuyan gwamnati, kuma ya zama wajibi a ɗauki ƙarin matakai masu inganci domin dakile ayyukan masu aikata ta’addanci.
A ƙarshe, ƙungiyar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan marigayin, rundunar tsaro da ɗaukacin ’yan Najeriya, tare da addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, Ya ba iyalansa da ƙasa baki ɗaya ƙarfin jure wannan babban rashi.
Comr. Muhammad Kwairi Waziri
National Editor I Arewa Media Writers